• English
  • Business News
Tuesday, July 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kungiyar Lauyoyi Ta Tabbatar Da Fara Gurfanar Da Masu Laifukan Zaben 2023

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Kungiyar Lauyoyi Ta Tabbatar Da Fara Gurfanar Da Masu Laifukan Zaben 2023
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin tarayya karkashin kungiyar lauyoyi ta Nijeriya (NBA) ta fara gurfanar da wasu jami’an hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) da mambobin jam’iyyar siyasa bisa samun su da laifuka daban-daban a lokacin gudanar da zaben 2023.   

Laifukan zabe sun kasance babban barazana ga gudanar da sahihin zabe a Nijeriya, domin sukan janyo tsananin gabar siyasa da kuma haddasa rikice-rikice.

  • Rikita-rikitar Sauka Da Komawar Sheikh Daurawa Shugabancin Hisbar Jihar Kano
  • Firaministan Kasar Malaysia Ya Ce Bai Kamata Ba A Yi Tsoron Bunkasuwar Kasar Sin

Bayan zaben shugaban kasa da na ‘yan majalisu da ya gudana a ranar 25 ga Fabrairun 2023, rundunar ‘yansandar Nijeriya ta ce ta samu nasarar damke mutane sama da 700, bisa karya dokokin zabe.

A ranar 2 ga Mayun 2023, INEC ta ce ta gurfanar da mutum 215 cikin mutum 774 da ‘yansanda suka kama bisa aikata laifuka daban-daban da suka shafi zabe.

Hukumar INEC ta ce ta hada kai da kungiyar lauyoyin Nijeriya domin gurfanar da wadanda aka kama bisa karya dokokin zabe a gaban kuliya.

Labarai Masu Nasaba

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

Daga cikin shari’o’i 215 da hukumar INEC ta samu, shari’o’i’ 196 sun kasance laifuka ne na karya dokokin zabe, wanda kuma INEC da lauyoyi suke kulawa da su.

Sakataren yada labarai na NBA, Habeeb Lawal, an gurfanar da wadanda ake zargi mutum 196 ciki har da jami’an INEC da mambobin jam’iyyun siyasa, bisa karya dokokin zabe da suka hada da sayan kuri’u, mallakar makamai da sauran laifuka da suka aikata lokacin zaben 2023.

Lawal ya kara da cewa an gurfanar da wadanda ake zargin ne a kotunan majestiri da sauran manyan kotuna da ke jihohi da kuma Abuja.

Ya ce, “An gurfanar da mutum 196 da ake zargi da karya dokokin zabe, kuma mambobin kungiyar lauyoyi ne ke kula da lamarin.

“Laifukan sun hada da sakaci wurin gudanar da aiki, kada kai wajen aikata ta’addanci, kawo hagitsi a wurin zabe, fito da makami lokacin zabe, satar akwatin zabe, lalata kayayyakin zabe, yin magudin zabe, mallakar kayayyakin zabe ba bisa ka’ida ba, rashin mayar da hankali lokacin zabe, sayar kuri’a da kuma kawo rikice-rikice a lokacin zabe.

“Wasu daga cikin wadanda ake zargin jami’an INEC ne, yayin da wasu mambobin jam’iyyun siyasa ne, sannan kuma wasu kuma ba su da alaka da harkokin siyasa.

“Kotunan majestiri da ke jihohi da Abuja suke kulawa da shari’o’in da suka danganci laifukan zabe kamar yadda dokar zabe ta tanada.

“Domin haka, mambobin kungiyarmu suna kulawa da wadannan shari’o’i a dukkan fadin kasar nan,” in ji shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnan Zamfara Ya Kai Ziyarar Ta’aziyya Garin Mada

Next Post

Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Da Su Tallafawa Matakan Siyasa A Sudan

Related

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

4 days ago
Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 
Tambarin Dimokuradiyya

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

4 days ago
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Masu Neman Takarar Shugaban Kasa A PDP Sun Kara Matsa Kaimi Bayan Ficewar Atiku

4 days ago
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

2 weeks ago
majalisar kasa
Tambarin Dimokuradiyya

Kirkirar Sabbin Jihohi Da Kananan Hukumomi Sun Dabaibaye Sauraron Jin Ra’ayoyin Gyaran Tsarin Mulki

2 weeks ago
Ko Yanzu Tinubu Ya Yi Rawar Gani, Kuma Yana Ƙoƙari Sosai – Buhari
Rahotonni

Muhimman Abubuwa 10 Da Kowa Zai So Ya Sani Game Da Marigayi Shugaban Ƙasa Buhari

2 weeks ago
Next Post
Sudan

Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Da Su Tallafawa Matakan Siyasa A Sudan

LABARAI MASU NASABA

Babu Wata Karamar Hukumar Dake Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang

Babu Wata Karamar Hukumar Dake Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang

July 29, 2025
Shugaba Xi Ya Aike Da Sako Ga Taron Wanzar Da Zaman Lafiya Na Matasan Kasa Da Kasa

Shugaba Xi Ya Aike Da Sako Ga Taron Wanzar Da Zaman Lafiya Na Matasan Kasa Da Kasa

July 29, 2025
Morocco Ta Shigar Da Ƙara Kan Nasarar Super Falcons A Gasar WAFCON

Morocco Ta Shigar Da Ƙara Kan Nasarar Super Falcons A Gasar WAFCON

July 29, 2025
An Fitar Da Kudaden Farfado Da Sassan Birnin Beijing Da Bala’in Ambaliyar Ruwa Ya Shafa

An Fitar Da Kudaden Farfado Da Sassan Birnin Beijing Da Bala’in Ambaliyar Ruwa Ya Shafa

July 29, 2025
Matashi Ya Kashe Surukarsa Saboda Shigarta Cikin Sha’anin Aurensu

Matashi Ya Kashe Surukarsa Saboda Shigarta Cikin Sha’anin Aurensu

July 29, 2025
Xi Ya Yi Kira Da A Yi Azamar Kare Rayukan Al’umma Yayin Da Ake Fuskantar Ibtila’in Ambaliya A Wasu Sassan Kasar Sin

Xi Ya Yi Kira Da A Yi Azamar Kare Rayukan Al’umma Yayin Da Ake Fuskantar Ibtila’in Ambaliya A Wasu Sassan Kasar Sin

July 29, 2025
Birtaniya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Mutane 33 A Zamfara

Birtaniya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Mutane 33 A Zamfara

July 29, 2025
Mai Cin Moriyar Kai Da Mai Cin Moriyar Juna

Mai Cin Moriyar Kai Da Mai Cin Moriyar Juna

July 29, 2025
Kar Ka Zuga Ƴan Arewa Kan Tinubu — Nabena Ya Gargaɗi Kwankwaso

Kar Ka Zuga Ƴan Arewa Kan Tinubu — Nabena Ya Gargaɗi Kwankwaso

July 29, 2025
Gwamnatin Katsina Ta Fara Bayar Da Maganin Zazzabi Kyauta A Asibitoci

Gwamnatin Katsina Ta Fara Bayar Da Maganin Zazzabi Kyauta A Asibitoci

July 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.