• English
  • Business News
Tuesday, November 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Lamine Yamal Na Fuskantar Bincike Kan Bikin Zagayowar Ranar Haihuwarsa A Spain

by Abba Ibrahim Wada and Sulaiman
4 months ago
Lamine

Ma’aikatar kare hakkin jama’a ta Sifaniya ta bukaci ofishin mai shigar da kara na kasar da ya binciki dan wasan gefe na Barcelona Lamine Yamal bayan da aka ce ya dauki hayar gajerun mutane zuwa wajen bikin cikarsa shekaru 18 da haihuwa, Lamine Yamal ya shirya liyafa a ranar Lahadi a wani wajen da ya dauka haya a Olibella, wani karamin gari mai tazarar kilomita 50 arewa maso yammacin Barcelona, a cikin wadanda suka halarci bikin akwai masu amfani da shafukan YouTube, mawaka da abokan wasansa a Barcelona da dama.

Ana zargin Lamine Yamal ya dauki hayar gungun masu wasan nishadi da ake kira da (Dwarf) wato wadanni domin nishadantar da mahalarta taron, wani abu da kungiyar mutanen da ke fama da ciwon Achondroplasia da sauran matsaloli na kashi (Skeletal Dysplasias) a kasar Sifaniya (ADEE) suka kira da abin da ba a yarda da shi ba a karni na 21, Darakta Janar na Nakasassu, wani bangare na Ma’aikatar Kare Hakkin Jama’a, ya ce kungiyar ADEE ta shigar da karar akan Yamal.

  • Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (6)
  • Mutuwar Malamin Jami’a A Otel: Jami’ar Kogi Za Ta Gudanar Da Bincike

Saboda haka, Darakta Janar din ya bukaci ofishin mai gabatar da kara da ya yi bincike domin sanin ko an tauye hakkokin nakasassu ko kuma an keta hakkin nakasassu, ADEE ta ce “Ta fito fili ta yi Allah wadai da daukar wadannin da ke da ra’ayin mazan jiya a matsayin wani bangare na nishadantarwa, kuma ta ce za ta dauki matakin shari’a saboda wannan ka iya zama wata hanya ta nuna wariya a tsakanin nakasassu da sauran mutane a kasar ta Sifaniya da ake yawan samun kararraki na nuna wariyar launin fata,” in ji shi.

A cikin wata sanarwa da ta fitar ta ce “Wadannan ayyuka ba wai kawai sun saba wa dokokin da ake da su a yanzu ba, har ma da muhimman ka’idojin da’a na al’ummar da ke neman daidaito da mutuntawa, akwai doka game da hakkin nakasassu da ta haramta ayyukan nakasassu a fili kamar aikata ayyukan nishadi a wajen taron jama’a ko wajen bukukuwa, wadanda ake amfani da nakasassu ko wasu masu rashin lafiya wajen yin izgili ko ba’a, wanda hakan ya matukar saba wa dokar mutunta dan’Adam,” in ji sanarwar.

 

LABARAI MASU NASABA

Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba

Wolves Ta Kori Da Kocinta Vitor Pereira Sakamakon Rashin Nasara

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba
Wasanni

Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba

November 2, 2025
Wolves Ta Kori Da Kocinta Vitor Pereira Sakamakon Rashin Nasara
Wasanni

Wolves Ta Kori Da Kocinta Vitor Pereira Sakamakon Rashin Nasara

November 2, 2025
Shin Mene Ne Matsalar Liverpool A Wannan Kakar?
Wasanni

Shin Mene Ne Matsalar Liverpool A Wannan Kakar?

November 2, 2025
Next Post
Xia Xueying: Muna Sayo Kashi 90% Na Kayan Aikinmu Daga Kasar Sin

Xia Xueying: Muna Sayo Kashi 90% Na Kayan Aikinmu Daga Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Jami’an Tsaro Sun Dawo Da Fasfo Ɗin Sanata Natasha Bayan Ƙwace Shi A Abuja

Natasha Ta Zargi Akpabio Da Sanya Jami’an Tsaro Su Ƙwace Mata Fasfo A Filin Jirgin Saman Abuja 

November 4, 2025
Masu Kashe Mutane A Kudu Maso Gabas Kiristoci Ne – Soludo

Masu Kashe Mutane A Kudu Maso Gabas Kiristoci Ne – Soludo

November 4, 2025
Ribadu Ya Gana Da Hafsoshin Tsaro Biyo Bayan Kalaman Trump 

Ribadu Ya Gana Da Hafsoshin Tsaro Biyo Bayan Kalaman Trump 

November 4, 2025
Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin

Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin

November 3, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce

Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce

November 3, 2025
An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau

An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau

November 3, 2025
“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

November 3, 2025
Shugabannin Wasu Kasashe Za Su Halarci Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas A Birnin Shanghai

Shugabannin Wasu Kasashe Za Su Halarci Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas A Birnin Shanghai

November 3, 2025
Li Qiang Zai Halarci Bikin Bude Taron CIIE Na 8 Da Sauran Ayyuka

Li Qiang Zai Halarci Bikin Bude Taron CIIE Na 8 Da Sauran Ayyuka

November 3, 2025
Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya

Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya

November 3, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.