• English
  • Business News
Friday, July 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mai Keta Hakkin Bil Adam Na Ikirarin Kare Shi

by CGTN Hausa and Sulaiman
9 months ago
in Ra'ayi Riga
0
Mai Keta Hakkin Bil Adam Na Ikirarin Kare Shi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwanan baya, kwamiti na 3 na babban taron MDD karo na 79, ya kira taron muhawara a hedkwatarsa, inda Amurka, da Austriliya da dai wasu kasashe ‘yan tsiraru suka soki kasar Sin kan batun hakkin Bil Adama ba gaira ba dalili.

 

Shin ko wane ne yake da ikon bayyana halin da ake ciki game da wannan batu? Ba shakka jama’a ne da kan su. Sinawa da yawansu ya kai biliyan 1.4 sun fita daga kangin talauci, har ma sun samu wadata tare, suna more rayuwarsu, suna zama cikin kwanciyar hankali, wannan shi ne hakikanin ci gaba a fannin kare hakkin Bil Adam.

  • Musabbabin Lalacewar Lantarki A Jihohin Arewa -TCN
  • Rikita-rikitar Aikin Hanyar Abuja Zuwa Kaduna…

A wani bangaren na daban, bari mu duba Amurka da Austriliya. Amurka ta dade tana fama da matsalar nuna bambancin launin fata, kana yawan mutanen da suka mutu sakamakon harin bindiga a kasar ya kai kimanin dubu 43 a shekarar 2023 kadai. A sa’i daya kuma, a kalla mutane 1,247 sun mutu a kasar, sakamakon nuna karfin tuwo da ‘yan sanda suke yi. A Austriliya fa? kowa ya san cewa kasar ta samu ci gabanta ne ta hanyar cin zarafin mutane ‘yan asalin wurin da aka kafa kasar.

 

Labarai Masu Nasaba

Manufar Raya Biranen Kasar Sin: Ba Wai Kawai a Tabbatar Da “Tsayi” Ba Ne Har Ma Da “Zafi”

Girman Kai Da Son Zuciya Ba Za Su Sa A Amince Ko Ba Da Hadin Kai Ba

Wadannan kasashe ba su kula da rayuka, da zaman rayuwar jama’arsu ba, balle na al’ummun sauran kasashe. Yanzu haka, a zirin Gaza, fararen hula fiye da dubu 40 sun mutu, miliyoyin mata da kananan yara na fama da yunwa da rashin muhallin zama. Ba shakka, wannan wuri na matukar bukatar kare hakkin al’ummun sa. Amma, jami’i mai kula da harkokin jin kai a zirin Gaza na kasar Amurka, ya yi ikirarin cewa, gwamnatin Amurka ba za ta daina samarwa Isra’ila makamai ba, duk da cewa matakan da ta dauka a Gaza sun sabawa dokar kasa da kasa.

 

Marigayi masani Publius Cornelius Tacitus, wanda ya mutu a shekaru 2000 da suka gabata, ya taba bayyana cewa, “An nunawa mutane baraguzan gine-gine sun ce wannan shi ne zaman lafiya”, yanzu wasu kasashen yamma suna kokarin ta da rikici a wasu wurare, inda mutane ke fama da asarar rayuka da dimbin wahalhalu, amma sun mai da kansu masu koyar da mutanen duniya dabarar kare hakkin Bil Adam, gami da shafawa kasar Sin bakin fenti, duk da iyakacin kokarin da kasar ke yi a fannin kare hakkin da ikon jama’arta.

 

Sai dai wadannan kasashen ba za su iya mai da fari baki ba. Ko da yake sun dade suna kokarin dora laifi kan kasar Sin, kan batun hakkin Bil Adam, amma yawancin kasashe ba su taba yarda da maganarsu ba.

