Ibrahim Muhammad">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home RAHOTANNI

Kungiyar ’Yan Tifa A Kano Ta Yi Wa Unguwar Rimi Gyaran Hanya

by Ibrahim Muhammad
December 22, 2020
in RAHOTANNI
2 min read
Kungiyar ’Yan Tifa
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Al’ummar yankin unguwar Rimi da ke yankin karamar hukumar Kumbotso sun bayyana mutukar jin dadinsu bisa dauki da hadaddiyar kungiyar ’Yan tifa na Jihar Kano su na kawo mu su na samar da kasa, domin cike hanyar dan saukaka mu su wahalar rashin.kyawun hanyar da su ka jima a ciki.

Hanyar ta Unguwar Rimi da ta dade a lalace har ta kai da damina ba ta saukin yiyuwa hakan ta sa Kungiyar ’Yantifa karkashin jagorancin Kwamred Mamunu Ibrahim Takai samar da kasa da a ka gudanar cike da dandabe hanyar.

samndaads

Da mu ka tuntube shi a kan dalilin gudanar da aiki Shugaban Hadaddiyar Kungiyar ta ’Yantifa na Jahar Kano ya ce, akalla hanyar da ta kai kilomita biyu da rabi, don haka su ka ga ya dace su gyara duba da su na su na da alaka da hanyar, domin motocinsu na bin ta su je debo kasa wannan kuma gyaran kyautata a takace tsakaninsu da al’ummar yankin.

Shugaban na ’Yantifa na Jahar Kano ya ce, aikin hanyar ya ci tifar kasa kusan 100, inda wannan kuma su ka samo gireda ta dandabe a ka kuma bi da motar ruwa.

Mamunu ya ce, akwai dai dai-daikun mutane da su ka ba su gudunmuwa akwai wanda shi ne ya samar da gireda da a ka dandabe kasar, sannan kuma akwai wani bawan Allah mai kamfanin kwangila da ta sa a ka kawo motar ruwa a yayin aikin.

Kwamred Mamuna Ibrahim Takai ya ce, akwai kungiyar cigaban al’ummar Unguwar da su ka jinjina mu su a kan aikin wanda zai mutukar rage mu su wahala da su ka dace a ciki. Ya kuma jaddada cewa, kungiyar tasu ta ’Yantifa a shirye ta ke wajen bada gudunmuwa da zai taimaka wa cigaban al’umma a kowane yanayi na saukaka rayuwa.

SendShareTweetShare
Previous Post

Kamfanonin Sarrafa Shinkafa Za Su Iya Wadata Nijeriya Da Shinkafa – Kurfi

Next Post

Kotu Ta Umarci Maina Da Ya Fara Gabatar Da Shaidun Kariya A Karshen Janairu

RelatedPosts

Makiyaya Ondo

Korar Makiyaya A Ondo: Cikakken Rahoton Yadda Ta Kaya Taron Gwamnoni Da Shugabannin Fulani

by Ibrahim Muhammad
16 hours ago
0

Daga Khalid Idris Doya, Gwamnonin Nijeriya sun kira taron gaggawa...

Kasafin 2021

Hotunan Sabbin Shugabannin Rundunonin Tsaro

by Ibrahim Muhammad
1 day ago
0

Major-Gen. Leo Irabor, Chief of Defence...

Garban

Garban Kauye Farawa Ne Allurar Dinke Barakar Kumbotso – Muslihu Yusuf Ali

by Ibrahim Muhammad
3 days ago
0

Daga Abdullahi Muhammad Sheka, An bayyana zaben Sabon shugaban Karamar...

Next Post
Maina

Kotu Ta Umarci Maina Da Ya Fara Gabatar Da Shaidun Kariya A Karshen Janairu

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version