• English
  • Business News
Tuesday, August 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Lokaci Ya Yi Da Za A Samar Da Sabon Tsarin Mulki – Babban Limamin Coci

by Yusuf Shuaibu and Sulaiman
11 months ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Lokaci Ya Yi Da Za A Samar Da Sabon Tsarin Mulki – Babban Limamin Coci
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Limamin cocin ‘Anglican Communion’, Reb Henry Ndukuba, ya yi kira ga gwamnatin tarayya da ta samar da wani sabon kundin tsarin mulkin tarayya wanda zai kasance mai amfani da mutane.

 

Ndukuba ya yi wannan kiran ne a wurin bude taron kwamitin cocin Nijeriya da ya gudana a cocin ‘St. Andrew’s Basilica Anglican Church’ a Jihar Inugu.

  • Rahoto Ya Nuna Yadda Noma Ya Samu Koma-baya A Nijeriya
  • Xi Jinping: Inganta Gina Dunkulewar Kabilun Kasar Sin Baki Daya

Limamin cocin a cikin wata sanarwa da jami’in yada labarai na cocin, Korede Akintunde ya sanya wa hannu, ya ce kowa ya san cewa Nijeriya na fama da matsaloli da dama, wasu daga cikinsu sun bayyana wanda mabambamtan kungiyoyi suka ankarar, musamman ma na zanga-zangar nuna adawa da rashin shugabanci nagari.

 

Labarai Masu Nasaba

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark

Ya bayyana cewa yayin da majalisar dokokin kasar ta yi aiki mai kyau wajen gyaran kundin tsarin mulkin da aka gada daga sojoji, ya kamata a ce Nijeriya ta samu sabbin dokoki a halin yanzu.

“Wannan sabon kundin tsarin mulki zai yi la’akari da abubuwan da aka riga aka bayyana a tarukan kasa da kuma kiraye-kiraye daban-daban na sake fasalin Nijeriya.

 

Nisantar wannna ya sa har yanzu ba gano bakin zaren matsalolin kasar nan ba,” in ji shi.

 

Limamin cocin ya ci gaba da cewa, makama guda daya tilo da gwamnatin Shugaba Bola Tinubu ke bukata ta shimfida shi ne, na tabbatar da mulkin dimokuradiyya da kuma bai wa Nijeriya sabon kundin tsarin mulkin farar hula da ya dace da dimokuradiyya wanda zai magance tushen matsalolin ‘yan kasa.

 

Ya kuma lura da cewa zanga-zangar kyamar rashin shugabanci nagari da aka gudanar duk da rashin jagoranci da manufa ta yi tasiri a wurin gwamnatin tarayya da na jihohi.

“Wannan ya nuna karara cewa jama’a sun gaji da ci gaba da yin alkawurran da gwamnati ta yi na dakile tsadar rayuwa wanda ya haifar da matsananciyar wahala ga magidanta a kasar nan.

“Bugu da kari, kiraye-kirayen da ake yi akai-akai don mahukunta su fahimci halin da ake ciki ko za su sauya salon mulkinsu tare da yin ayyukan da suka makata wajen fitar da al’ummar kasar nan daga kuncin rayuwa.

“Wannan zanga-zangar wani kira ne ga gwamnatoci a dukkan matakai, musamman na tarayya da suka yi kunnen uwar shegu da kukan da jama’a ke yi kan abubuwan da ke ci musu tuwo a karya, domin babu wata gwamnati da za ta iya kafa doka ko hana mutanen da ke fama da yunwa yin zanga-zangar.”

Har ila yau, cocin na Nijeriya ya nuna takaicin yadda wasu masu zanga-zangar suka daga tutocin kasar Rasha a wasu sassan kasar, inda suka bayyana hakan a matsayin abin da ba za a amince da shi ba, domin ya saba ka’idojin zanga-zangar a Nijeriya, kuma da alama ce ta saba wa tsarin mulki na sauyin gwamnati ba bisa ka’ida ba.

“Mun tabbatar da cewa, wannan hadin gambizar da aka yi ba daidai ba ne, zai iya haifar da rugujewar dimokuradiyyarmu, ya kamata a yi cikakken bincike kan lamarin da magance musabbabin wannan aika-aika da kuma masu ta da zaune tsaye.

“Abin takaici, yana iya yiwuwa akwai alaman tambaya kan wannan lamarin, domin da akwai wata makarkashiya, muna kira da a dauki matakin dakile aukuwar lamarin nan gaba,” in ji shi.