 

Tabbas, zamani na yin shisshigi cikin harkokin gidan sauran kasashe bisa hujjar kare hakkin Bil Adama ya kai karshensa. (Mai zane da rubutu: MINA)

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Wang Yi, Ya Yi Karin Haske Game Da Halartar Taron BRICS Karo 16 Da Shugaba Xi Ya Yi

Next Post

Gwamnatin Tarayya Da Google Sun Bullo Da Hanyar Samar Wa Da Matasa 2,500 Aikin Dogaro Da Kai

Related

Manufar Raya Biranen Kasar Sin: Ba Wai Kawai a Tabbatar Da “Tsayi” Ba Ne Har Ma Da “Zafi”
Ra'ayi Riga

Manufar Raya Biranen Kasar Sin: Ba Wai Kawai a Tabbatar Da “Tsayi” Ba Ne Har Ma Da “Zafi”

15 hours ago
Girman Kai Da Son Zuciya Ba Za Su Sa A Amince Ko Ba Da Hadin Kai Ba
Ra'ayi Riga

Girman Kai Da Son Zuciya Ba Za Su Sa A Amince Ko Ba Da Hadin Kai Ba

3 days ago
“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai
Ra'ayi Riga

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

7 days ago
Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin

1 week ago
Rawar Ganin Da BRICS Ke Takawa Wajen Samar Wa Kasashe Masu Tasowa ‘Yanci A Tsarin Gudanar Da Harkokin Kasa Da Kasa
Ra'ayi Riga

Rawar Ganin Da BRICS Ke Takawa Wajen Samar Wa Kasashe Masu Tasowa ‘Yanci A Tsarin Gudanar Da Harkokin Kasa Da Kasa

1 week ago
Kayayyakin Sin Na Kara Samun Karbuwa A Kasuwar Duniya
Ra'ayi Riga

Kayayyakin Sin Na Kara Samun Karbuwa A Kasuwar Duniya

2 weeks ago
Next Post
Gwamnatin Tarayya Da Google Sun Bullo Da Hanyar Samar Wa Da Matasa 2,500 Aikin Dogaro Da Kai

Gwamnatin Tarayya Da Google Sun Bullo Da Hanyar Samar Wa Da Matasa 2,500 Aikin Dogaro Da Kai

LABARAI MASU NASABA

Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

Manyan Jami’an ‘Yansanda 150 Ke Fuskantar Kwamitin Ladabtarwa

July 18, 2025
Peng Liyuan Ta Halarci Bikin Hada Hannun Matasa Da Yaran Sin Da Amurka Na Shekarar 2025

Peng Liyuan Ta Halarci Bikin Hada Hannun Matasa Da Yaran Sin Da Amurka Na Shekarar 2025

July 18, 2025
Buhari 1942 – 2025: Rayuwarsa, Rasuwarsa, Jana’izarsa, Da Ci gaba Da Ta’aziyya

Buhari 1942 – 2025: Rayuwarsa, Rasuwarsa, Jana’izarsa, Da Ci gaba Da Ta’aziyya

July 18, 2025
Raya Hulda Tsakanin Sin Da Australia Ya Dace Da Yanayin Zamanin Da Ake Ciki

Raya Hulda Tsakanin Sin Da Australia Ya Dace Da Yanayin Zamanin Da Ake Ciki

July 17, 2025
Shugaba Tinubu Zai Ziyarci Kano Don Ta’aziyyar Ɗantata

Shugaba Tinubu Zai Ziyarci Kano Don Ta’aziyyar Ɗantata

July 17, 2025
Gudummawar Sin Ga Tattaunawa Tsakanin Mabanbantan Wayewar Kai Da Dunkulewar Duniya

Gudummawar Sin Ga Tattaunawa Tsakanin Mabanbantan Wayewar Kai Da Dunkulewar Duniya

July 17, 2025
Natasha Ta Rubuta Wa Majalisa, Tana Neman A Yi Biyayya Ga Umarnin Kotu

Natasha Ta Rubuta Wa Majalisa, Tana Neman A Yi Biyayya Ga Umarnin Kotu

July 17, 2025
Binciken Jin Ra’ayoyin Jama’a Na CGTN: Rahoton Matsayar Japan Kan Tsaro Na Takala Na Nuna Hatsari Mai Girma Game Da Tsaro

Binciken Jin Ra’ayoyin Jama’a Na CGTN: Rahoton Matsayar Japan Kan Tsaro Na Takala Na Nuna Hatsari Mai Girma Game Da Tsaro

July 17, 2025
Direban Da Ya Murƙushe Furen Gwamnati A Kano Ya Shiga Hannu

Direban Da Ya Murƙushe Furen Gwamnati A Kano Ya Shiga Hannu

July 17, 2025
Ma’aikatar Harkokin Waje: Kasar Sin Ta Kasance Mai Fafutukar Inganta Ci Gaban Duniya A Koyaushe

Ma’aikatar Harkokin Waje: Kasar Sin Ta Kasance Mai Fafutukar Inganta Ci Gaban Duniya A Koyaushe

July 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.