• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Lalong Ya Yi Allah-wadai Da Kashe-kashen Da Aka Yi A Filato, Ya Bukaci A Gurfanar Da Masu Laifin

by Sadiq
3 years ago
in Labarai
0
Lalong Ya Yi Allah-wadai Da Kashe-kashen Da Aka Yi A Filato, Ya Bukaci A Gurfanar Da Masu Laifin
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamna Simon Lalong na Jihar Filato, ya yi Allah-wadai da harin da aka kai a daren ranar Talata a unguwar Maikatako da ke gundumar Butura ta karamar hukumar Bokkos, wanda ya yi sanadin mutuwar mutane 11 tare da jikkata wasu mutane takwas.

A wata sanarwa da Daraktan yada labarai da hulda da jama’a na Jihar, Makut Machan ya fitar, Lalong ya bukaci jami’an tsaro a jihar da su kamo wadanda suka aikata wannan aika-aika domin gurfanar da su a gaban kuliya.

  • Sin Za Ta Kara Raya Sana’o’in Dake Shafar Kasuwar Sinadarin Carbon
  • Dakarun Soji A Jihar Kaduna Sun Kara Kashe Wani Jagoran ‘Yan Bindiga Gudau Kachalla

Gwamnan wanda ya jajantawa iyalan wadanda harin ya rutsa da su, ya nanata cewa gwamnatinsa ba za ta bari ‘yan ta’adda da ‘yan bindiga su kai hari a wani yanki na jihar ba saboda an umarci dukkanin hukumomin tsaro da su tabbatar da ta yi maganin duk wani mutum ko kungiyar da ta kai harin. .

A cewarsa, yawaitar hare-hare da lalata amfanin gonaki, dabbobi, da sauran dukiyoyi a karamar hukumar ta Bokkos, na zama abin damuwa, kuma dole ne a duba su cikin gaggawa.

Wasu da ake zargin makiyaya ne sun afkawa al’ummar yankin da misalin karfe 11 na daren ranar Talata, inda suka kona gidaje hudu a harin, sannan suka fara harbi ba kakkautawa bayan da suka mamaye ‘yan banga da ke sintiri.

Labarai Masu Nasaba

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

An ce guda tara daga cikin wadanda abin ya shafa an kona su ne ta yadda ba za a iya gane su ba a wani waje, yayin da sauran kuma aka same su da sanyin safiyar Laraba a gidajensu da suka kone bayan an harbe su.

Wani dan unguwar ya tuna cewa harin ba gaira ba dalili ya fara ne bayan ranar kasuwar Litinin ta mako-mako inda aka harbe wani yaro a Hilltop, wanda ke da tazarar kilomita daga Maikatako.

Rahotanni sun ce lamarin harbin ya haifar da tashin hankali a tsakanin al’ummar a ranar Talata duk da cewa ‘yan banga sun yi kokarin fatattakar maharan.

Da yake tabbatar da faruwar lamarin, kakakin rundunar ‘yansandan Jihar Filato, Alfred Alabo, ya ce har yanzu bai samu cikakken bayanin lamarin ba.

Sai dai kwamandan rundunar ‘Operation Safe Haven’ Manjo-Janar Ibrahim Ali, ya bayyana cewa rundunar tsaron da aka bai wa alhakin kula da al’amuran tsaro a Filato, da kuma wasu sassan jihohin Bauchi da Kaduna, sun kasance a kasa don shirin ko ta kwana.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: FilatoKashe-kasheKauyeMaharaMazauna
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kotu Ta Kori Karar Da Maina Ya Shigar Kan Ministan Harkokin Cikin Gida Da Wasu

Next Post

Duk Bayan Shekaru 8 Ya Kamata Ake Sauya Fasalin Naira – Shugaban EFCC

Related

Daurarru
Labarai

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

8 hours ago
Wutar lantarki
Labarai

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

10 hours ago
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka
Labarai

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

11 hours ago
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano
Manyan Labarai

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

12 hours ago
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu
Labarai

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

14 hours ago
Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara
Labarai

Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

15 hours ago
Next Post
Duk Bayan Shekaru 8 Ya Kamata Ake Sauya Fasalin Naira – Shugaban EFCC

Duk Bayan Shekaru 8 Ya Kamata Ake Sauya Fasalin Naira - Shugaban EFCC

LABARAI MASU NASABA

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.