• English
  • Business News
Tuesday, July 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kudi Na Zo Nema A Kannywood Ba Suna Ba -Haruna Talle Fata

by Rabilu Sanusi Bena
8 months ago
in Nishadi
0
Kudi Na Zo Nema A Kannywood Ba Suna Ba -Haruna Talle Fata
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jarumi a masana’antar Kannywood Haruna Talle Mai Fata ya yi karin haske a kan dalilin da ya sa ya shigo wannan masana’antar ta Kannywood shekaru fiye da ashirin da suka gabata, Haruna wanda dan uwa ne ga Hamza Talle Mai Fata da kuma Baban Umma wadanda dukansu su na wannan harka ta fim ya ce ba suna ya zo nema a Kannywood ba hasalima yanzu haka idan ya samu wata sana’ar da tafi harkar fim kawo kudi zai canza sana’a.

A hirar da ya yi da Hadiza Gabon a cikin shirinta mai suna ‘Gabon’s Room Talk Show’ Haruna ya ce idan zan fada maki abin da ya kawo ni Kannywood zan ce maki kudi ne domin kuwa yadda iyayena suka rufa mani asiri suka rike mani mutuncina haka nima na ke fatan in kiyaye wa ‘ya’yana mutuncinsu.

  • Jirgin Ruwan Aikin Jiyya Na “Peace Ark” Ya Kammala Aikinsa A Benin
  • Gwamnatin Tarayya Da Google Sun Bullo Da Hanyar Samar Wa Da Matasa 2,500 Aikin Dogaro Da Kai

Babu wata sana’ar da na san zan yi in samu kwabo da ba zan iya yinta ba, don yanzu haka bayan harkar fim ina yin sana’ar ‘recycling’ wato ina sayen tsofaffin robobi in kawo Kano in sayar in samu ‘yan kudadena’’, in ji shi.

Amma fa ba zan taba manta abin alherin da na samu a wannan harka ba domin ta yi mani riga da wando, da kuma sauran abubuwan alherin da na samu ta sanadiyar wannan sana’a, kama daga sanayyar manyan mutane, gida, mota, hajji kai hatta auren da na yi ta sanadiyar wannan sana’a ta fim na yi shi ya kara cewa.

Amma gaskiya neman kudi na zo yi duk da dai na samu daukaka kuma mutane sun sanni da dama,amma idan yanzu zan samu wata sana’ar da zan samu fiye da abinda nake samu a fim kwata kwata zan bar fim in koma waccan sana’ar domin duk abin da zan yi saboda iyalina su samu abin da za su ci a kuma rufawa kai asiri nake yi, inji Haruna.

Labarai Masu Nasaba

Zan Dade Ban Manta Da Mahaifinmu Ba -Abba Sadau

Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

Da ya ke amsa tambaya dangane da mutanen da ke daukar masu wannan harka ta fim a matsayin yan iska ko wasu mutanen banza Haruna ya ce,ni a kashin kaina duk wani wanda ya ke fadin irin wannan magana walau malami ko almajiri mai kudi ko talaka da duk wani wanda ya ke da irin wannan tunani na cewa yan fim ya iska ne to babu abinda zan ce masu illa su sani akwai ranar da Allah zai taramu ga bakidaya ya yi mana hisabi.

Haruna ya cigaba da cewa babu inda babu dan iska a Duniya kuma babu inda babu mutanen kwarai,kuma kwata kwata babu adalci ka yi wa mutane jam’u yayin da zaka fadi wani abu dangane dasu, ba dukkan malamai ne na kwarai ba hakazalika ba dukkan yan fim ne na banza ba.