Cocin ta kuma jinjina wa Shugaba Tinubu da ma’aikatan Nijeriya kan rattaba hannu a kan sabon mafi karancin albashi na naira 70,000, inda ta ce wannan abin a yaba ne.

“Duk da haka, muna kira ga gwamnati da ta tsawaita shirinta na biyan ‘yan fansho, wadanda da yawa daga cikinsu na rayuwa ne cikin yunwa, akwai bukatar a sake duba kudaden fansho duk bayan shekaru biyar kamar yadda dokar kasa ta tanada.”

Malamin cocin ya tunatar da masu rike da madafun iko cewa ma’aikatan yau su ne ‘yan fansho na gobe, yayin da ya bukaci majalisar dokokin kasar da tabbatar da biyan kudaden fansho ga wadanda suka cancanta a lokacin da ya kamata.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Gwamnatin APCMulkin Dimokuraɗiyyasiyasar Nijeriya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Ya Yi Kira Ga Ma’aikatan Masana’antu Da Su Ba Da Gudummawar Farfado Da Arewa Maso Gabashin Sin

Next Post

Binciken Ra’ayin Jama’a Na CGTN: Al’ummun Duniya Sun Nuna Karin Amincewa Da Kasar Sin

Related

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC
Tambarin Dimokuradiyya

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

4 days ago
An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark
Tambarin Dimokuradiyya

An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark

2 weeks ago
Muhimman Batutuwan Da Za Mu Yi La’akari Da Su Kafin Amincewa Da Bukatun Kirkirar Sabbin Jihohi — Majalisar Dattawa
Tambarin Dimokuradiyya

Muhimman Batutuwan Da Za Mu Yi La’akari Da Su Kafin Amincewa Da Bukatun Kirkirar Sabbin Jihohi — Majalisar Dattawa

2 weeks ago
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

1 month ago
Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 
Tambarin Dimokuradiyya

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

1 month ago
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Masu Neman Takarar Shugaban Kasa A PDP Sun Kara Matsa Kaimi Bayan Ficewar Atiku

1 month ago
Next Post
Binciken Ra’ayin Jama’a Na CGTN: Al’ummun Duniya Sun Nuna Karin Amincewa Da Kasar Sin

Binciken Ra'ayin Jama'a Na CGTN: Al’ummun Duniya Sun Nuna Karin Amincewa Da Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Majalisar Dokokin Rasha

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Majalisar Dokokin Rasha

August 26, 2025
Sin Ta Bukaci Japan Ta Waiwayi Tarihin Kutsen Da Ta Yi

Sin Ta Bukaci Japan Ta Waiwayi Tarihin Kutsen Da Ta Yi

August 26, 2025
Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 128 Daga Hannun ‘Yan Bindiga A Zamfara

Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 128 Daga Hannun ‘Yan Bindiga A Zamfara

August 26, 2025
Xi Da Uwargidansa ​​Sun Gana Da Sarkin Cambodia Da Mahaifiyarsa Sarauniya

Xi Da Uwargidansa ​​Sun Gana Da Sarkin Cambodia Da Mahaifiyarsa Sarauniya

August 26, 2025
Hatsarin Jirgin Kasa: Gwamna Uba Sani Ya Ba Da Umarnin Talllafawa Fasinjojin Da Ke Cikin Jirgin

Hatsarin Jirgin Kasa: Gwamna Uba Sani Ya Ba Da Umarnin Talllafawa Fasinjojin Da Ke Cikin Jirgin

August 26, 2025
Sassou Nguesso: Muna Fatan Gaggauta Tabbatar Da Sakamakon Taron Beijing Na FOCAC

Sassou Nguesso: Muna Fatan Gaggauta Tabbatar Da Sakamakon Taron Beijing Na FOCAC

August 26, 2025
Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harbar Rukunonin Taurarin Dan Adam 10 

Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harbar Rukunonin Taurarin Dan Adam 10 

August 26, 2025
Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba

Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba

August 26, 2025
Saka Zai Yi Jinyar Makonni 4 Sakamakon Rauni Da Ya Samu A Wasan Leeds

Saka Zai Yi Jinyar Makonni 4 Sakamakon Rauni Da Ya Samu A Wasan Leeds

August 26, 2025
‘Yan Kasuwa Na Neman Diyya Bayan Rushe Kasuwar Alaba Rago A Legas

‘Yan Kasuwa Na Neman Diyya Bayan Rushe Kasuwar Alaba Rago A Legas

August 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.