• English
  • Business News
Saturday, September 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ku Riƙa Bincike Kafin Ku Yi Magana, Martanin Gwamnatin Katsina Ga ASUU

by El-Zaharadeen Umar
1 year ago
in Ilimi
0
Ku Riƙa Bincike Kafin Ku Yi Magana, Martanin Gwamnatin Katsina Ga ASUU
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin jihar Katsina ta mayar wa ƙungiyar Malaman jami’a ASUU reshen jami’ar Yar’adua da ke Katsina martani dangane da iƙirarin da ƙungiyar ta yi na cewa jami’ar ta kama hanyar durƙushewa. 

Kwamishinan ma’aikatan ilimi mai zurfi da kula da ƙere-ƙere Ferfasa Abdulhamid Ahmad ya maida martanin ne da cewa ba gwamnatin su ba ce ta rage kuɗaɗen gudanarwar jami’ar ba.

“Wannan gwamnatin ƙarkashin jagorancin Malam Dikko Umar Raɗɗa bata taɓa rage ko Naira ba daga kuɗaɗen gudanarwa da ake ba jami’ar Yar’adua kuma ba a taɓa fashin biyan su ba.”inji shi.

Kwamishinan wanda ya ce shi daya ne daga cikin Malaman jami’ar kafin ya samu muƙami yasan duk abinda ke faruwa yana da masaniyar musamman tafiyar da sha’anin jami’ar

  • ASUU Ta Bada Wa’adin Mako 3 Ga Gwamnatin Tarayya, Ta Yi Barazanar Shiga Sabon Yajin aiki
  • Jami’ar Yar’adua Da Ke Katsina Ta Kama Hanyar Durƙushewa – ASUU

Kazalika ya yi kira ga ƙungiyar ASUU da ta koma jami’ar ta bincika ta gani daga yaushe ne aka rage waɗancan kuɗaɗen da suke magana, ba wai su fito a kafafen yaɗa labarai suna faɗin abinda ba haka yake ba.

Labarai Masu Nasaba

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

NTIC Ta Jinjina Wa Gwamna Buni Kan Taimako A Bangaren Ilimi

Sannan ya ƙara da cewa babu wanda ya taɓa rubutawa gwamnati cewa kuɗaɗen gudanarwa da ake ba jami’ar da sauran manyan makarantu ba sa isar su, babu wanda ya taɓa sanar da gwamnati.

“Kuma ina san jama’a da su gane, ASUU sun ce adadin ɗalibai da tsangaya sun ƙaro, to su bayyanawa duniya adadin kuɗaɗen shiga da suke samu a yanzu kowa ya sani.

A cewar sa, ko Naira ɗaya basa ba gwamnatin jihar Katsina, su ke tara kuɗin su, su ke kashe su, saboda haka ya ce su je su bincika tun shekarar 2015 aka fara zabtare kuɗaɗen gudanarwa na jami’ar da sauran makarantu guda biyar.

Da kwamishinan ya juya game da korafin da ƙungiyar ASUU ta yi na cewa gwamnatin tarayya ta fara aiwatar da shirin ƙarin albashi na kaso 25/35 ya ce yanzu haka maganar tana kan teburin gwamna Dikko Umar Raɗɗa jira ake akwai ya bada umarni.

Ya ƙara da cewa maganar ƙarin albashi da ƙungiyar ƙwadago ya bijiro da shi, ya tsayar da batun, amma tuni an gama wannan maganar, yana mai cewa ya sanar da duk manyan makarantun da suke ƙarƙashin kulawar ma’aikatarsa, inda aka kwana da inda aka tashi akan batun ƙarin albashi, amma ba wai an fasa ba.

Ferfasa Abdulhamid Ahmad ya ce akwai abubuwa da yawa da gwamnatin jihar Katsina ta shirya yi ɓangaren ilimi wanda ya ce wasu ba zai faɗe su ba yanzu, sai nan gaba saboda mahimmancin su ga jihar Katsina.

