• English
  • Business News
Monday, September 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

LEADERSHIP Ta Jinjina Wa Shehu Isma’ila Mai Diwani Kan Shafin Dausayin Musulunci

by Shehu Yahaya
2 years ago
in Labarai
0
LEADERSHIP Ta Jinjina Wa Shehu Isma’ila Mai Diwani Kan Shafin Dausayin Musulunci
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Biyo bayan gagarumar gudummawar da yake bayarwa a Jaridar LEADERSHIP Hausa wajen gabatar da darussan addini a shafin Dausayin Musulunci tun daga 2014, Mahukuntan Kamfanin LEADERSHIP sun mika takardar yabo da godiya ga Shehu Isma’il Umar Almadda da aka fi sani da “Mai Diwani”, a zawiyyarsa da ke Tudun Wada, Kaduna.

Mahukunta kamfanin sun ce babu shakka Shehu Isma’il Umar Almadda, ya zama zakaran gwajin dafi wajen jajircewarsa kan kula da shafin na tsawon shekaru akalla 10, wanda hakan ya sanya suka mika masa takardar jinjina da yabo a kan namijin kokarinsa.

  • Mun Gano Famfo 5,570 Da Ake Amfani Da Su Wajen Satar Danyen Mai — NNPCL
  • Ba Za A Iya Dakatar Da Dunkulewar Kasar Sin Ba

Babban Editan LEADERSHIP Hausa, Abdulrazak Yahuza Jere, ne ya mika takardar yabon a madadin hukumar gudanarwar kamfanin LEADERSHIP.

Mika takardar yabon, ta zo daidai da ranar bude tafsirin watan Ramadana wanda Shehu Isma’il Umar Almadda yake gabatarwa a duk shekara a Zawiyyar Ahlul Faidhati Mai Diwani Group da ke Tudun Wada, cikin Karamar Hukumar Kaduna ta Kudu a Jihar Kaduna a makon da ya gabata.

Da yake jawabi kafin mika takardar, Babban Editan, ya jaddada muhimmancin rubutun da Shehu Isma’il Umar Almadda yake yi na ilmantar da al’umma a bangaren daban-daban da suka shafi addinin Musulunci tare da kuma jajircewarsa wajen tabbatar da cewa a duk Juma’a shafin Dausayin Musulunci yana fita ba tare da fashi ko sau daya ba, don haka ya ce ya ce lallai wannan abin a yaba ne.

Labarai Masu Nasaba

An Gano Gawar Yarinyar da Ruwan Sama Ya Tafi Da ita A Zariya

Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba

“Ba mu taba samun marubuci da ya jima yana ba da gudunmawa a LEADERSHIP Hausa kamar Shehu Isma’ila Umar Almadda ba. Karatuttukan da yake gabatarwa sun samu karbuwa a wurin jama’a bisa irin sakonnin da ake aiko mana a kai. Tun daga kan tarihin Annabi (SAW) da matsayinsa a wurin Allah da dabi’unsa da halayensa, da hukunce-hukuncen ibada da sauran karatuttukan da yake gabatarwa a shafin masu ilmantar ga al’umma sosai da kara wanzar da zaman lafiya. A madadin mahukuntan kamfaninmu, tun daga kan Shugaba, Madam Zainab Nda-Isaiah, da mataimakinta na farko, Azu Ishiekwene, da mataimaki na biyu, Mike Okpere da Manajan Darakta, Mu’azu Elazeh da Darktan Tarurruka, Abraham Nda-Isaiah da dukkan sauran mahukunta da manya da kananan ma’aikatan Kamfanin LEADERSHIP Group Limited, muna godiya.” In ji Abdulrazak.

A nashi bangaren, Shehu Isma’il Umar Almadda ya bayyana gamsuwarsa bisa karramashi da Kamfanin LEADERSHIP ya yi masa. Ya yi alkawarin ci gaba da bayar da gudummawarsa wajen ilmantar da al’umma kan lamuran da suka shafi addinin Musulunci.

