ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 11, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kowa Ya Ci Zomo Ya Ci Gudu: Shekaru 80 Da Nasarar Sinawa A Kan Zalunci Da Danniyar Japanawa

by Sulaiman
10 months ago
Sinawa

Hausawa na cewa, “Mai nema na tare da samu”, a ranar 3 ga watan Satumban 2025, Sinawa yara da manya, samari da ’yan mata ta ko ina sun cika da farin cikin tunawa da wannan rana mai dimbin tarihi a rayuwar Sinawa, ita ce ranar da aka samu nasara a yaki da zalunci da danniya na Japanawa da suka mamaye yankunan Sinawa.

A bana, Sinawa na murnar cika shekaru 80 da samun wannan babbar nasara wacce juriya, jajircewa da hadin kai ya samar da ita bayan kai ruwa rana, wanda hankali ke dimauta da irin yadda aka cimma wannan nasara.

Saboda muhimnancin wannan rana, fiye da shugabannin kasashen waje 20 ne suka halarci bikin a dandalin Tian’anmen a birnin Beijing, wanda ya cika makil da jama’a, ga kuma an masa ado da kambun tarihin shekarar nasara “1945” da “2025”.

ADVERTISEMENT

A wannan rana mai dimbin tarihi, rundunar soji ta jama’ar Sin ta gwangwaje duniya da fareti mai kayatarwa tare da baje kolin makamai masu linzami na zamani, jiragen yaki na sama da na ruwa, da sauran kayayyakin yaki na zamani don tunawa da wannan rana ta ’yan mazan jiya.

Yakin duniya na II shi ne mafi muni a tarihin yakin da dan adam ya taba yi. A duk duniya, mutane miliyan 70 zuwa 85 ne suka rasa rayukansu. An yi asarar kusan dala tiriliyan 4. A kasar Sin, shekaru 14 da aka shafe ana gwabzawa da jama’ar kasar Sin kan adawa da danniyar kasar Japan, ya yi sanadin jikkatawa da mutuwar sojoji da fararen hula fiye da miliyan 35, wannan sama da kashi daya cikin ukun wadanda suka mutu a yakin duniya II ke nan. Lallai sannu Sinawa, wato ko za a kare gaba daya, babu guduwa kuma ba mika wuya. A nan ne bahaushe ke cewa, “kowa ya ci zomo, ya ci gudu”.

LABARAI MASU NASABA

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?

Yakin ya farkar da Sin da duniya baki daya, wanda ya zama tushen kafuwar jamhuriyar jama’ar kasar Sin a shekarar 1949, daga bisani kuma ya dora kasar bisa tafarkin zamani. Ga duniya, mulkin mallaka ya fara wargajewa. Kasashe da dama sannu a hankali suka fahimci cewa, in sun jajirce, za su samu ‘yancin kai.

Tasirin yaki da zalunci da danniya da Jama’ar Sinawa suka yi, ya sa kasar ta kudiri aniyar yaki da zalunci da danniya a duniya ta rungumi manufar tabbatar da zaman lafiya, inda ta nuna wa duniya cewa, lokacin wariya da danniya, tsarin rayuwar dabbobi (na sama ya buge na kasa), ba zai dore ba amma samar da dawwamammen zaman lafiya da tsaro, na sama ya yi wa na kasa adalci, shi ne tsarin da ya dace kowa ya runguma.

Wannan fareti na nunawa duniya cewa, sojojin jama’ar kasar Sin an tanade su ne don tabbatar da zaman lafiya da aminci, inda yake a rubuce jikin alluna da tutoci, “Adalci zai yi nasara,” “samar da zaman lafiya zai yi nasara,” da kuma “mutane za su yi nasara”.

Daga cikin kasashe biyar na dindindin a kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya (MDD), kasar Sin ta ba da gudummawar mafi yawan dakarun kiyaye zaman lafiya a fadin duniya.

A ’yan kwanakin nan, shugaban kasar Sin Xi Jinping a lokacin wani taron tattauna bukatun tsarin shugabancin duniya, ya yi nuni da cewa, kasar Sin za ta yi aiki kafada-da-kafada da kasashen duniya domin samar da “tsarin shugabanci na duniya mai adalci da daidaito”.

Wannan ya tabbatar da cewa, yakin da jama’ar Sinawa suka yi a kan yakin zalunci da danniya daga Japanawa bai tsaya nan kadai ba har ma da neman wa sauran kasashe masu tasowa ’yancin zaman lafiya da ci gaba mai dorewa.

 

 

 

Sinawa
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Annalena Baerbock: Kasar Sin Babbar Mai Goyon Bayan Tsarin Mabambantan Bangarori Ce
  • Sulaiman
    Sin Ta Kalubalanci A Tabbatar Da Tsagaita Bude Wuta A Gabas Ta Tsakiya
  • Sulaiman
    Babban Jami’i: Nazartar Mahangar Xi Jinping Mabudi Ne Na Fahimtar Kasar Sin Ta Zamani
  • Sulaiman
    Xi Da Kim Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Yarjejeniyar Abota, Hadin Gwiwa Da Taimakon Juna Tsakanin Sin Da DPRK

MASU ALAKA

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

July 10, 2026
Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?

July 9, 2026
Mu Leka Yadda Sin Ke Ba Da Misali Ga Duniya Wajen Raya Aikin Noma Da Kauyuka
Ra'ayi Riga

Mu Leka Yadda Sin Ke Ba Da Misali Ga Duniya Wajen Raya Aikin Noma Da Kauyuka

July 7, 2026
Next Post
'Yan Bindiga

Sulhu Da 'Yan Bindiga Ya Fara Haifar Da Da Mai Ido A Katsina

LABARAI MASU NASABA

Annalena Baerbock: Kasar Sin Babbar Mai Goyon Bayan Tsarin Mabambantan Bangarori Ce

Annalena Baerbock: Kasar Sin Babbar Mai Goyon Bayan Tsarin Mabambantan Bangarori Ce

July 11, 2026
Sin Ta Kalubalanci A Tabbatar Da Tsagaita Bude Wuta A Gabas Ta Tsakiya

Sin Ta Kalubalanci A Tabbatar Da Tsagaita Bude Wuta A Gabas Ta Tsakiya

July 11, 2026
Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

July 11, 2026
Babban Jami’i: Nazartar Mahangar Xi Jinping Mabudi Ne Na Fahimtar Kasar Sin Ta Zamani

Babban Jami’i: Nazartar Mahangar Xi Jinping Mabudi Ne Na Fahimtar Kasar Sin Ta Zamani

July 11, 2026
Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 11, 2026
Xi Da Kim Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Yarjejeniyar Abota, Hadin Gwiwa Da Taimakon Juna Tsakanin Sin Da DPRK

Xi Da Kim Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Yarjejeniyar Abota, Hadin Gwiwa Da Taimakon Juna Tsakanin Sin Da DPRK

July 11, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina

July 11, 2026
Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare

Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare

July 11, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa

July 11, 2026
NAF Ta Kai Hare-Haren Sama Kan Maboyar Ƴan Ta’adda A Borno

NAF Ta Kai Hare-Haren Sama Kan Maboyar Ƴan Ta’adda A Borno

July 11, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.