• English
  • Business News
Thursday, May 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kwamishinan Kasafin Kudin Jihar Zamfara Ya Bar APC Ya Koma PDP

by Bello Hamza
2 years ago
in Siyasa
0
Kwamishinan Kasafin Kudin Jihar Zamfara Ya Bar APC Ya Koma PDP
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwamishinan kasafin kudi a Zamfara ya saki tafiyar APC, ya kama jam’iyyar PDP mai adawa gabanin zaben 2023.

Alhaji Aliyu ya bayyana cewa, ba zai ci gaba da zama a jam’iyyar da gazawarta ta fi nasararta yawa ba, tuni dan takarar gwamnan jihar Zamfara a PDP ya karbi kwamishinan tare da bayyana kwarin gwiwa a zaben bana.

  • PDP Ta Kori Nnamani, Ogbu, Dan Fayose, Da Wasu Daga Jam’iyyar
  • Mataimakin Gwamnan Sakkwato, Dan Iya, Ya Musanta Ficewa Daga PDP

Sabon rikici na kunno kai a jam’iyyar APC a jihar Zamfara yayin da kwamishinan gwamna Muhammad Bello Matawalle ya sauya sheka zuwa jam’iyyar PDP.

Kwamishinan kasafin kudi da tattalin arziki, Alhaji Aliyu Tukur E.S Mafara a wani taron ‘yan jarida a Gasau a ranar Juma’a ya ce ya bar jam’iyyar APC tare da komawa PDP; ya marawa dan takarar gwamnan PDP a jihar, Dauda Lawal.

Alhaji Mafara na daya daga cikin jiga-jigan jam’iyyar APC a jihar Zamfara kuma yana daga cikin masu fada a ji a siyasar jihar, LEADERSHIP ta ruwaito.

Labarai Masu Nasaba

PDP Ta Sake Zaɓar Amb. El-Gash A Yobe

Kyakkyawan Tunanin Kwankwaso Na Kafa Jami’ar Kimiyya Ta Wudil Ta Zama Alkairi Ga Al’umma – Alhaji Abdukadir

Da yake magana bayan ganawa da dan takarar gwamnan na PDP, tsohon kwamishinan ya jaddada cewa, ba zai bari ya ci gaba da zama a inda abu ya ki gaba ya ki baya ba.

A cewarsa: “Na sanar da gwamnatin jihar, tsohon gwamna da kuma mabiya bayana gabanin sauya sheka daga APC zuwa PDP.

“Ina yin wannan ne saboda mutane na, kuma ina da yakini kan Dr. Dauda Lawal, idan aka ba shi dama ya zama gwamnan Zamfara a zabe mai zuwa, zai shawo kan matsalolin tsaro, ya habaka harkar noma, ya samar da kasuwanni masu kyau ga manoma.

“Saboda haka, na ba da dukkan goyon baya na ga jam’iyyar PDP, kuma ina son yin kira ga magoya bayana a Zamfara da su bi tafiyar Dauda Lawal da PDP a zabe mai zuwa.”

Dan takarar gwamnan PDP ya magantu A nasa bangaren, dan takarar gwamnan jihar Zamfara na PDP, Dauda Lawal, ya tabbatar da cewa, Zamfara jiha ce ta PDP, inda ya kara da cewa, jam’iyyar za ta sake samun nasarar karbe mulki a zaben 2023.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Bashin Dala Miliyan 350 Da Kaduna Ta Ciyo: Nasara Ko Akasinta?