Ya kuma ƙalubalanci jami’ar Yar’adua wanda ya ce gwamna Malam Dikko Umar Raɗɗa ya yi alkawarin cewa duk dalibin da ya fita da digiri mai daraja ta farko zai ɗauke aiki ba tare da ɓata lokaci ba, amma ya ce kusan wata biyu da yin wannan batu har gobe jami’ar bata rubutu a rubuce ba tana san a aiwatar da wancan alƙawari.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ASUUIlimiKatsinaStrikeUniversityYakin aiki
ShareTweetSendShare
Previous Post

Masana’antar Kera Bayanan Kayayyakin Laturoni Ta Kasar Sin Ta Ba Da Rahoton Bunkasuwa Daga Janairu Zuwa Mayu

Next Post

Yawan Kayayyakin Da Sin Ta Yi Jigila Cikin Sauri A Farkon Watanni 6 Da Suka Gabata Ya Zarce Biliyan 80

Related

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai
Da ɗumi-ɗuminsa

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

1 day ago
Lambar Yabo Ta CON: Buni Ya Zama Zinare Bashi Da Maboya
Ilimi

NTIC Ta Jinjina Wa Gwamna Buni Kan Taimako A Bangaren Ilimi

1 week ago
Hukumar SUBEB Ta Yi Kira Ga Al’umma Da Su Sa ‘Ya’yansu Makaranta
Ilimi

Hukumar SUBEB Ta Yi Kira Ga Al’umma Da Su Sa ‘Ya’yansu Makaranta

1 week ago
Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu
Ilimi

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

2 weeks ago
Kungiyoyi Masu Fada Aji Kan Harkar Ilimi Sun Nemi A Yi Wa Sashen Kwaskwarima
Ilimi

Kungiyoyi Masu Fada Aji Kan Harkar Ilimi Sun Nemi A Yi Wa Sashen Kwaskwarima

3 weeks ago
Gwamnatin Yobe Za Ta Yi Taron Girmama Ɗalibar Turanci Ta Duniya, Nafisa Abdullah
Ilimi

Gwamnatin Yobe Za Ta Yi Taron Girmama Ɗalibar Turanci Ta Duniya, Nafisa Abdullah

1 month ago
Next Post
Yawan Kayayyakin Da Sin Ta Yi Jigila Cikin Sauri A Farkon Watanni 6 Da Suka Gabata Ya Zarce Biliyan 80

Yawan Kayayyakin Da Sin Ta Yi Jigila Cikin Sauri A Farkon Watanni 6 Da Suka Gabata Ya Zarce Biliyan 80

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja

‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja

September 6, 2025
Mutanen Gari Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Wasu A Sakkwato

Mutanen Gari Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Wasu A Sakkwato

September 6, 2025
Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa

September 6, 2025
Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON

Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON

September 6, 2025
Gwamnatin Kogi Ta Jaddada Aniyar Magance Ambaliya Da Zaizayar Ƙasa

Gwamnatin Kogi Ta Jaddada Aniyar Magance Ambaliya Da Zaizayar Ƙasa

September 6, 2025
Zulum Ya Ba Da Tallafin ₦300,000 Ga Iyaye, Da Ciyar Da Ɗalibai 90 Kyauta A Borno

Zulum Ya Ba Da Tallafin ₦300,000 Ga Iyaye, Da Ciyar Da Ɗalibai 90 Kyauta A Borno

September 6, 2025
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho

Kungiyoyi Da Abokan Arziki Na Ci Gaba Da Taya Dantsoho Murna

September 6, 2025
Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

September 6, 2025
Tsohon Mataimakin Gwamnan Gombe Da Wasu jigogin PDP Sun Koma APC

Tsohon Mataimakin Gwamnan Gombe Da Wasu jigogin PDP Sun Koma APC

September 6, 2025

Ilimi Shi Ne Matakin Nasarar Rayuwar Duniya Da Lahira – Yerima Shettima

September 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.