• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Lokacin Da Ya Fi Dacewa A Shuka Makani

by Abubakar Abba
1 year ago
in Noma Da Kiwo
0
Makani
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A Nijeriya ana fara shuka Makani ne daga watan Maris zuwa watan Afirilu, wani lokacin kuma daga watan Afirilu zuwa watan Mayu.

 

Tsawon Wane Lokaci A Girbe Shi?  

yadda binciken masana harkokin nomansa ya nuna, Makani na kammala girma ne cikin wata takwas, sannan a daidai wannan lokacin ne ya kamata manomi ya girbe shi.

Idan aka shuka shi a kasar noman da ta dace, ana samun amfani mai dimbin yawa, musamman idan kasar noman ta kasance ta na rike ruwa sosai.

Labarai Masu Nasaba

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani

 

Shin Ana Samun Riba Mai Yawa A Noman Makani A Nijeriya?

Ko shakka babu, ana samun dimbin riba a noman Makani, sannan ribar da ake samu ya danganta da irin kyansa, inda a wani lokaci a kan samu ribar daga Naira 408,608 zuwa Naira 840,000, ko kuma daga Naira 235,592 zuwa Naira 431,392.

Akasari, an fi yin noman Makani a kasar noman da ta bushe; sannan kuma ana gwama nomansa da wasu amfanin gona kamar Masara da waken Soya da kuma Rogo.

Kudaden da ake kashewa wajen nomansa; bai kai wanda ake kashewa a noman Rogo ba.

Yaya Ake Girbin Makani?

Makani na kammala girma ne a watan a takwas, bayan an shuka Irinsa; sannan kuma ana girbe shi ne ta hanyar tugo shi tun daga jijiyarsa ko kuma hako shi daga cikin kasar da aka shuka shi.

 

Matakan Noman Makani Don Samun Riba A Nijeriya:

Ana samun riba mai yawa a noman Makani, don samun riba a Nijeriya, har ila yau Makani cima ne ga ‘yan Nijeriya da dama; ana kuma yin nomansa a Kudancin kasar nan, ba kuma ya yin girman da ake bukata idan zafin rana ya yi masa yawa ko kuma idan akwai karancin ruwa.

 

Tsara Yadda Za A Gudanar Da Nomansa Domin Samun Riba:  

Ana bukatar tsarinka na noman Makani ya kasance ya kunshi dukkanin abubuwan da ka ke so ka gudanar, domin yin nomansa ta yadda za ka samu cin nasara ba tare da wata tangarda ba.

 

Gyaran Gonar Da Za Ka Shuka Shi:

Idan za ka noma shi don samun riba, ya kamata ka samu babbar gona ko ka nemi ta haya ko kuma daga gurin hukumomin harkar noma na gwamnati, misali daga ma’aikatar aikin noma da raya karkara ko kuma daga gurin hukumamin kula da koramu.

Bugu da kari, za ka iya yin gyaran gonar ta hanyoyi biyu, wato ta hanyar gargajiya ko a zamanance.

Har ila yau, za ka iya shuka shi a kowane lokaci a shekara, musamman saboda irin yanayin da ake da shi, amma ya fi yin kyau a kudancin Nijeriya.

 

Lokacin Da Ya Fi Dacewa A Shuka Makani A Kudu Da Yamma Da Gabashin Nijeriya:

A wasu sassa na kasar nan, ana samun ruwan sama mai yawa ana kuma bai wa manomansa shawara ka da su shuka shi a lokacin da ake yin rana sosai, sannan kuma lokacin da ya fi dacewa a shuka shi a kudanci da gabashin kasar nan, shi ne lokacin aka samu matsakaicin ruwan sama.

Ana kuma iya shuka shi a tsakanin watan Mayu zuw watan Afirilu, amma a Arewacin Nijeriya; ana shuka shi a kowane lokaci na damina.

Yadda Ake Samo Irin Makani:

Za a iya sayo Irin Makani a kasuwanin da suke fadin wannan kasa, ana kuma iya samun sa da dama a kasuwannin da ke Jihohin Kuros Riba, Ondo, Enugu, Edo da kuma garuruwan Jos da Abakilike.

Lokacin Da Ya Kamata A Girbe Shi:

Za a iya girbe shi bayan ‘yan watanni, inda manomansa ke tugo shi daga tushensa ko kuma janyo shi daga cikin kasar da aka shuka shi.

Adana Shi Bayan An Girbe Shi:

Za a iya adana shi daga sati hudu zuwa sati shida, musamman ana so yanayin da za adana shi ya kai nauyin ma’aunin yanayi 7°C.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Gyaran gonaNoman shinkafaYadda ake shuka Karas
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Filato Za Ta Horas Da Mata 1000 Kan Sana’o’i Da Fasahar Ƙirƙira Ta Zamani

Next Post

Saudiyya Ta Shirya Karbar Bakuncin Kofin Duniya A 2034

Related

Neja
Noma Da Kiwo

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

3 hours ago
Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani
Noma Da Kiwo

Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani

1 week ago
Gwamnonin Arewa Na Kokarin Farfado Da Hadin Kan Yankin
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Jihar Gombe Ta Rattaba Hannu Kan Yarjejeniya Domin Gina Mayankar Dabbobi

1 week ago
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima
Noma Da Kiwo

Nau’ikan Amfanin Gona Da Ke Saurin Girma Cikin ‘Yan Watanni

1 week ago
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci A Sama Wa Manoma Masu Renon Tsirrai Rancen Kudi

2 weeks ago
Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Zuba Dala Biliyan 74 A Fannin Kiwon Dabbobi
Noma Da Kiwo

Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Zuba Dala Biliyan 74 A Fannin Kiwon Dabbobi

2 weeks ago
Next Post
Kofin Duniya

Saudiyya Ta Shirya Karbar Bakuncin Kofin Duniya A 2034

LABARAI MASU NASABA

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.