• English
  • Business News
Saturday, November 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kwamishinan ‘Yansandan Abuja Ya Gargadi Jami’ansa Kan Arangama Da Direbobi A Titi

by Rabi'u Ali Indabawa and Sulaiman
2 months ago
Yansanda

Kwamishinan ‘Yansanda na Babban Birnin Tarayya (FCT), CP Ajao Adewale, ya gargadi jami’an ‘yansanda da na kula da zirga-zirga kan yin tsalle cikin motocin da ke tafe ko kuma jan sitiyarin direbobi, yana mai bayyana irin wannan hali a matsayin abin da bai da tsaro, bai dace ba, kuma yana lalata mutuncin Rundunar ‘Yansanda ta Najeriya (NPF).

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun ‘yansandan FCT, SP Josephine Adeh, ta fitar a Abuja, ta ce Kwamishinan ‘Yansanda ya yi Allah-wadai da dabi’ar rashin kwarewa ta jami’an zirga-zirga na yin tsalle cikin motocin masu karya doka ko kuma yunkurin kwace sitiyarin direbobi. CP ya bayyana irin wadannan ayyuka a matsayin masu hadari, da ba za a aminta da su ba, kuma ya sabawa ka’idojin aikin ‘yansanda.

Adeh ta ce CP ya kuma sanar da kaddamar da aikin musamman mai suna Operation Keep Traffic Flowing, inda aka kafa tawagar sa ido domin tabbatar da bin wannan umarni, tare da gargadin cewa duk jami’in da aka samu yana keta wadannan dokoki za a hukunta shi.

“CP ya bayyana fara aikin gaggawa na Operation ‘Keep Traffic Flowing’, kuma ya kafa tawagar sintiri domin bibiyar ayyukan jami’an zirga-zirga gaba kaya, tare da umarni na musamman kan kama duk wani jami’i da aka samu da karya wannan doka,” in ji ta.

Hakazalika, CP ya bayyana muhimman wuraren da ke da cunkoson zirga-zirga a Abuja, ya kuma gargadi jami’an sintiri kan gujewa dabi’ar rashin kwarewar yin tsalle cikin motocin masu laifi.

LABARAI MASU NASABA

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna

A jawabin da ya yi wa shugabannin sashen sintiri, jami’an ‘yansandan motoci, da sauran jami’an da ke aiki a hedikwatar rundunar, CP ya ce halayen jami’an sintiri a fili suke bayyana hoton da al’umma ke da shi game da rundunar ‘yansanda.

Adeh ta bayyana cewa CP ya nuna rashin jin dadinsa kan yadda jami’ai ke gudanar da ayyuka a halin yanzu, yana mai jaddada cewa kula da zirga-zirga na daga cikin manyan alamomin nuna ci gaban gari.

Bayan ya yi yawon duba wurare da dama a birnin a lokutan cunkoso, CP ya gano muhimman wurare kusan 30 da ke da matsalar zirga-zirga, ciki har da Wuse, Area 1 Roundabout, Jikwoyi, Karu, Kurudu, AYA, Apo Resettlement, Gudu, Galadima, Dawaki, da Kubwa.

Ya umarci jami’ai da su kasance a bayyane a wadannan wurare domin tabbatar da tafiyar zirga-zirga yadda ya kamata.

“CP Adewale ya bayyana rashin jin dadinsa kan yadda jami’an sintiri ke gudanar da aikinsu yanzu, yana mai jaddada bukatar sabuwar fahimtar aiki. Ya ce harkar sintiri na daga cikin muhimman alamu na auna tsari da ci gaban gari, yayin da jami’an zirga-zirga suke kasancewa hoton farko da jama’a ke gani daga ‘yansanda.

“A kan haka, ya gargade su da su kiyaye ladubban aiki da bin doka, su guji duk wani hali marar kyau da zai iya bata sunan rundunar gaba daya da kuma na FCT musamman,” in ji PPRO.

Ya kuma roki mazauna birnin da su bi dokokin zirga-zirga, su mutunta jami’an da ke bakin aiki, su kuma guji bayar da cin hanci, wanda ya bayyana a matsayin abin da bai dace ba. Ya tabbatar wa jama’a cewa rundunar za ta ci gaba da kasancewa a fili tare da tabbatar da ingantacciyar tafiyar zirga-zirga a FCT.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma
Manyan Labarai

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

November 7, 2025
APC Da Uba Sani Ba Su Lashe Zaben Gwamnan Kaduna Ba -PDP
Labarai

Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna

November 7, 2025
Jerin Gwarazan Taurarinmu!
Rahotonni

Jerin Gwarazan Taurarinmu!

November 7, 2025
Next Post
Arewa

Matsalar Tsaro: Gwamnonin Arewa Sun Bullo Da Sabbin Matakan Yaki Da Ta’addanci

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Shirin Shugaba Tinubu Na ‘Renewed Hope’ Zai Karfafa Wa Manoma Gwiwa – Oyebanji

November 7, 2025
Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

November 7, 2025
Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

November 7, 2025
An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

November 7, 2025
Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

November 7, 2025
An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

November 7, 2025
APC Da Uba Sani Ba Su Lashe Zaben Gwamnan Kaduna Ba -PDP

Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna

November 7, 2025
Kasar Sin Ta Musanta Zargin Da Wakilin Amurka Ya Yi Game Da Batun Sauyin Yanayi

Kasar Sin Ta Musanta Zargin Da Wakilin Amurka Ya Yi Game Da Batun Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Halarci Taron COP30 A Brazil

Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Halarci Taron COP30 A Brazil

November 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.