ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Lokaci Ya Yi Da Za A Samar Da Sabon Tsarin Mulki – Babban Limamin Coci

by Yusuf Shuaibu and Sulaiman
2 years ago
Mulki

Limamin cocin ‘Anglican Communion’, Reb Henry Ndukuba, ya yi kira ga gwamnatin tarayya da ta samar da wani sabon kundin tsarin mulkin tarayya wanda zai kasance mai amfani da mutane.

 

Ndukuba ya yi wannan kiran ne a wurin bude taron kwamitin cocin Nijeriya da ya gudana a cocin ‘St. Andrew’s Basilica Anglican Church’ a Jihar Inugu.

ADVERTISEMENT
  • Rahoto Ya Nuna Yadda Noma Ya Samu Koma-baya A Nijeriya
  • Xi Jinping: Inganta Gina Dunkulewar Kabilun Kasar Sin Baki Daya

Limamin cocin a cikin wata sanarwa da jami’in yada labarai na cocin, Korede Akintunde ya sanya wa hannu, ya ce kowa ya san cewa Nijeriya na fama da matsaloli da dama, wasu daga cikinsu sun bayyana wanda mabambamtan kungiyoyi suka ankarar, musamman ma na zanga-zangar nuna adawa da rashin shugabanci nagari.

 

LABARAI MASU NASABA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

Ya bayyana cewa yayin da majalisar dokokin kasar ta yi aiki mai kyau wajen gyaran kundin tsarin mulkin da aka gada daga sojoji, ya kamata a ce Nijeriya ta samu sabbin dokoki a halin yanzu.

“Wannan sabon kundin tsarin mulki zai yi la’akari da abubuwan da aka riga aka bayyana a tarukan kasa da kuma kiraye-kiraye daban-daban na sake fasalin Nijeriya.

 

Nisantar wannna ya sa har yanzu ba gano bakin zaren matsalolin kasar nan ba,” in ji shi.

 

Limamin cocin ya ci gaba da cewa, makama guda daya tilo da gwamnatin Shugaba Bola Tinubu ke bukata ta shimfida shi ne, na tabbatar da mulkin dimokuradiyya da kuma bai wa Nijeriya sabon kundin tsarin mulkin farar hula da ya dace da dimokuradiyya wanda zai magance tushen matsalolin ‘yan kasa.

 

Ya kuma lura da cewa zanga-zangar kyamar rashin shugabanci nagari da aka gudanar duk da rashin jagoranci da manufa ta yi tasiri a wurin gwamnatin tarayya da na jihohi.

“Wannan ya nuna karara cewa jama’a sun gaji da ci gaba da yin alkawurran da gwamnati ta yi na dakile tsadar rayuwa wanda ya haifar da matsananciyar wahala ga magidanta a kasar nan.

“Bugu da kari, kiraye-kirayen da ake yi akai-akai don mahukunta su fahimci halin da ake ciki ko za su sauya salon mulkinsu tare da yin ayyukan da suka makata wajen fitar da al’ummar kasar nan daga kuncin rayuwa.

“Wannan zanga-zangar wani kira ne ga gwamnatoci a dukkan matakai, musamman na tarayya da suka yi kunnen uwar shegu da kukan da jama’a ke yi kan abubuwan da ke ci musu tuwo a karya, domin babu wata gwamnati da za ta iya kafa doka ko hana mutanen da ke fama da yunwa yin zanga-zangar.”

Har ila yau, cocin na Nijeriya ya nuna takaicin yadda wasu masu zanga-zangar suka daga tutocin kasar Rasha a wasu sassan kasar, inda suka bayyana hakan a matsayin abin da ba za a amince da shi ba, domin ya saba ka’idojin zanga-zangar a Nijeriya, kuma da alama ce ta saba wa tsarin mulki na sauyin gwamnati ba bisa ka’ida ba.

“Mun tabbatar da cewa, wannan hadin gambizar da aka yi ba daidai ba ne, zai iya haifar da rugujewar dimokuradiyyarmu, ya kamata a yi cikakken bincike kan lamarin da magance musabbabin wannan aika-aika da kuma masu ta da zaune tsaye.

“Abin takaici, yana iya yiwuwa akwai alaman tambaya kan wannan lamarin, domin da akwai wata makarkashiya, muna kira da a dauki matakin dakile aukuwar lamarin nan gaba,” in ji shi.

Cocin ta kuma jinjina wa Shugaba Tinubu da ma’aikatan Nijeriya kan rattaba hannu a kan sabon mafi karancin albashi na naira 70,000, inda ta ce wannan abin a yaba ne.

“Duk da haka, muna kira ga gwamnati da ta tsawaita shirinta na biyan ‘yan fansho, wadanda da yawa daga cikinsu na rayuwa ne cikin yunwa, akwai bukatar a sake duba kudaden fansho duk bayan shekaru biyar kamar yadda dokar kasa ta tanada.”

Malamin cocin ya tunatar da masu rike da madafun iko cewa ma’aikatan yau su ne ‘yan fansho na gobe, yayin da ya bukaci majalisar dokokin kasar da tabbatar da biyan kudaden fansho ga wadanda suka cancanta a lokacin da ya kamata.

Mulki
Yusuf Shuaibu
+ posts Bio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Mulki
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
  • Sulaiman
    Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
  • Sulaiman
    Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

MASU ALAKA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

June 19, 2026
2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Next Post
Binciken Ra’ayin Jama’a Na CGTN: Al’ummun Duniya Sun Nuna Karin Amincewa Da Kasar Sin

Binciken Ra'ayin Jama'a Na CGTN: Al’ummun Duniya Sun Nuna Karin Amincewa Da Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.