ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba Mu Da Takardun Kuɗi Da Zamu Buga Sababbin Kuɗi Isassu Su Wadata – Emefiele

by Muhammad
4 years ago
Emefiele

Gwaman Babban Bankin Nijeriya Godwin Emefiele ya ce CBN ba shi da isassun takardun da zai ishe su buga sababbin kuɗin da ake buƙata a ƙasar.

BBC Hausa ta ce, Mista Emefiele ya bayyana hakan ne a ranar Juma’a a lokacin da yake gabatar da jawabi ga taron majalisar magabata ta ƙasar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasar, kamar yadda wata majiya ta shaida wa Jaridar PREMIUM TIMES a ƙasar.

  • Sabon Shugaban NLC Ya Yi Barazanar Tsunduma Yajin Aiki Kan Karancin Man Fetur Da Sauyin Kudi
  • Sauyin Kudi: Tinubu Ya Jinjinawa Gwamnonin Nijeriya Kan Hukuncin Kotun Koli

Gwamnan Babban Bankin ya shaida wa majalisar magabatan cewa hukumar da ke lura da buga takardun kuɗin ƙasar ba ta da isassun takardun buga sababbin kuɗin, abin da ya sa aka kasa buga wadatattun takardun kuɗi da aka sabunta a ƙasar.

ADVERTISEMENT

“Hukumar ba ta da takardun da za ta buga 500 da 1,000. Amma sun yi odar takardar daga ƙasashen Jamus da Birtaniya, to sai dai har yanzu layi bai zo kansu ba kasancewar akwai layi a odar, dan haka odarsu ba za ta samu yanzu ba”, in ji Emefiele.

Ya ƙara da cewa “CBN ya buƙaci hukumar da ke buga kuɗin da ta buga kofin takardu miliyan 70, abin da zai isa a buga naira biliyan 126 da za a sake su, su zagaya hannun mutane a wannan rana ta Juma’a, to amma hukumar ba ta da isassun takardun da za ta yi wannan aiki”. Kamar yadda majiyar ta shaida wa jaridar PREMIUM TIMES.

LABARAI MASU NASABA

Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

A makon da ya gabata ne dai shugaban ƙasar Muhammadu Buhari ya alƙawarta cewa za a shawo kan matsalar cikin kwana bakwai.

Tuni dai wasu jihohin ƙasar sun shigar da ƙarar gwamnatin tarayya da Babban Bankin domin ƙara wa’adin amfani da tsofaffin takardun kuɗin ƙasar.

Lamarin da ya sa Kotun Ƙolin ƙasar ta yanke hukuncin ci gaba da amfani da tsoffin takardun kuɗin har zuwa ranar 15 ga watan Fabrairun da muke ciki, lokacin da za ta yanke hukunci kan lamarin.

Emefiele
Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu
  • Muhammad
    Yadda Na Tsira Daga Cutar Mashaƙo A Katsina: “Na Fara Da Tsartuwar Jini Tare Da Yawu”
  • Muhammad
    An Naɗa Yusuf Nasidi Nasir A Matsayin Talban Barayan Kano
  • Muhammad
    Wani Kamfani Ya Tallafa Wa Masu Sana’ar Shayi A Kano

MASU ALAKA

Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki
Labarai

Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

September 10, 2026
Emefiele
Labarai

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

September 10, 2026
Emefiele
Labarai

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026
Next Post
Bashin Dala Miliyan 350 Da Kaduna Ta Ciyo: Nasara Ko Akasinta?

Bashin Dala Miliyan 350 Da Kaduna Ta Ciyo: Nasara Ko Akasinta?

LABARAI MASU NASABA

Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

September 10, 2026
Emefiele

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

September 10, 2026
Emefiele

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026
Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.