ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

LEADERSHIP Ta Jinjina Wa Shehu Isma’ila Mai Diwani Kan Shafin Dausayin Musulunci

by Shehu Yahaya
2 years ago
LEADERSHIP

Biyo bayan gagarumar gudummawar da yake bayarwa a Jaridar LEADERSHIP Hausa wajen gabatar da darussan addini a shafin Dausayin Musulunci tun daga 2014, Mahukuntan Kamfanin LEADERSHIP sun mika takardar yabo da godiya ga Shehu Isma’il Umar Almadda da aka fi sani da “Mai Diwani”, a zawiyyarsa da ke Tudun Wada, Kaduna.

Mahukunta kamfanin sun ce babu shakka Shehu Isma’il Umar Almadda, ya zama zakaran gwajin dafi wajen jajircewarsa kan kula da shafin na tsawon shekaru akalla 10, wanda hakan ya sanya suka mika masa takardar jinjina da yabo a kan namijin kokarinsa.

  • Mun Gano Famfo 5,570 Da Ake Amfani Da Su Wajen Satar Danyen Mai — NNPCL
  • Ba Za A Iya Dakatar Da Dunkulewar Kasar Sin Ba

Babban Editan LEADERSHIP Hausa, Abdulrazak Yahuza Jere, ne ya mika takardar yabon a madadin hukumar gudanarwar kamfanin LEADERSHIP.

ADVERTISEMENT

Mika takardar yabon, ta zo daidai da ranar bude tafsirin watan Ramadana wanda Shehu Isma’il Umar Almadda yake gabatarwa a duk shekara a Zawiyyar Ahlul Faidhati Mai Diwani Group da ke Tudun Wada, cikin Karamar Hukumar Kaduna ta Kudu a Jihar Kaduna a makon da ya gabata.

Da yake jawabi kafin mika takardar, Babban Editan, ya jaddada muhimmancin rubutun da Shehu Isma’il Umar Almadda yake yi na ilmantar da al’umma a bangaren daban-daban da suka shafi addinin Musulunci tare da kuma jajircewarsa wajen tabbatar da cewa a duk Juma’a shafin Dausayin Musulunci yana fita ba tare da fashi ko sau daya ba, don haka ya ce ya ce lallai wannan abin a yaba ne.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

“Ba mu taba samun marubuci da ya jima yana ba da gudunmawa a LEADERSHIP Hausa kamar Shehu Isma’ila Umar Almadda ba. Karatuttukan da yake gabatarwa sun samu karbuwa a wurin jama’a bisa irin sakonnin da ake aiko mana a kai. Tun daga kan tarihin Annabi (SAW) da matsayinsa a wurin Allah da dabi’unsa da halayensa, da hukunce-hukuncen ibada da sauran karatuttukan da yake gabatarwa a shafin masu ilmantar ga al’umma sosai da kara wanzar da zaman lafiya. A madadin mahukuntan kamfaninmu, tun daga kan Shugaba, Madam Zainab Nda-Isaiah, da mataimakinta na farko, Azu Ishiekwene, da mataimaki na biyu, Mike Okpere da Manajan Darakta, Mu’azu Elazeh da Darktan Tarurruka, Abraham Nda-Isaiah da dukkan sauran mahukunta da manya da kananan ma’aikatan Kamfanin LEADERSHIP Group Limited, muna godiya.” In ji Abdulrazak.

A nashi bangaren, Shehu Isma’il Umar Almadda ya bayyana gamsuwarsa bisa karramashi da Kamfanin LEADERSHIP ya yi masa. Ya yi alkawarin ci gaba da bayar da gudummawarsa wajen ilmantar da al’umma kan lamuran da suka shafi addinin Musulunci.

Tun da farko, da yake bude tafsirin na bana, Shehu Isma’il Umar Almadda, ya dauki lokaci yana bayani kan sirrorin Alkur’ani mai girma da falalarsa da kuma addu’o’in samun zaman lafiya da kawar da kuncin rayuwa a Nijeriya da dukkan sauran kasashen duniya musamman Falasdin da Isra’ila take muzguna musu.

Malamai daga wurare daban-daban sun samu halartar bude tafsirin shehin na bana.

LEADERSHIP
Shehu Yahaya
+ postsBio
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Bayan Shehu Sani Ya Ƙalubalanci Zailani, Rikicin APC Ya Ƙara Zafi A Kaduna
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Ya Dace ‘Yan Arewa Su Ƙara Marawa Tinubu Baya Domin Kammala Wa’adi Na Biyu — Shehu Sani
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Zargin Ware Ɓangaren El-rufa’i: Rikicin Cikin Gida Ya Kaure A Jam’iyyar ADC, Kaduna

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Next Post
Ya Kamata CBN Ya Sanya Hoton Obasanjo A Jikin Sabbin Kudin Da Za A Sauya Wa Fasali

Kafa Jam’iyyar Adawa: Atiku Da Wasu Sanatoci Sun Sake Sabon Yunkuri

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.