Don haka duk wanda ya kiramu da wannan suna na yan iska ko mutanen banza na barshi da mahalicci wanda ya ke da ‘record’ na duk abinda mutum ya yi kuma shi ne yake da ranar sakamako, ranar da babu wani mai dabara ko wayau shi ne zai yi mana hisabi da mu da wadanda ke kiranmu mutanen banza.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: HarunaJarumiKannywoodKudi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ban Hadu Da Wani Kalubale A Lokacin Shiga Masana’antar Kannywood Ba -Fiddausi Yahaya

Next Post

NNPP Ta Lashe Kujerun Shugabannin Kananan Hukumomi 44 Da Kansiloli 484 Na Jihar Kano

Related

Zan Dade Ban Manta Da Mahaifinmu Ba -Abba Sadau
Nishadi

Zan Dade Ban Manta Da Mahaifinmu Ba -Abba Sadau

2 days ago
Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi
Nishadi

Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

3 days ago
Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda
Nishadi

Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

1 week ago
Fim Babbar Hanya Ce Ta Nishaɗantar Da Al’umma -D Malam Dan Bola (2)
Nishadi

Fim Babbar Hanya Ce Ta Nishaɗantar Da Al’umma -D Malam Dan Bola (2)

2 weeks ago
Rashin Abinci Na A Waka Ya Sa Na Daina Yi -T Y Shaba
Nishadi

Rashin Abinci Na A Waka Ya Sa Na Daina Yi -T Y Shaba

4 weeks ago
Yadda Jarumai A Masana’antar Kannywood Ke Auren Junansu
Nishadi

Yadda Jarumai A Masana’antar Kannywood Ke Auren Junansu

1 month ago
Next Post
NNPP Ta Lashe Kujerun Shugabannin Kananan Hukumomi 44 Da Kansiloli 484 Na Jihar Kano

NNPP Ta Lashe Kujerun Shugabannin Kananan Hukumomi 44 Da Kansiloli 484 Na Jihar Kano

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

ADC: Tinubu Na Yunƙurin Raba Kawunan Masu Haɗaka Kafin Zaɓen 2027

July 8, 2025
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa

Nijeriya Ba Ta Da Sha’awar Yin Gwajin Makamin Nukiliya — Shettima

July 8, 2025
Da Ɗumi-Ɗumi: Osimhen Ya Amince Da Komawa Galatasaray Na Dindindin

Da Ɗumi-Ɗumi: Osimhen Ya Amince Da Komawa Galatasaray Na Dindindin

July 7, 2025
Sin Za Ta Ci Gaba Da Karfafa Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Kan Tinkarar Sauyin Yanayi

Sin Za Ta Ci Gaba Da Karfafa Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Kan Tinkarar Sauyin Yanayi

July 7, 2025
Ƙungiyar Al’ummar Igbo Ta Ohanaeze Ndigbo Ta Ce Tinubu Ya Fi Ƙarfin ‘Yan Jam’iyyar Haɗaka Ta ADC

Ƙungiyar Al’ummar Igbo Ta Ohanaeze Ndigbo Ta Ce Tinubu Ya Fi Ƙarfin ‘Yan Jam’iyyar Haɗaka Ta ADC

July 7, 2025
Sin Za Ta Gina Wuraren Cajin Ababen Hawa Masu Ingantaccen Lantarki

Sin Za Ta Gina Wuraren Cajin Ababen Hawa Masu Ingantaccen Lantarki

July 7, 2025
NiMet Ta Yi Hasashen Cikin Watan Yulin 2025 Za A Tabka Ambaliyar Ruwan Sama A Jihohin Nijeriya 19

NiMet Ta Yi Hasashen Cikin Watan Yulin 2025 Za A Tabka Ambaliyar Ruwan Sama A Jihohin Nijeriya 19

July 7, 2025
Sin Ta Kafa Kungiyar Masana Masu Binciken Sararin Samaniya Mai Zurfi Ta Farko

Sin Ta Kafa Kungiyar Masana Masu Binciken Sararin Samaniya Mai Zurfi Ta Farko

July 7, 2025
Xi Ya Ajiye Furanni Ga Wadanda Suka Mutu Yayin Yakin Bijirewa Harin Japan

Xi Ya Ajiye Furanni Ga Wadanda Suka Mutu Yayin Yakin Bijirewa Harin Japan

July 7, 2025
Asibiti Mai Zaman Kansa A Kano Zai Fara Aikin Manyan Tiyatu Tare Da Rage Kuɗi Kaso 50%

Asibiti Mai Zaman Kansa A Kano Zai Fara Aikin Manyan Tiyatu Tare Da Rage Kuɗi Kaso 50%

July 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.