• English
  • Business News
Saturday, September 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Machina Ya Yi Barazanar Daukar Matakin Shari’a Kan Sauya Sunansa Da Ahmad Lawan

by Muhammad
3 years ago
in Siyasa
0
Machina Ya Yi Barazanar Daukar Matakin Shari’a Kan Sauya Sunansa Da Ahmad Lawan
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Dan takarar kujerar Sanata a karkashin jam’iyyar APC mai wakiltar Yobe ta Arewa a jihar Yobe, Hon. Bashir Sheriff Machina, ya yi barazanar shigar da kara kan zargin sauya sunansa da na shugaban majalisar dattawa, Ahmad Lawan, a cikin jerin sunayen da jam’iyyar ta aike wa hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) a ranar Juma’a.

Jam’iyyar APC da wasu ‘yan takarar sanata a fadin jihohi 36 na tarayya da babban birnin tarayya (FCT) ne suka sanya sunan Lawan a cikin sunan da aka aike wa hukumar.

  • Lawan Na Fuskantar Barazanar Rasa Kujerarsa Wanda Ya Maye Gurbinsa Ya Ki Janye Masa
  • Abun Mamaki: Lawan ya Manta Da Wasikar Murabus Din Abaribe A Gida

LEADERSHIP ta ruwaito cewa, Machina ya tsaya takara a zaben fidda gwani na jihar Yobe ta Arewa a karkashin jam’iyyar APC a zaben fiida gwani da INEC da hukumomin tsaro suka sanyawa hannu.

Amma Lawan, wanda ya tsaya takarar shugaban kasa a jam’iyyar kuma ya sha kaye a hannun Asiwaju Bola Ahmed Tinubu bai shiga zaben fidda gwani na takarar Sanata na jam’iyyar a yankin Yobe ta Arewa ba.

Sai dai APC ta rubuta wa INEC wasika, inda ta sanar da hukumar zaben cewa shugaban majalisar dattawa ne zai tsaya mata takarar kujerar sanatan Yobe ta Arewa, wadda Lawan ke wakilta a halin yanzu.

Labarai Masu Nasaba

Ba Abin Da Zai Hana Tinubu Sake Lashe Zaɓe A 2027 – Jigon APC

Gwamnan Bauchi Ya Gargaɗi Magoya Bayan Wike A PDP

Machina ya mayar da martani ga wannan matakin na Jam’iyya a daren Juma’a, kuma ya sha alwashin garzaya kotu domin kalubalantar yunkurin kwace masa hakkinsa.

Da yake zantawa da manema labarai a Abuja, Machina ya roki jam’iyyar APC da ta gyara sunansa, inda ya ce ba shi da wani zabi da ya wuce ya nemi a yi masa shari’a idan aka maye gurbinsa da na Lawan.

Machina, ya shan alwashin ba zai ja da baya kan wannan kudurin ba, ya ce, “A cikin jerin sunayen da aka aika wa INEC, an gano ba sunana bane. Ban sani ba ko kuskure ne, sunana ba ya cikin jerin sunayen da aka ce za a gabatar a yau ga INEC. Don ni ne dan takarar da aka zaba na jam’iyyar APC ta shiyyar Yobe ta Arewa a majalisar dattawa.

“Ni ne zababben dan takara; Ban janye wa kowa ba, kuma ba zan janye ba, domin a matsayin hakki na wannan yake, shi ne aikin da ‘yan jam’iyyarmu da wakilai suka ba ni. Don haka cire sunana cikin sirri, rashin bin tsarin demokradiyya ne.

