• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mahaukaci Kadai Ne Zai Iya Sake Zaben APC – Ayu

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Mahaukaci Kadai Ne Zai Iya Sake Zaben APC – Ayu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban jam’iyyar PDP na kasa, Dakta Iyorchia Ayu ya bayyana cewa ma-haukaci kadai ne zai iya sake zaben jam’iyyar APC duba da irin bakar wahalar da ‘yan Nijeriya suka shiga na tsawon shekaru takwas na mulkin APC.

Ayu ya bayyana hakan ne a Jihar Benuwai lokacin gangamin yakin neman zaben shugaban kasa na PDP, inda ya bukaci mutane su zabi duka ‘yan takarar jam’iyyarsa.

  • PDP Ta Kori Nnamani, Ogbu, Dan Fayose, Da Wasu Daga Jam’iyyar

Ya ce PDP ta magance matsalar gwamnan Jihar Abiya, Okezie Ikpeazu, sannan suna kokarin lallashin fusatattun gwamnonin PDP guda biyar wadanda suka bijire.

Ya ce wannan shi ne dan takarar shugaban kasa daya tilo na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar wanda ya yi alkawarin idan har aka zabe shi a matsayin shugaban kasa zai dawo da zaman lafiya a wannan jiha da kuma sake bude tashar jirgin kasa da ke jihar.

Haka kuma Ayu ya ce duk da cewa akwai korafe-korafe a cikin babbar jam’iyyar adawa, ya dage da cewa jam’iyyar ba ta rabu ba, yana mai jaddada cewa tuni jam’iyyar ta fara tattaunawa da dukkan ‘ya’yanta da suka fusata domin ganin sun dawo cikin jam’iyyar.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

“Abin da dukkaninmu muka sani shi ne, ana shan wahala a kasar nan a cikin she-karu takwas da APC ta shafe a kan mulki, wanda ke da matsalar tabin hankali ne kwai zai sake zaben APC. Kar ku kuskura ku bata kuri’unku.

“Ku zabi kowane dan takarar PDP, jam’iyyar ba ta rabu ba. Akwai mambobi kali-lan da suka fusata kuma muna magana da su. Za mu tabbatar sun dawo cikin jam’iyyar domin mu yi aiki tare gaba daya. Mako daya ya isa a sauya komi. Dama hakan yana faruwa kuma ina tabbatar da cewa za mu karbi kowa da kowa,” in ji shi.

Ya roki gwamnan Jihar Benuwai, Samuel Ortom ya dawo domin yakin ceto Nijeri-ya daga hannun APC.

Ortom yana daga cikin mambobin gwamnonin PDP na G-5, tawagar fusatattun gwamnonin guda biyar na jam’iyyar wanda gwamnan Jihar Ribas, Nyesom Wike yake jagoranta da ke neman sai Ayu ya sauka daga mukaminsa a matsayin sharad-in yin sulhu.

Sauran mambobin na G5 sun hada da gwamnan Jihar Inugu, Ifeanyi Ugwanyi da gwamnan Jihar Abiya, Okezie Ikpeazu da kuma gwamnan Jihar Oyo, Seyi Makinde.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yan Bindiga Sun Bude Wa Tawagar Jami’an Tsaron Okowa Wuta Sun Kashe ‘Yansanda Uku

Next Post

Ba Mu Da Takardun Kuɗi Da Zamu Buga Sababbin Kuɗi Isassu Su Wadata – Emefiele

Related

Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

22 hours ago
‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

1 week ago
Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

2 weeks ago
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Adawa Na Cacakar APC A Yankin Arewa Maso Yamma Bisa Goyon Bayan Tazarcen Tinubu

2 weeks ago
Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027

1 month ago
Ayu
Tambarin Dimokuradiyya

Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

1 month ago
Next Post
Ba Mu Da Takardun Kuɗi Da Zamu Buga Sababbin Kuɗi Isassu Su Wadata – Emefiele

Ba Mu Da Takardun Kuɗi Da Zamu Buga Sababbin Kuɗi Isassu Su Wadata – Emefiele

LABARAI MASU NASABA

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.