ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

LEADERSHIP Ta Jinjina Wa Shehu Isma’ila Mai Diwani Kan Shafin Dausayin Musulunci

by Shehu Yahaya
2 years ago
LEADERSHIP

Biyo bayan gagarumar gudummawar da yake bayarwa a Jaridar LEADERSHIP Hausa wajen gabatar da darussan addini a shafin Dausayin Musulunci tun daga 2014, Mahukuntan Kamfanin LEADERSHIP sun mika takardar yabo da godiya ga Shehu Isma’il Umar Almadda da aka fi sani da “Mai Diwani”, a zawiyyarsa da ke Tudun Wada, Kaduna.

Mahukunta kamfanin sun ce babu shakka Shehu Isma’il Umar Almadda, ya zama zakaran gwajin dafi wajen jajircewarsa kan kula da shafin na tsawon shekaru akalla 10, wanda hakan ya sanya suka mika masa takardar jinjina da yabo a kan namijin kokarinsa.

  • Mun Gano Famfo 5,570 Da Ake Amfani Da Su Wajen Satar Danyen Mai — NNPCL
  • Ba Za A Iya Dakatar Da Dunkulewar Kasar Sin Ba

Babban Editan LEADERSHIP Hausa, Abdulrazak Yahuza Jere, ne ya mika takardar yabon a madadin hukumar gudanarwar kamfanin LEADERSHIP.

ADVERTISEMENT

Mika takardar yabon, ta zo daidai da ranar bude tafsirin watan Ramadana wanda Shehu Isma’il Umar Almadda yake gabatarwa a duk shekara a Zawiyyar Ahlul Faidhati Mai Diwani Group da ke Tudun Wada, cikin Karamar Hukumar Kaduna ta Kudu a Jihar Kaduna a makon da ya gabata.

Da yake jawabi kafin mika takardar, Babban Editan, ya jaddada muhimmancin rubutun da Shehu Isma’il Umar Almadda yake yi na ilmantar da al’umma a bangaren daban-daban da suka shafi addinin Musulunci tare da kuma jajircewarsa wajen tabbatar da cewa a duk Juma’a shafin Dausayin Musulunci yana fita ba tare da fashi ko sau daya ba, don haka ya ce ya ce lallai wannan abin a yaba ne.

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

“Ba mu taba samun marubuci da ya jima yana ba da gudunmawa a LEADERSHIP Hausa kamar Shehu Isma’ila Umar Almadda ba. Karatuttukan da yake gabatarwa sun samu karbuwa a wurin jama’a bisa irin sakonnin da ake aiko mana a kai. Tun daga kan tarihin Annabi (SAW) da matsayinsa a wurin Allah da dabi’unsa da halayensa, da hukunce-hukuncen ibada da sauran karatuttukan da yake gabatarwa a shafin masu ilmantar ga al’umma sosai da kara wanzar da zaman lafiya. A madadin mahukuntan kamfaninmu, tun daga kan Shugaba, Madam Zainab Nda-Isaiah, da mataimakinta na farko, Azu Ishiekwene, da mataimaki na biyu, Mike Okpere da Manajan Darakta, Mu’azu Elazeh da Darktan Tarurruka, Abraham Nda-Isaiah da dukkan sauran mahukunta da manya da kananan ma’aikatan Kamfanin LEADERSHIP Group Limited, muna godiya.” In ji Abdulrazak.

A nashi bangaren, Shehu Isma’il Umar Almadda ya bayyana gamsuwarsa bisa karramashi da Kamfanin LEADERSHIP ya yi masa. Ya yi alkawarin ci gaba da bayar da gudummawarsa wajen ilmantar da al’umma kan lamuran da suka shafi addinin Musulunci.

Tun da farko, da yake bude tafsirin na bana, Shehu Isma’il Umar Almadda, ya dauki lokaci yana bayani kan sirrorin Alkur’ani mai girma da falalarsa da kuma addu’o’in samun zaman lafiya da kawar da kuncin rayuwa a Nijeriya da dukkan sauran kasashen duniya musamman Falasdin da Isra’ila take muzguna musu.

Malamai daga wurare daban-daban sun samu halartar bude tafsirin shehin na bana.

LEADERSHIP
Shehu Yahaya
+ postsBio
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Majalisar Zartarwa Ta Jihar Kaduna Ta Amince Da Manufofin Haɓaka Walwalar Al’ummar Jihar
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Rashin Tarbiyya Da Ilimin Addini Ne Ke Sa Matasa Ɗaukar Doka a Hannu – Hon. Aminu Adam
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Yadda Ayyukan Titunan Gwamnan Kaduna Suka Farfaɗo Da Ilimi Da Kiwon Lafiya Da Noma A Sabon Gari
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Da Yadda Aka Hallaka Malamar Islamiyya A Kaduna

MASU ALAKA

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
Labarai

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 
Labarai

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Next Post
Ya Kamata CBN Ya Sanya Hoton Obasanjo A Jikin Sabbin Kudin Da Za A Sauya Wa Fasali

Kafa Jam’iyyar Adawa: Atiku Da Wasu Sanatoci Sun Sake Sabon Yunkuri

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.