“Insha Allahu zan dauki matakai, na farko ta hanyar tunatarwa da kuma kira ga jam’iyyata cewa idan har da gaske aka yi wannan mataki a gyara, musamman idan aka yi kuskure. A gaskiya muna neman gyara daga kwamitin ayyuka na jam’iyyarmu ta kasa a karkashin jagorancin Sanata Abdullahi Adamu, cewa akwai wata matsala kuma muna bukatar a gyara.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Ahmad lawanAPCMachina
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Za Ta Taimakawa Tanzania Bunkasa Ilimin Sana’o’in Hannu

Next Post

A Bana Ne Sin Ta Samu Sakamako Mai Kyau Wajen Sa Kaimi Ga Yin Hadin Gwiwa A Tsakanin Kasashen BRICS

Related

Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Siyasa

Ba Abin Da Zai Hana Tinubu Sake Lashe Zaɓe A 2027 – Jigon APC

3 days ago
2027: Fastocin Takarar Shugaban Ƙasa Na Gwamnan Bauchi Sun Bayyana
Manyan Labarai

Gwamnan Bauchi Ya Gargaɗi Magoya Bayan Wike A PDP

3 days ago
Ina Da Yaƙinin Tinubu Ne Zai Lashe Zaɓen 2027 — Wike
Siyasa

Ina Da Yaƙinin Tinubu Ne Zai Lashe Zaɓen 2027 — Wike

5 days ago
Ɗaukar Nauyin Ƴan Ta’addan Da Suka Farmake Mu A Kaduna Aka Yi – El-Rufai
Siyasa

Ɗaukar Nauyin Ƴan Ta’addan Da Suka Farmake Mu A Kaduna Aka Yi – El-Rufai

5 days ago
Ɗan Majalisa Zai Saya Wa Makinde Fam Ɗin Takarar Shugaban Ƙasa A 2027
Siyasa

Ɗan Majalisa Zai Saya Wa Makinde Fam Ɗin Takarar Shugaban Ƙasa A 2027

5 days ago
Peter Obi Ya Caccaki Gwamnati Kan Ƙarin Kuɗin Fasfo
Siyasa

Peter Obi Ya Caccaki Gwamnati Kan Ƙarin Kuɗin Fasfo

1 week ago
Next Post
A Bana Ne Sin Ta Samu Sakamako Mai Kyau Wajen Sa Kaimi Ga Yin Hadin Gwiwa A Tsakanin Kasashen BRICS

A Bana Ne Sin Ta Samu Sakamako Mai Kyau Wajen Sa Kaimi Ga Yin Hadin Gwiwa A Tsakanin Kasashen BRICS

LABARAI MASU NASABA

Sashen Cinikayyar Bayar Da Hidima Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni Bakwai Na Farkon Shekarar Bana

Sashen Cinikayyar Bayar Da Hidima Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni Bakwai Na Farkon Shekarar Bana

September 5, 2025
Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Wani Sabon Tauraron Dan Adam

Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Wani Sabon Tauraron Dan Adam

September 5, 2025
Jami’an Kasa Da Kasa Sun Yi Matukar Jinjinawa Jawabin Xi Jinping

Jami’an Kasa Da Kasa Sun Yi Matukar Jinjinawa Jawabin Xi Jinping

September 5, 2025
Za Mu Riƙe Wa Minista Tijjani Muƙaminsa Bayan Hamɓarar Da Tinubu A 2027 – El-Rufai 

Ana Ci Gaba Da Caccakar El-rufai Kan Kalamansa Game Da Tsaron Kasa

September 5, 2025
Kasar Sin Ta Kasance Muhimmin Karfi Dake Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya

Kasar Sin Ta Kasance Muhimmin Karfi Dake Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya

September 5, 2025
Yadda Al’ummar Da Ke Zaune Da ‘Yan Bindiga Ke Rayuwa A Zamfara

Duk Da Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ana Ci Gaba Da Kai Hare-hare Wasu Yankunan Zamfara

September 5, 2025
Antonio Guterres Ya Yi Maraba Da Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

Antonio Guterres Ya Yi Maraba Da Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

September 5, 2025
Ban Yi Kuskure Wajen Zaben Kashim A Matsayin Mataimaki Ba – Tinubu

Ban Yi Kuskure Wajen Zaben Kashim A Matsayin Mataimaki Ba – Tinubu

September 5, 2025
Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Bikin Baje Kolin Masana’antun Kirkirarriyar Basira

Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Bikin Baje Kolin Masana’antun Kirkirarriyar Basira

September 5, 2025
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi

’Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 2 Da Wasu 156 Kan Aikata Laifuka A Jigawa

September 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.