• English
  • Business News
Thursday, June 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kudi Na Zo Nema A Kannywood Ba Suna Ba -Haruna Talle Fata

by Rabilu Sanusi Bena
8 months ago
in Nishadi
0
Kudi Na Zo Nema A Kannywood Ba Suna Ba -Haruna Talle Fata
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jarumi a masana’antar Kannywood Haruna Talle Mai Fata ya yi karin haske a kan dalilin da ya sa ya shigo wannan masana’antar ta Kannywood shekaru fiye da ashirin da suka gabata, Haruna wanda dan uwa ne ga Hamza Talle Mai Fata da kuma Baban Umma wadanda dukansu su na wannan harka ta fim ya ce ba suna ya zo nema a Kannywood ba hasalima yanzu haka idan ya samu wata sana’ar da tafi harkar fim kawo kudi zai canza sana’a.

A hirar da ya yi da Hadiza Gabon a cikin shirinta mai suna ‘Gabon’s Room Talk Show’ Haruna ya ce idan zan fada maki abin da ya kawo ni Kannywood zan ce maki kudi ne domin kuwa yadda iyayena suka rufa mani asiri suka rike mani mutuncina haka nima na ke fatan in kiyaye wa ‘ya’yana mutuncinsu.

  • Jirgin Ruwan Aikin Jiyya Na “Peace Ark” Ya Kammala Aikinsa A Benin
  • Gwamnatin Tarayya Da Google Sun Bullo Da Hanyar Samar Wa Da Matasa 2,500 Aikin Dogaro Da Kai

Babu wata sana’ar da na san zan yi in samu kwabo da ba zan iya yinta ba, don yanzu haka bayan harkar fim ina yin sana’ar ‘recycling’ wato ina sayen tsofaffin robobi in kawo Kano in sayar in samu ‘yan kudadena’’, in ji shi.

Amma fa ba zan taba manta abin alherin da na samu a wannan harka ba domin ta yi mani riga da wando, da kuma sauran abubuwan alherin da na samu ta sanadiyar wannan sana’a, kama daga sanayyar manyan mutane, gida, mota, hajji kai hatta auren da na yi ta sanadiyar wannan sana’a ta fim na yi shi ya kara cewa.

Amma gaskiya neman kudi na zo yi duk da dai na samu daukaka kuma mutane sun sanni da dama,amma idan yanzu zan samu wata sana’ar da zan samu fiye da abinda nake samu a fim kwata kwata zan bar fim in koma waccan sana’ar domin duk abin da zan yi saboda iyalina su samu abin da za su ci a kuma rufawa kai asiri nake yi, inji Haruna.

Labarai Masu Nasaba

Fim Babbar Hanya Ce Ta Nishaɗantar Da Al’umma -D Malam Dan Bola (2)

Rashin Abinci Na A Waka Ya Sa Na Daina Yi -T Y Shaba

Da ya ke amsa tambaya dangane da mutanen da ke daukar masu wannan harka ta fim a matsayin yan iska ko wasu mutanen banza Haruna ya ce,ni a kashin kaina duk wani wanda ya ke fadin irin wannan magana walau malami ko almajiri mai kudi ko talaka da duk wani wanda ya ke da irin wannan tunani na cewa yan fim ya iska ne to babu abinda zan ce masu illa su sani akwai ranar da Allah zai taramu ga bakidaya ya yi mana hisabi.

Haruna ya cigaba da cewa babu inda babu dan iska a Duniya kuma babu inda babu mutanen kwarai,kuma kwata kwata babu adalci ka yi wa mutane jam’u yayin da zaka fadi wani abu dangane dasu, ba dukkan malamai ne na kwarai ba hakazalika ba dukkan yan fim ne na banza ba.

Don haka duk wanda ya kiramu da wannan suna na yan iska ko mutanen banza na barshi da mahalicci wanda ya ke da ‘record’ na duk abinda mutum ya yi kuma shi ne yake da ranar sakamako, ranar da babu wani mai dabara ko wayau shi ne zai yi mana hisabi da mu da wadanda ke kiranmu mutanen banza.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: HarunaJarumiKannywoodKudi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ban Hadu Da Wani Kalubale A Lokacin Shiga Masana’antar Kannywood Ba -Fiddausi Yahaya

Next Post

NNPP Ta Lashe Kujerun Shugabannin Kananan Hukumomi 44 Da Kansiloli 484 Na Jihar Kano

