• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mahajjata Sama Da Miliyan 2 Ne Za Su Yi Aikin Hajjin Bana

by Abubakar Abba
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Mahajjata Sama Da Miliyan 2 Ne Za Su Yi Aikin Hajjin Bana
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Mahajjata sama da miliyan biyu daga sassa daban-daban na duniya ne da suka isa masarautar Saudiyya domin gudanar da aikin hajjin bana, sun yi dafifi a filin Arafah domin gudanar da ibada muhimmiya.

Alhazan dai tun daga wayewar garin ranar Talata suka fara tafiya Muna daga Makkah zuwa Arafah, Muzdalifah da komawa Muna, hakan ya nuna an fara aikin Hajjin.

  • Matawalle Bai Saci Kudin Jihar Zamfara Ba — Anas Kaura
  • Za Mu Kawar Da Matsalar Tsaro A Nijeriya -Nuhu Ribadu

Ana sa ran mahajjata za su kasance a filin Arafah a yau, daga bayan Sallar La’asar da La’asar zuwa faduwar rana, suna neman gafarar Allah, Rahma, Albarka, shiriya, aminci, kwanciyar hankali, ci gaba da sauran addu’o’i.

Ana sa ran Malamai za su jagoranci mahajjatan Nijeriya wajen yin addu’o’in samun zaman lafiya, kwanciyar hankali, ci gaba da ci gaban al’ummar Nijeriya da kuma kasar ta shawo kan dukkan kalubalen da ta ke fuskanta ta fuskar tsaro da siyasa da tattalin arziki.

Bayan faduwar rana alhazai za su tashi zuwa Muzdalifah inda ake sa ran za su kwana kafin su koma Muna bayan an idar da sallar Asubah, domin jifan shaidan.

Labarai Masu Nasaba

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

A gefe guda kuwa, Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Nijeriya (NAHCON), ta nuna rashin gamsuwarta kan rashin isassun tantuna ga mahajjatan Nijeriya a Muna da Kamfanin Saudiyya ke da alhakin samarwa da isassun tantuna a Mashã’ir ga ‘yan Nijeriya.

Shugaban Hukumar Alhaji Zikrullah Kunle Hassan wanda ya gabatar da tambayoyi daga manema labarai a Muna kan halin da ake ciki, shi ma bai ji dadin shirin ciyarwar ba, wanda ya ce abincin bai wadatar ba.

Ya ce hukumar ta NAHCON ta yi hasashen cewa wannan matsala ta fi faruwa ne don haka ta ba da shawarar a shiga cikin lamarin, amma hukumomin Saudiyya da abin ya shafa sun dage cewa suna da babban dakin girki, da sanin makamar aiki da kuma wasu tsare-tsare guda uku na daban da za su gamsar da kowa.

Shugaban ya bayyana cewa tuni hukumarsa ta sanar da ma’aikatar aikin Hajji da Umrah ta Saudiyya kan halin da Nijeriya ke ciki dangane da tantuna da ciyarwa, inda ya ce an shirya za su hadu da daddare don duba halin da ake ciki a kasar tare da nemo mafita.

Tuni dai Alhazai suka ci gaba da gabatar da ibada da addu’o’i a filin Arfa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ArfatHajjin 2023MalamaiMusulmiNAHCON
ShareTweetSendShare
Previous Post

Za Mu Kawar Da Matsalar Tsaro A Nijeriya -Nuhu Ribadu

Next Post

Da Buhari Ya Cire Tallafin Mai Da Tinubu Bai Zama Shugaban Kasa Ba —Garba Shehu

Related

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano
Manyan Labarai

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

15 hours ago
Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

1 day ago
Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi
Manyan Labarai

Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi

1 day ago
Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa
Manyan Labarai

Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa

1 day ago
Hukumar kashe gobara
Manyan Labarai

An Samu Asarar Dukiya ta Miliyan ₦273, Tare Da Mutuwar Mutum 5 A Kano – Hukuma

2 days ago
Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 
Manyan Labarai

Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 

2 days ago
Next Post
Da Buhari Ya Cire Tallafin Mai Da Tinubu Bai Zama Shugaban Kasa Ba —Garba Shehu

Da Buhari Ya Cire Tallafin Mai Da Tinubu Bai Zama Shugaban Kasa Ba —Garba Shehu

LABARAI MASU NASABA

Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.