• English
  • Business News
Thursday, July 31, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kudi Na Zo Nema A Kannywood Ba Suna Ba -Haruna Talle Fata

by Rabilu Sanusi Bena
9 months ago
in Nishadi
0
Kudi Na Zo Nema A Kannywood Ba Suna Ba -Haruna Talle Fata
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jarumi a masana’antar Kannywood Haruna Talle Mai Fata ya yi karin haske a kan dalilin da ya sa ya shigo wannan masana’antar ta Kannywood shekaru fiye da ashirin da suka gabata, Haruna wanda dan uwa ne ga Hamza Talle Mai Fata da kuma Baban Umma wadanda dukansu su na wannan harka ta fim ya ce ba suna ya zo nema a Kannywood ba hasalima yanzu haka idan ya samu wata sana’ar da tafi harkar fim kawo kudi zai canza sana’a.

A hirar da ya yi da Hadiza Gabon a cikin shirinta mai suna ‘Gabon’s Room Talk Show’ Haruna ya ce idan zan fada maki abin da ya kawo ni Kannywood zan ce maki kudi ne domin kuwa yadda iyayena suka rufa mani asiri suka rike mani mutuncina haka nima na ke fatan in kiyaye wa ‘ya’yana mutuncinsu.

  • Jirgin Ruwan Aikin Jiyya Na “Peace Ark” Ya Kammala Aikinsa A Benin
  • Gwamnatin Tarayya Da Google Sun Bullo Da Hanyar Samar Wa Da Matasa 2,500 Aikin Dogaro Da Kai

Babu wata sana’ar da na san zan yi in samu kwabo da ba zan iya yinta ba, don yanzu haka bayan harkar fim ina yin sana’ar ‘recycling’ wato ina sayen tsofaffin robobi in kawo Kano in sayar in samu ‘yan kudadena’’, in ji shi.

Amma fa ba zan taba manta abin alherin da na samu a wannan harka ba domin ta yi mani riga da wando, da kuma sauran abubuwan alherin da na samu ta sanadiyar wannan sana’a, kama daga sanayyar manyan mutane, gida, mota, hajji kai hatta auren da na yi ta sanadiyar wannan sana’a ta fim na yi shi ya kara cewa.

Amma gaskiya neman kudi na zo yi duk da dai na samu daukaka kuma mutane sun sanni da dama,amma idan yanzu zan samu wata sana’ar da zan samu fiye da abinda nake samu a fim kwata kwata zan bar fim in koma waccan sana’ar domin duk abin da zan yi saboda iyalina su samu abin da za su ci a kuma rufawa kai asiri nake yi, inji Haruna.

Labarai Masu Nasaba

Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

Akwai Bukatar Manyan Jaruman Da Suka Yi Kudi Su Taimaki Na Baya -Barau Dadin Kowa

Da ya ke amsa tambaya dangane da mutanen da ke daukar masu wannan harka ta fim a matsayin yan iska ko wasu mutanen banza Haruna ya ce,ni a kashin kaina duk wani wanda ya ke fadin irin wannan magana walau malami ko almajiri mai kudi ko talaka da duk wani wanda ya ke da irin wannan tunani na cewa yan fim ya iska ne to babu abinda zan ce masu illa su sani akwai ranar da Allah zai taramu ga bakidaya ya yi mana hisabi.

Haruna ya cigaba da cewa babu inda babu dan iska a Duniya kuma babu inda babu mutanen kwarai,kuma kwata kwata babu adalci ka yi wa mutane jam’u yayin da zaka fadi wani abu dangane dasu, ba dukkan malamai ne na kwarai ba hakazalika ba dukkan yan fim ne na banza ba.