Next Post

Gakpo Ya Yi Gaggawar Koma Wa Liverpool, Cewar Koeman

Related

PDP Ta Sake Zaɓar Amb. El-Gash A Yobe
Siyasa

PDP Ta Sake Zaɓar Amb. El-Gash A Yobe

4 days ago
Kyakkyawan Tunanin Kwankwaso Na Kafa Jami’ar Kimiyya Ta Wudil Ta Zama Alkairi Ga Al’umma – Alhaji Abdukadir
Ilimi

Kyakkyawan Tunanin Kwankwaso Na Kafa Jami’ar Kimiyya Ta Wudil Ta Zama Alkairi Ga Al’umma – Alhaji Abdukadir

4 days ago
Majalisar Wakilai Ta Yi Watsi Da Kafa Dokar Karba-karba A Shugabancin Nijeriya
Siyasa

Majalisar Wakilai Ta Yi Watsi Da Kafa Dokar Karba-karba A Shugabancin Nijeriya

5 days ago
A Tsammaci Garambawul Ga Dokar Zabe Kafin Zaben 2027 — Shugaban INEC
Siyasa

A Tsammaci Garambawul Ga Dokar Zabe Kafin Zaben 2027 — Shugaban INEC

6 days ago
NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC
Siyasa

NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

7 days ago
Rikicin Ribas: Fubara Ya Ce Ya San Yadda Zai Magance Matsalar, Ya Gargaɗi Magoya Bayansa
Labarai

Rikicin Ribas: Fubara Ya Ce Ya San Yadda Zai Magance Matsalar, Ya Gargaɗi Magoya Bayansa

1 week ago
Next Post
Gakpo Ya Yi Gaggawar Koma Wa Liverpool, Cewar Koeman

Gakpo Ya Yi Gaggawar Koma Wa Liverpool, Cewar Koeman

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Tarwatsa Wuraren Haɗa Jabun Taki A Bauchi, An Cafke Mutum 5

‘Yansanda Sun Tarwatsa Wuraren Haɗa Jabun Taki A Bauchi, An Cafke Mutum 5

May 21, 2025
Kocin Super Eagle Ya Gayyaci Ahmed Musa Buga Gasar Kofin Unity A Landan

Kocin Super Eagle Ya Gayyaci Ahmed Musa Buga Gasar Kofin Unity A Landan

May 21, 2025
Farar Dabarar Da Tsoffin Masana’antu Ke Yi A Kasar Sin Don Tafiya Da Zamani

Farar Dabarar Da Tsoffin Masana’antu Ke Yi A Kasar Sin Don Tafiya Da Zamani

May 21, 2025
Tottenham Ta Doke Manchester United A Wasan Karshe Na Europa 

Tottenham Ta Doke Manchester United A Wasan Karshe Na Europa 

May 21, 2025
Kotu Ta Soke Umarnin Kwace Filin Asibitin Tiamin, Ta Umarci Gwamnatin Kano Ta Biya Diyyar ₦2.6bn

Kotu Ta Soke Umarnin Kwace Filin Asibitin Tiamin, Ta Umarci Gwamnatin Kano Ta Biya Diyyar ₦2.6bn

May 21, 2025
Shirye-shiryen Tinubu Suna Buɗe Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arzikin Nijeriya – Minista

Shirye-shiryen Tinubu Suna Buɗe Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arzikin Nijeriya – Minista

May 21, 2025
Salon “Kasa Daya Manufa Daya” Ya Dace Da “Ayyuka Goma” Na Hadin Gwiwa Da Afirka

Salon “Kasa Daya Manufa Daya” Ya Dace Da “Ayyuka Goma” Na Hadin Gwiwa Da Afirka

May 21, 2025
Sin Tana Da Karfi Wajen Tinkarar Hadari Da Kalubale A Fannoni Daban Daban

Sin Tana Da Karfi Wajen Tinkarar Hadari Da Kalubale A Fannoni Daban Daban

May 21, 2025
Sabbin Ministoci

Boko Haram: Majalisar Dattijai Ta Amince Da Kafa Sansanin Sojoji A Hong Ta Jihar Adamawa

May 21, 2025
Sin Ta Soki Yunkurin Amurka Na Hana Amfani Da Chips Kirar Kasar Sin

Sin Ta Soki Yunkurin Amurka Na Hana Amfani Da Chips Kirar Kasar Sin

May 21, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.