ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

LEADERSHIP Da CMG Sun Karfafa Dangantakar Aiki A Tsakaninsu

by Sadiq
3 years ago
Leadership

Kamfanin LEADERSHIP wallafa jaridar Leadership ta Turanci da Hausa, sun kara karfafa dangantakarsa da kamfanin yada labarai na Kasar Sin (CMG) don fadada aiki tsakanin kamfanonin biyu.

Wannan ci gaban ya samo asali ne lokacin da tawagar CMG karkashin jagorancin babban daraktan cibiyar shirye-shiryen harsunan Asiya da Afirka, An Xiaoyu, ta kai ziyarar aiki hedikwatar kamfanin LEADERSHIP da ke Abuja a ranar Talata.

  • Fadan Sudan Ya Hana Kananan Yara Samun Ilimi —UNICEF
  • Dokokin Da Buhari Ya Sanya Wa Hannu Kafin Barin Mulki

Sun rattaba hannu kan wata yarjejeniya da ke da nufin kawo sabbin matakai da za su amfanar da kamfanonin biyu.

ADVERTISEMENT

Da take maraba da tawagar CMG, shugabar kamfanin LEADERSHIP Group Limited, Misis Zainab Nda-Isaiah, ta ce ziyarar ta yi daidai domin za ta karfafa hadin gwiwar da ke tsakanin manyan kafafen yada labarai biyu da aka fara a shekarar 2018.

Ta kuma kara da cewa, kamfanin LEADERSHIP na da tsari da hangen nesa don bunkasa ayyukansa, ta kuma bukaci kafar ta kasar Sin da ta taka muhimmiyar rawa wajen ciyar da dangantakar da ke tsakaninsu zuwa wani mataki.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

Ta ce, “Idan muka sa wannan hadin gwiwa ya kasance mai amfani ta hanyar cika yarjejeniyar da muka yi, jama’armu za su amfana, ba a iya kanmu kadai ba har jikokinmu.”

Dangantakar dai ta fara ne daga wallafa labaran kasar sin a shafin “Daga Sin,” na LEADERSHIP Hausa wanda daga bisani aka samar masa da shafinna musamman q jaridar Hausa mai suna “Baban Bongo”.

Madam Nda-Isaiah ta kuma yaba wa gwamnatin kasar Sin bisa tsauraran ka’idoji da takunkumin da ta dauka kan yada labaran karya.

Ta bayyana cewa hakan zai magance rashin dacewar da wasu shafukan sada zumunta ke yi, da kuma dakile barazanar da labaran karya ke yi wa al’umma.

“Yana da kyau a samar da ka’idoji kan yada labaran karya don magance munanan illolinsa ga al’umma. Yana da kyau gwamnatin kasar Sin ta dauki nauyi,” in ji ta.

Ta kuma ba da tabbacin cewa LEADERSHIP za ta samu lokaci don kai wa CMG ziyara.

A nasa bangaren, Xiaoyu ya ce kofar CMG a bude take ga duk wani nau’in hadin gwiwa daga kamfanin LEADERSHIP, musamman kan kafafen yada labarai.

Ya kuma bayyana cewa, CMG za ta fadada shirye-shiryensa na horas da ma’aikatan LEADERSHIP don samun ci gaba a fannin aikinsu.

MASU ALAKA

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan
Manyan Labarai

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Next Post
Ina Neman Gafarar ‘Yan Nijeriya Idan Na Muku Ba Dai-dai Ba —Buhari

Buhari Ya Nemi Majalisa Ta Biya Bashin Shari'a N226bn, $556.8m, £98.5m

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026
‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

July 15, 2026
Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.