Don haka duk wanda ya kiramu da wannan suna na yan iska ko mutanen banza na barshi da mahalicci wanda ya ke da ‘record’ na duk abinda mutum ya yi kuma shi ne yake da ranar sakamako, ranar da babu wani mai dabara ko wayau shi ne zai yi mana hisabi da mu da wadanda ke kiranmu mutanen banza.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: HarunaJarumiKannywoodKudi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ban Hadu Da Wani Kalubale A Lokacin Shiga Masana’antar Kannywood Ba -Fiddausi Yahaya

Next Post

NNPP Ta Lashe Kujerun Shugabannin Kananan Hukumomi 44 Da Kansiloli 484 Na Jihar Kano

Related

Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa
Nishadi

Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

5 days ago
Akwai Bukatar Manyan Jaruman Da Suka Yi Kudi Su Taimaki Na Baya -Barau Dadin Kowa
Nishadi

Akwai Bukatar Manyan Jaruman Da Suka Yi Kudi Su Taimaki Na Baya -Barau Dadin Kowa

3 weeks ago
Zan Dade Ban Manta Da Mahaifinmu Ba -Abba Sadau
Nishadi

Zan Dade Ban Manta Da Mahaifinmu Ba -Abba Sadau

4 weeks ago
Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi
Nishadi

Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

4 weeks ago
Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda
Nishadi

Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

1 month ago
Fim Babbar Hanya Ce Ta Nishaɗantar Da Al’umma -D Malam Dan Bola (2)
Nishadi

Fim Babbar Hanya Ce Ta Nishaɗantar Da Al’umma -D Malam Dan Bola (2)

1 month ago
Next Post
NNPP Ta Lashe Kujerun Shugabannin Kananan Hukumomi 44 Da Kansiloli 484 Na Jihar Kano

NNPP Ta Lashe Kujerun Shugabannin Kananan Hukumomi 44 Da Kansiloli 484 Na Jihar Kano

LABARAI MASU NASABA

Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Ziyarci Jama’a, Ya Daina Sauraron Gwamnoni — ADC

Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Ziyarci Jama’a, Ya Daina Sauraron Gwamnoni — ADC

July 31, 2025
Faransa Za Ta Fara Jefa Kayan Agaji Ta Sama A Gaza

Faransa Za Ta Fara Jefa Kayan Agaji Ta Sama A Gaza

July 31, 2025
Za A Kammala Aikin Titin Jirgin Ƙasan Kaduna-Kano A 2026 – Gwamnatin Tarayya

Za A Kammala Aikin Titin Jirgin Ƙasan Kaduna-Kano A 2026 – Gwamnatin Tarayya

July 31, 2025
Sin Ta Dade Tana Aiki Tukuru Kan Kiyaye Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali Na Yanki

Sin Ta Dade Tana Aiki Tukuru Kan Kiyaye Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali Na Yanki

July 30, 2025
Ma’aikatar Bunƙasa Harkar Kiwo Za Ta Taimaka Wajen Magance Rikicin Manoma Da Makiyaya — Jega

Ma’aikatar Bunƙasa Harkar Kiwo Za Ta Taimaka Wajen Magance Rikicin Manoma Da Makiyaya — Jega

July 30, 2025
Salisu Yusuf Ya Ajiye Aikinsa Na Kocin Nasarawa United

Salisu Yusuf Ya Ajiye Aikinsa Na Kocin Nasarawa United

July 30, 2025
Rikicin Makiyaya Da Manoma: An Kashe Mutum Daya, Gidaje 31 Sun Kone A Abuja

Rikicin Makiyaya Da Manoma: An Kashe Mutum Daya, Gidaje 31 Sun Kone A Abuja

July 30, 2025
Binciken CGTN: Za A Ci Gaba Da Nuna Kyakkyawan Fata Ga Bunkasar Sin Nan Da Shekaru 5

Binciken CGTN: Za A Ci Gaba Da Nuna Kyakkyawan Fata Ga Bunkasar Sin Nan Da Shekaru 5

July 30, 2025
Wasan Kwallon Mutum-Mutumi Ya Nuna Yadda Sin Ta Shirya Wa Karbar Bakuncin Wasanninsu Na Duniya

Wasan Kwallon Mutum-Mutumi Ya Nuna Yadda Sin Ta Shirya Wa Karbar Bakuncin Wasanninsu Na Duniya

July 30, 2025
Gwamnati Za Ta Kafa Cibiyoyin Kiwo a Yankuna Shida — Ƙaramin Ministan Noma

Gwamnati Za Ta Kafa Cibiyoyin Kiwo a Yankuna Shida — Ƙaramin Ministan Noma

July 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.