• English
  • Business News
Sunday, October 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kungiyoyi Da Abokan Arziki Na Ci Gaba Da Taya Dantsoho Murna

by Bello Hamza and Sulaiman
1 month ago
Dantsoho

Kungiyoyi da kuma sauran abokan arziki, ba ci gaba data taya Shugaban Hukumar kula da Tashoshin Jiragen Ruwa ta Kasa NPA Dakta Abubakar Dantsoho bisa zama Mataimakin Shugaban Kungiyar Tashoshin Jiragen Ruwa ta duniya wato IAPH.

Daya daga cikin su ita ce, Hukumar Sufurin Jiragen Ruwa ta Kasa  wato NSC wadda Sakatarenta kuma shugabanta Dakta Akutah Pius Ukeyima, ya bayyana cewa, zabar Dantsoho a mukamin hakan ya nuna salon shugabancinsa, na tafiyar da Hukumar ta NPA, musamman yadda ya mayar da hankali, wajen kara bunkasa fannin na sufurin kasar.

“Wannan nasarar da  Dantsoho ya samu babban abin alfahari ne, ga kasar nan wanda kuma hakan ya nuna irin shugabanci na gari na Dantsoho ke ci gaba da yi ne, a bangaren Hukumar da kuma a bangren ruwa,” Inji Dakta Akutah.

Kazalika, Hukumar ta kuma jinjinawa Dakta Dantsoho kan samar da dabarun tsare-tsaren da suka kara saita fannin sufuri a kasar da kuma a fadin duniya.

Ya bayyana kwarin guiwarsa da cewa, shugabancin na Dantsoho, ya taimaka matuka wajen samar da damarmaki da dama a nahiyar Afirka, wanda hakan ya kuma kai Nijeriya ga wani babban mataki a bangaren sufurin Jiragen Ruwa a Afirka.

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Amince A Fara Aikin Tashoshin Jiragen Ruwa Na Apapa Da Kalaba Da Fatakwal Da Warri — NPA

Zan Tabbatar Ana Tafiyar Da Ayyuka A Tashoshin Jiragen Ruwa A Afrika Ta Yamma —Dantsoho

Ya kuma sanar da ci gaba da bai wa shugabancin Dakta Dantsoho goyon baya, musaman domin kara samar da sauye-sauyen da za su kara bunkasa hada-hadar zirga-zirga, da kuma a bangaren kara bunkasa kasuwancin tatalin azrki na Teku.

A nan kuma Kamfanin Rukunonin SIFAD, ya taya Dakta Dantsoho murnar zama Mataimakin Shugaban na kungiyar ta IAPH.

Hakan na kunshe ne, a cikin wata wasika da Shugaban Kamfanin Dakta Taiwo Afolabi CON ya fitar ta taya murnar, inda ya danganta zabar Dantsoho kan mukamanin a matsyin abinda ya dace, musamman duba irin salon shugabanci na gari na Dakta Dantsoho, wanda hakan ya sanya ya samar da gagarumar gudunmawa a bangaren sufurin Jiragen Ruwa na kasar.

Shugaban sashen samar da bayanai na Kamfanin  Mista Olumuyiwa Akande, ya bayyana haka a cikin wata sanarwa da ya fitar.

“Wannan zaben na ka ya nuna irin kwarewar da kake da ita da kuma shekarun da ka shafe, kana yiwa Hukumar aiki wadda ta faro tun daga lokacin da ka yi aikin yiwa kasa hidima a Hukumar a shekarar 1992, inda a yanzu kuma ka kasance shugaban Hukumar ta NPA, “ A cewar Afolabi.

Ya kara da cewa, iya salon shugabanci na gari da kuma sauye-sayen da Dakta Dantsoho ya samar a hukumar, sun kara karfafa ayyukan Tashoshin Jiragen Ruwan Kasar.

A cewarsa, nasarorin da shugaban ya samar a Hukumar ba wai Hukumar ce kadai za ta amfana ba, har da daukacin fadin nahiyar Afirka

Kamfanin ya kuma bayyana kwarin airin Dakta Dantsoho zai yi amfani da sabbin dabarunsa na kara karfafa hadaka domin kai Afirka .

“Kamfanin na alfahari da nasarorin da ka samar da kuma ci gaba da kara ciyar da Hukumar gaba,”Inji Afolabi.

Kazalika, Kamfanin na SIFAD ya kuma kara jaddda goyon bayansa kan shiye-shiryen da Hukumar ke ci gaba da yin a kara ciyar da Hukumar gaba

Ya kuma ayyana ci gaba da yin hadaka da Hukumar ta NPA, musamman domin kara fadada gasa a bangaren sufurin Jiragen Ruwa na kasar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tinubu Ya Amince A Fara Aikin Tashoshin Jiragen Ruwa Na Apapa Da Kalaba Da Fatakwal Da Warri — NPA
Tattalin Arziki

Tinubu Ya Amince A Fara Aikin Tashoshin Jiragen Ruwa Na Apapa Da Kalaba Da Fatakwal Da Warri — NPA

October 17, 2025
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho
Tattalin Arziki

Zan Tabbatar Ana Tafiyar Da Ayyuka A Tashoshin Jiragen Ruwa A Afrika Ta Yamma —Dantsoho

October 17, 2025
sallah
Tattalin Arziki

Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci’ Yan Nijeriya Su Rika Sayen Kayan Da Aka Sarrafa A Gida

October 11, 2025
Next Post
Zulum Ya Ba Da Tallafin ₦300,000 Ga Iyaye, Da Ciyar Da Ɗalibai 90 Kyauta A Borno

Zulum Ya Ba Da Tallafin ₦300,000 Ga Iyaye, Da Ciyar Da Ɗalibai 90 Kyauta A Borno

LABARAI MASU NASABA

gombe

Ɗaliban Jihar Gombe Sun Samu Ƙarin Kashi 100 Na Kuɗin Tallafin Karatu

October 18, 2025
Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

October 18, 2025
An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

October 18, 2025
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya

DHQ Ta Ƙaryata Rahoton Yunƙurin Yi Wa Tinubu Juyin Mulki

October 18, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas

‘Yansanda Sun Kai Samame Maboyar ‘Yan Ta’adda, Sun Kwato Miyagun Kwayoyi A Gombe

October 18, 2025
Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya

Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya

October 18, 2025
ASUU

Cikin Wata 9 Farfesoshi 309 Sun Bar Aiki A Jami’o’in Gwamnati, In Ji ASUU

October 18, 2025
Masanin Ilimin Physics Chen Ning Yang Ya Rasu Yana Da Shekaru 103

Masanin Ilimin Physics Chen Ning Yang Ya Rasu Yana Da Shekaru 103

October 18, 2025
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

October 18, 2025
Kasar Sin Ta Gargadi Amurka Game Da Yunkurin Samarwa Yankin Taiwan Makamai

Kasar Sin Ta Gargadi Amurka Game Da Yunkurin Samarwa Yankin Taiwan Makamai

October 18, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.