• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kudi Na Zo Nema A Kannywood Ba Suna Ba -Haruna Talle Fata

by Rabilu Sanusi Bena
10 months ago
in Nishadi
0
Kudi Na Zo Nema A Kannywood Ba Suna Ba -Haruna Talle Fata
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jarumi a masana’antar Kannywood Haruna Talle Mai Fata ya yi karin haske a kan dalilin da ya sa ya shigo wannan masana’antar ta Kannywood shekaru fiye da ashirin da suka gabata, Haruna wanda dan uwa ne ga Hamza Talle Mai Fata da kuma Baban Umma wadanda dukansu su na wannan harka ta fim ya ce ba suna ya zo nema a Kannywood ba hasalima yanzu haka idan ya samu wata sana’ar da tafi harkar fim kawo kudi zai canza sana’a.

A hirar da ya yi da Hadiza Gabon a cikin shirinta mai suna ‘Gabon’s Room Talk Show’ Haruna ya ce idan zan fada maki abin da ya kawo ni Kannywood zan ce maki kudi ne domin kuwa yadda iyayena suka rufa mani asiri suka rike mani mutuncina haka nima na ke fatan in kiyaye wa ‘ya’yana mutuncinsu.

  • Jirgin Ruwan Aikin Jiyya Na “Peace Ark” Ya Kammala Aikinsa A Benin
  • Gwamnatin Tarayya Da Google Sun Bullo Da Hanyar Samar Wa Da Matasa 2,500 Aikin Dogaro Da Kai

Babu wata sana’ar da na san zan yi in samu kwabo da ba zan iya yinta ba, don yanzu haka bayan harkar fim ina yin sana’ar ‘recycling’ wato ina sayen tsofaffin robobi in kawo Kano in sayar in samu ‘yan kudadena’’, in ji shi.

Amma fa ba zan taba manta abin alherin da na samu a wannan harka ba domin ta yi mani riga da wando, da kuma sauran abubuwan alherin da na samu ta sanadiyar wannan sana’a, kama daga sanayyar manyan mutane, gida, mota, hajji kai hatta auren da na yi ta sanadiyar wannan sana’a ta fim na yi shi ya kara cewa.

Amma gaskiya neman kudi na zo yi duk da dai na samu daukaka kuma mutane sun sanni da dama,amma idan yanzu zan samu wata sana’ar da zan samu fiye da abinda nake samu a fim kwata kwata zan bar fim in koma waccan sana’ar domin duk abin da zan yi saboda iyalina su samu abin da za su ci a kuma rufawa kai asiri nake yi, inji Haruna.

Labarai Masu Nasaba

Na Hadu Da Azzalumai Da Mayaudara Farkon Shigata Kannywood – Dan’duniya

Ko Maƙiyina Ba Na Yi Masa Fatan Tsintar Kansa A Halin Da Na Samu Kaina – Ummi Nuhu

Da ya ke amsa tambaya dangane da mutanen da ke daukar masu wannan harka ta fim a matsayin yan iska ko wasu mutanen banza Haruna ya ce,ni a kashin kaina duk wani wanda ya ke fadin irin wannan magana walau malami ko almajiri mai kudi ko talaka da duk wani wanda ya ke da irin wannan tunani na cewa yan fim ya iska ne to babu abinda zan ce masu illa su sani akwai ranar da Allah zai taramu ga bakidaya ya yi mana hisabi.

Haruna ya cigaba da cewa babu inda babu dan iska a Duniya kuma babu inda babu mutanen kwarai,kuma kwata kwata babu adalci ka yi wa mutane jam’u yayin da zaka fadi wani abu dangane dasu, ba dukkan malamai ne na kwarai ba hakazalika ba dukkan yan fim ne na banza ba.

Don haka duk wanda ya kiramu da wannan suna na yan iska ko mutanen banza na barshi da mahalicci wanda ya ke da ‘record’ na duk abinda mutum ya yi kuma shi ne yake da ranar sakamako, ranar da babu wani mai dabara ko wayau shi ne zai yi mana hisabi da mu da wadanda ke kiranmu mutanen banza.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: HarunaJarumiKannywoodKudi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ban Hadu Da Wani Kalubale A Lokacin Shiga Masana’antar Kannywood Ba -Fiddausi Yahaya

Next Post

NNPP Ta Lashe Kujerun Shugabannin Kananan Hukumomi 44 Da Kansiloli 484 Na Jihar Kano

Related

Na Hadu Da Azzalumai Da Mayaudara Farkon Shigata Kannywood – Dan’duniya
Nishadi

Na Hadu Da Azzalumai Da Mayaudara Farkon Shigata Kannywood – Dan’duniya

6 days ago
Ko Maƙiyina Ba Na Yi Masa Fatan Tsintar Kansa A Halin Da Na Samu Kaina – Ummi Nuhu
Nishadi

Ko Maƙiyina Ba Na Yi Masa Fatan Tsintar Kansa A Halin Da Na Samu Kaina – Ummi Nuhu

2 weeks ago
Na Yi Lokacin Da Idan Aka Gan Ni Ake Gudu A Masana’antar Kannywood – Mai Dawayya
Nishadi

Na Yi Lokacin Da Idan Aka Gan Ni Ake Gudu A Masana’antar Kannywood – Mai Dawayya

2 weeks ago
An Ɗaura Auren Rahma Sadau A Kaduna
Nishadi

An Ɗaura Auren Rahma Sadau A Kaduna

2 weeks ago
Samun Kuɗi Ya Fi Samun Ɗaukaka Wahala A Kannywood -Baba Sadiƙ
Nishadi

Samun Kuɗi Ya Fi Samun Ɗaukaka Wahala A Kannywood -Baba Sadiƙ

3 weeks ago
Ban Yi Danasanin Shiga Harkar Fim Ba – Baba Ƙarami
Nishadi

Ban Yi Danasanin Shiga Harkar Fim Ba – Baba Ƙarami

3 weeks ago
Next Post
NNPP Ta Lashe Kujerun Shugabannin Kananan Hukumomi 44 Da Kansiloli 484 Na Jihar Kano

NNPP Ta Lashe Kujerun Shugabannin Kananan Hukumomi 44 Da Kansiloli 484 Na Jihar Kano

LABARAI MASU NASABA

Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

August 23, 2025
Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana

Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana

August 23, 2025
Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

August 23, 2025
Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

August 23, 2025
Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

August 23, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

August 23, 2025
NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

August 23, 2025
Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

August 23, 2025
Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara

Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara

August 23, 2025
Hotuna: Shettima Ya Wakilci Shugaba Tinubu Wajen Jana’izar Sarkin Zuru

Hotuna: Shettima Ya Wakilci Shugaba Tinubu Wajen Jana’izar Sarkin Zuru

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.