Related

Fim Babbar Hanya Ce Ta Nishaɗantar Da Al’umma -D Malam Dan Bola (2)
Nishadi

Fim Babbar Hanya Ce Ta Nishaɗantar Da Al’umma -D Malam Dan Bola (2)

3 days ago
Rashin Abinci Na A Waka Ya Sa Na Daina Yi -T Y Shaba
Nishadi

Rashin Abinci Na A Waka Ya Sa Na Daina Yi -T Y Shaba

2 weeks ago
Yadda Jarumai A Masana’antar Kannywood Ke Auren Junansu
Nishadi

Yadda Jarumai A Masana’antar Kannywood Ke Auren Junansu

4 weeks ago
Ban Dauki Harkar Fim Da Wasa Ba -Hauwa Ayawa 
Nishadi

Ban Dauki Harkar Fim Da Wasa Ba -Hauwa Ayawa 

1 month ago
Hukuma Ta Dakatar Da Haska Fina-Finai 22 Har Sai Baba Tagani
Nishadi

Hukuma Ta Dakatar Da Haska Fina-Finai 22 Har Sai Baba Tagani

1 month ago
Ban Ɗauki Harkar Fim Da Wasa Ba – Hauwa Ayawa
Nishadi

Ban Ɗauki Harkar Fim Da Wasa Ba – Hauwa Ayawa

1 month ago
Next Post
NNPP Ta Lashe Kujerun Shugabannin Kananan Hukumomi 44 Da Kansiloli 484 Na Jihar Kano

NNPP Ta Lashe Kujerun Shugabannin Kananan Hukumomi 44 Da Kansiloli 484 Na Jihar Kano

LABARAI MASU NASABA

Cristiano Ronaldo Na Shirin Tsawaita Kwantiraginsa A Kungiyar Al-Nassr

Cristiano Ronaldo Na Shirin Tsawaita Kwantiraginsa A Kungiyar Al-Nassr

June 25, 2025
Ni Ne Na Kai Kaina ga Hukumar EFCC, In Ji Tsohon Jami’in NNPC

Ni Ne Na Kai Kaina ga Hukumar EFCC, In Ji Tsohon Jami’in NNPC

June 25, 2025
Shugabannin Sin Da Mozamqiue Sun Mikawa Juna Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafuwar Huldar Diflomasiyya

Shugabannin Sin Da Mozamqiue Sun Mikawa Juna Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafuwar Huldar Diflomasiyya

June 25, 2025
MSS: Neman Sinawa ‘Yan Leken Asiri Da CIA Ta Yi Tamkar Wasan Ban Dariya Ne

MSS: Neman Sinawa ‘Yan Leken Asiri Da CIA Ta Yi Tamkar Wasan Ban Dariya Ne

June 25, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Kano Ta Ayyana Ranar Alhamis Hutu Domin Murnar Sabuwar Shekarar Musulunci

June 25, 2025
Gwamnan Jigawa Ya Kaddamar Da Rumbun Sauki Don Sayar Wa Ma’aikata Kayayyakin Abinci A Farashi Mai Rahusa A Sakkwato

Gwamnan Jigawa Ya Kaddamar Da Rumbun Sauki Don Sayar Wa Ma’aikata Kayayyakin Abinci A Farashi Mai Rahusa A Sakkwato

June 25, 2025
Sin Ta Sha Alwashin Rarraba Fasahohinta Na Ainihi Da Dabarunta Na Kirkire-Kirkire Tare Da Sauran Sassan Kasa Da Kasa

Sin Ta Sha Alwashin Rarraba Fasahohinta Na Ainihi Da Dabarunta Na Kirkire-Kirkire Tare Da Sauran Sassan Kasa Da Kasa

June 25, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Katse Hanyar Maiduguri Zuwa Damboa

Mutane 4 Sun Mutu, 10 Sun Jikkata Yayin Da Wata Mota Ta Taka Bam A Borno

June 25, 2025
Shawarar Gudanar Da Harkokin AI Na Duniya Na Jagorantar Ci Gaban Wayewar Kan Dan Adam Ta Hanyar Amfani Da Fasahar Zamani

Shawarar Gudanar Da Harkokin AI Na Duniya Na Jagorantar Ci Gaban Wayewar Kan Dan Adam Ta Hanyar Amfani Da Fasahar Zamani

June 25, 2025
Sojoji

DHQ Za Ta Tura Dakaru Na Musamman 800 Yankunan Da Ke Fama Da Rashin Tsaro – CDS

June 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.