• English
  • Business News
Saturday, July 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Lamine Yamal Na Fuskantar Bincike Kan Bikin Zagayowar Ranar Haihuwarsa A Spain

by Abba Ibrahim Wada and Sulaiman
4 hours ago
in Wasanni
0
Lamine Yamal Na Fuskantar Bincike Kan Bikin Zagayowar Ranar Haihuwarsa A Spain
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ma’aikatar kare hakkin jama’a ta Sifaniya ta bukaci ofishin mai shigar da kara na kasar da ya binciki dan wasan gefe na Barcelona Lamine Yamal bayan da aka ce ya dauki hayar gajerun mutane zuwa wajen bikin cikarsa shekaru 18 da haihuwa, Lamine Yamal ya shirya liyafa a ranar Lahadi a wani wajen da ya dauka haya a Olibella, wani karamin gari mai tazarar kilomita 50 arewa maso yammacin Barcelona, a cikin wadanda suka halarci bikin akwai masu amfani da shafukan YouTube, mawaka da abokan wasansa a Barcelona da dama.

Ana zargin Lamine Yamal ya dauki hayar gungun masu wasan nishadi da ake kira da (Dwarf) wato wadanni domin nishadantar da mahalarta taron, wani abu da kungiyar mutanen da ke fama da ciwon Achondroplasia da sauran matsaloli na kashi (Skeletal Dysplasias) a kasar Sifaniya (ADEE) suka kira da abin da ba a yarda da shi ba a karni na 21, Darakta Janar na Nakasassu, wani bangare na Ma’aikatar Kare Hakkin Jama’a, ya ce kungiyar ADEE ta shigar da karar akan Yamal.

  • Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (6)
  • Mutuwar Malamin Jami’a A Otel: Jami’ar Kogi Za Ta Gudanar Da Bincike

Saboda haka, Darakta Janar din ya bukaci ofishin mai gabatar da kara da ya yi bincike domin sanin ko an tauye hakkokin nakasassu ko kuma an keta hakkin nakasassu, ADEE ta ce “Ta fito fili ta yi Allah wadai da daukar wadannin da ke da ra’ayin mazan jiya a matsayin wani bangare na nishadantarwa, kuma ta ce za ta dauki matakin shari’a saboda wannan ka iya zama wata hanya ta nuna wariya a tsakanin nakasassu da sauran mutane a kasar ta Sifaniya da ake yawan samun kararraki na nuna wariyar launin fata,” in ji shi.

A cikin wata sanarwa da ta fitar ta ce “Wadannan ayyuka ba wai kawai sun saba wa dokokin da ake da su a yanzu ba, har ma da muhimman ka’idojin da’a na al’ummar da ke neman daidaito da mutuntawa, akwai doka game da hakkin nakasassu da ta haramta ayyukan nakasassu a fili kamar aikata ayyukan nishadi a wajen taron jama’a ko wajen bukukuwa, wadanda ake amfani da nakasassu ko wasu masu rashin lafiya wajen yin izgili ko ba’a, wanda hakan ya matukar saba wa dokar mutunta dan’Adam,” in ji sanarwar.

 

Labarai Masu Nasaba

Kamfanin Puma Zai Biya Man City Fam Biliyan 1 A Shekara 10 Domin Samar Wa Kungiyar Kayan Wasa

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Wakilin Sin: Hukumar Shiga Tsakani Ta Duniya Za Ta Karfafa Warware Takaddamar Kasa Da Kasa Cikin Lumana

Next Post

Xia Xueying: Muna Sayo Kashi 90% Na Kayan Aikinmu Daga Kasar Sin

Related

Kamfanin Puma Zai Biya Man City Fam Biliyan 1 A Shekara 10 Domin Samar Wa Kungiyar Kayan Wasa
Wasanni

Kamfanin Puma Zai Biya Man City Fam Biliyan 1 A Shekara 10 Domin Samar Wa Kungiyar Kayan Wasa

