ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Lokaci Ya Yi Da Za A Samar Da Sabon Tsarin Mulki – Babban Limamin Coci

by Yusuf Shuaibu and Sulaiman
2 years ago
Mulki

Limamin cocin ‘Anglican Communion’, Reb Henry Ndukuba, ya yi kira ga gwamnatin tarayya da ta samar da wani sabon kundin tsarin mulkin tarayya wanda zai kasance mai amfani da mutane.

 

Ndukuba ya yi wannan kiran ne a wurin bude taron kwamitin cocin Nijeriya da ya gudana a cocin ‘St. Andrew’s Basilica Anglican Church’ a Jihar Inugu.

ADVERTISEMENT
  • Rahoto Ya Nuna Yadda Noma Ya Samu Koma-baya A Nijeriya
  • Xi Jinping: Inganta Gina Dunkulewar Kabilun Kasar Sin Baki Daya

Limamin cocin a cikin wata sanarwa da jami’in yada labarai na cocin, Korede Akintunde ya sanya wa hannu, ya ce kowa ya san cewa Nijeriya na fama da matsaloli da dama, wasu daga cikinsu sun bayyana wanda mabambamtan kungiyoyi suka ankarar, musamman ma na zanga-zangar nuna adawa da rashin shugabanci nagari.

 

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

Ya bayyana cewa yayin da majalisar dokokin kasar ta yi aiki mai kyau wajen gyaran kundin tsarin mulkin da aka gada daga sojoji, ya kamata a ce Nijeriya ta samu sabbin dokoki a halin yanzu.

“Wannan sabon kundin tsarin mulki zai yi la’akari da abubuwan da aka riga aka bayyana a tarukan kasa da kuma kiraye-kiraye daban-daban na sake fasalin Nijeriya.

 

Nisantar wannna ya sa har yanzu ba gano bakin zaren matsalolin kasar nan ba,” in ji shi.

 

Limamin cocin ya ci gaba da cewa, makama guda daya tilo da gwamnatin Shugaba Bola Tinubu ke bukata ta shimfida shi ne, na tabbatar da mulkin dimokuradiyya da kuma bai wa Nijeriya sabon kundin tsarin mulkin farar hula da ya dace da dimokuradiyya wanda zai magance tushen matsalolin ‘yan kasa.

 

Ya kuma lura da cewa zanga-zangar kyamar rashin shugabanci nagari da aka gudanar duk da rashin jagoranci da manufa ta yi tasiri a wurin gwamnatin tarayya da na jihohi.

“Wannan ya nuna karara cewa jama’a sun gaji da ci gaba da yin alkawurran da gwamnati ta yi na dakile tsadar rayuwa wanda ya haifar da matsananciyar wahala ga magidanta a kasar nan.

“Bugu da kari, kiraye-kirayen da ake yi akai-akai don mahukunta su fahimci halin da ake ciki ko za su sauya salon mulkinsu tare da yin ayyukan da suka makata wajen fitar da al’ummar kasar nan daga kuncin rayuwa.

“Wannan zanga-zangar wani kira ne ga gwamnatoci a dukkan matakai, musamman na tarayya da suka yi kunnen uwar shegu da kukan da jama’a ke yi kan abubuwan da ke ci musu tuwo a karya, domin babu wata gwamnati da za ta iya kafa doka ko hana mutanen da ke fama da yunwa yin zanga-zangar.”

Har ila yau, cocin na Nijeriya ya nuna takaicin yadda wasu masu zanga-zangar suka daga tutocin kasar Rasha a wasu sassan kasar, inda suka bayyana hakan a matsayin abin da ba za a amince da shi ba, domin ya saba ka’idojin zanga-zangar a Nijeriya, kuma da alama ce ta saba wa tsarin mulki na sauyin gwamnati ba bisa ka’ida ba.

“Mun tabbatar da cewa, wannan hadin gambizar da aka yi ba daidai ba ne, zai iya haifar da rugujewar dimokuradiyyarmu, ya kamata a yi cikakken bincike kan lamarin da magance musabbabin wannan aika-aika da kuma masu ta da zaune tsaye.

“Abin takaici, yana iya yiwuwa akwai alaman tambaya kan wannan lamarin, domin da akwai wata makarkashiya, muna kira da a dauki matakin dakile aukuwar lamarin nan gaba,” in ji shi.

Cocin ta kuma jinjina wa Shugaba Tinubu da ma’aikatan Nijeriya kan rattaba hannu a kan sabon mafi karancin albashi na naira 70,000, inda ta ce wannan abin a yaba ne.

“Duk da haka, muna kira ga gwamnati da ta tsawaita shirinta na biyan ‘yan fansho, wadanda da yawa daga cikinsu na rayuwa ne cikin yunwa, akwai bukatar a sake duba kudaden fansho duk bayan shekaru biyar kamar yadda dokar kasa ta tanada.”

Malamin cocin ya tunatar da masu rike da madafun iko cewa ma’aikatan yau su ne ‘yan fansho na gobe, yayin da ya bukaci majalisar dokokin kasar da tabbatar da biyan kudaden fansho ga wadanda suka cancanta a lokacin da ya kamata.

Mulki
Yusuf Shuaibu
+ posts Bio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027
Mulki
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta
  • Sulaiman
    Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
  • Sulaiman
    Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

MASU ALAKA

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan
Manyan Labarai

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

July 11, 2026
Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
Tambarin Dimokuradiyya

Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 11, 2026
Next Post
Binciken Ra’ayin Jama’a Na CGTN: Al’ummun Duniya Sun Nuna Karin Amincewa Da Kasar Sin

Binciken Ra'ayin Jama'a Na CGTN: Al’ummun Duniya Sun Nuna Karin Amincewa Da Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.