Tun da farko, da yake bude tafsirin na bana, Shehu Isma’il Umar Almadda, ya dauki lokaci yana bayani kan sirrorin Alkur’ani mai girma da falalarsa da kuma addu’o’in samun zaman lafiya da kawar da kuncin rayuwa a Nijeriya da dukkan sauran kasashen duniya musamman Falasdin da Isra’ila take muzguna musu.

Malamai daga wurare daban-daban sun samu halartar bude tafsirin shehin na bana.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Bullar Sabuwar Annoba Ta Firgita Al’ummar Nafada A Jihar Gombe

Next Post

Kafa Jam’iyyar Adawa: Atiku Da Wasu Sanatoci Sun Sake Sabon Yunkuri

Related

An Gano Gawar Yarinyar da Ruwan Sama Ya Tafi Da ita A Zariya
Labarai

An Gano Gawar Yarinyar da Ruwan Sama Ya Tafi Da ita A Zariya

6 hours ago
Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba
Manyan Labarai

Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba

7 hours ago
Bayan Fara Kamen Mabarata, An Samu Dalar Amurka, Wuƙa A Kwara
Labarai

Bayan Fara Kamen Mabarata, An Samu Dalar Amurka, Wuƙa A Kwara

9 hours ago
Fadar Shugaban Ƙasa Ta Sanar Da Dalilin Korar Hadimin Shettima Kan Bunƙasa Tattalin Arziƙi
Labarai

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Sanar Da Dalilin Korar Hadimin Shettima Kan Bunƙasa Tattalin Arziƙi

10 hours ago
Shugabanci A Nijeriya: A Ina Ne Gizo Ke Saƙar?
Manyan Labarai

Shugabanci A Nijeriya: A Ina Ne Gizo Ke Saƙar?

10 hours ago
Matashi Ya Rasa Ransa A Yunƙurin Satar Kyabul Ɗin Taransifoma A Maiduguri
Labarai

Matashi Ya Rasa Ransa A Yunƙurin Satar Kyabul Ɗin Taransifoma A Maiduguri

13 hours ago
Next Post
Ya Kamata CBN Ya Sanya Hoton Obasanjo A Jikin Sabbin Kudin Da Za A Sauya Wa Fasali

Kafa Jam’iyyar Adawa: Atiku Da Wasu Sanatoci Sun Sake Sabon Yunkuri

LABARAI MASU NASABA

Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)

Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)

September 14, 2025
Sin Da Amurka Sun Fara Gudanar Da Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Madrid

Sin Da Amurka Sun Fara Gudanar Da Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Madrid

September 14, 2025
An Gano Gawar Yarinyar da Ruwan Sama Ya Tafi Da ita A Zariya

An Gano Gawar Yarinyar da Ruwan Sama Ya Tafi Da ita A Zariya

September 14, 2025
Kano Pillars Ta Samu Nasarar Farko A Gasar Firimiyar Nijeriya Ta Bana

Kano Pillars Ta Samu Nasarar Farko A Gasar Firimiyar Nijeriya Ta Bana

September 14, 2025
Za A Kaddamar Da Fim Mai Taken 731 A Sassan Duniya

Za A Kaddamar Da Fim Mai Taken 731 A Sassan Duniya

September 14, 2025
Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba

Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba

September 14, 2025
Kasar Sin Na Samarwa Duniya Damammaki A Fannin Hada-hadar Ba Da Hidima

Kasar Sin Na Samarwa Duniya Damammaki A Fannin Hada-hadar Ba Da Hidima

September 14, 2025
Duba Ga Kwaɗayi Da Son Duniya A Tsakanin Matan Wannan Zamanin

Duba Ga Kwaɗayi Da Son Duniya A Tsakanin Matan Wannan Zamanin

September 14, 2025
Jagororin Kamfanonin Ketare Sun Nuna Gamsuwa Dangane Da Zuba Jari A Kasar Sin

Jagororin Kamfanonin Ketare Sun Nuna Gamsuwa Dangane Da Zuba Jari A Kasar Sin

September 14, 2025
Bayan Fara Kamen Mabarata, An Samu Dalar Amurka, Wuƙa A Kwara

Bayan Fara Kamen Mabarata, An Samu Dalar Amurka, Wuƙa A Kwara

September 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.