1 hour ago
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0
Wasanni

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

1 day ago
Osimhen Na Dab Da Komawa Galatasaray Na Dindindin
Wasanni

Osimhen Na Dab Da Komawa Galatasaray Na Dindindin

5 days ago
Chelsea Ta Kafa Babban Tarihi Bayan Lashe Kofin Duniya Na Ƙungiyoyi
Wasanni

Chelsea Ta Kafa Babban Tarihi Bayan Lashe Kofin Duniya Na Ƙungiyoyi

6 days ago
Abubuwa 5 da Ya Kamata Ku Sani Game da Wasan Ƙarshe Tsakanin Chelsea Da PSG
Wasanni

Abubuwa 5 da Ya Kamata Ku Sani Game da Wasan Ƙarshe Tsakanin Chelsea Da PSG

7 days ago
Abubuwa 10 Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Peter Rufai, Fitaccen Golan Nijeriya
Wasanni

Abubuwa 10 Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Peter Rufai, Fitaccen Golan Nijeriya

7 days ago
Next Post
Xia Xueying: Muna Sayo Kashi 90% Na Kayan Aikinmu Daga Kasar Sin

Xia Xueying: Muna Sayo Kashi 90% Na Kayan Aikinmu Daga Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Kamfanin Puma Zai Biya Man City Fam Biliyan 1 A Shekara 10 Domin Samar Wa Kungiyar Kayan Wasa

Kamfanin Puma Zai Biya Man City Fam Biliyan 1 A Shekara 10 Domin Samar Wa Kungiyar Kayan Wasa

July 19, 2025
An Yi Taron Farko Na Shugabannin Matasa Na Dandalin Zaman Lafiya Da Tsaro Na Sin Da Afirka

An Yi Taron Farko Na Shugabannin Matasa Na Dandalin Zaman Lafiya Da Tsaro Na Sin Da Afirka

July 19, 2025
Yadda Donal Trump Ya Lashe Zaben Shugabancin Amurka

Putin Ya Fita Daga Raina – Trump

July 19, 2025
Kasar Sin Ta Ba Da Rahoton Samun Ci Gaban Aikin Gona Mara Gurbata Muhalli Ba Tare Da Tangarda Ba

Kasar Sin Ta Ba Da Rahoton Samun Ci Gaban Aikin Gona Mara Gurbata Muhalli Ba Tare Da Tangarda Ba

July 19, 2025
Dole Mu Hada Kai Da ‘Yan Siyasa Don Ciyar Da Masana’antar Kannywood Gaba -Shugaban MOPPAN

Dole Mu Hada Kai Da ‘Yan Siyasa Don Ciyar Da Masana’antar Kannywood Gaba -Shugaban MOPPAN

July 19, 2025
Xia Xueying: Muna Sayo Kashi 90% Na Kayan Aikinmu Daga Kasar Sin

Xia Xueying: Muna Sayo Kashi 90% Na Kayan Aikinmu Daga Kasar Sin

July 19, 2025
Lamine Yamal Na Fuskantar Bincike Kan Bikin Zagayowar Ranar Haihuwarsa A Spain

Lamine Yamal Na Fuskantar Bincike Kan Bikin Zagayowar Ranar Haihuwarsa A Spain

July 19, 2025
Wakilin Sin: Hukumar Shiga Tsakani Ta Duniya Za Ta Karfafa Warware Takaddamar Kasa Da Kasa Cikin Lumana

Wakilin Sin: Hukumar Shiga Tsakani Ta Duniya Za Ta Karfafa Warware Takaddamar Kasa Da Kasa Cikin Lumana

July 19, 2025
‘Yan Makaranta Sun Kera Mota Mai Amfani Da Lantarki A Sakkwato

‘Yan Makaranta Sun Kera Mota Mai Amfani Da Lantarki A Sakkwato

July 19, 2025
Xi Da Takwaransa Na Mauritania Ghazouani Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 60 Da Kulla Huldar Diflomasiyya

Xi Da Takwaransa Na Mauritania Ghazouani Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 60 Da Kulla Huldar Diflomasiyya

July 19, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.