• English
  • Business News
Sunday, July 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Majalisa Ba Ta Amince Da Sayo Sabon Jirgin Shugaban Ƙasa Ba’

by Abubakar Sulaiman
11 months ago
in Manyan Labarai
0
‘Majalisa Ba Ta Amince Da Sayo Sabon Jirgin Shugaban Ƙasa Ba’
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An sami rahotannin cewa gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ta sayi sabon jirgin shugaban ƙasa ba tare da amincewar Majalisar Ƙasa ba. A cewar binciken jaridar Daily Trust, an sayi sabon jirgin Airbus A330 daga wani babban bankin Jamus bayan da aka kwace shi daga wani Yariman ƙasar Larabawa da ya kasa biyan bashinsa.

Majalisar ƙasa bata tabbatar da samun wata buƙata daga fadar shugaban ƙasa dangane da sayan jirgin ba, inda shugaban majalisar dattawa, Godswill Akpabio, ya bayyana a baya cewa ba a gabatar da irin wannan buƙatar ba. Sai dai ya ce idan har an gabatar da buƙatar, za a yi nazari a kanta idan tana da alaƙa da tsaron ƙasa da jin daɗin al’ummar Nijeriya.

  • Manoma Sun Nemi Tinubu Ya Kara Yawan Tallafin Noma 
  • Shugaba Tinubu Ya Amince A Sake Gina Gadar Wagga Da Ta Rushe

Wani saɓani ya ƙara bayyana lokacin da wata kotun Faransa ta umarci a kwace jirage uku na Nijeriya yayin wata taƙaddama ta doka tsakanin wani kamfanin Sin da gwamnatin jihar Ogun. An ce kamfanin Sin ɗin ya saki jirgin Airbus A330 domin bai wa Shugaba Tinubu damar halartar taro da Shugaban ƙasar Faransa Emmanuel Macron.

Majalisa

Ko da yake babu wani bayani na cikakken yadda aka sayi jirgin, wasu majiyoyi sun ce za a iya sayen shi ne da kuɗin umarnin kai tsaye daga fadar shugaban ƙasa wanda ba lallai sai an nemi izinin majalisa ba.

Labarai Masu Nasaba

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson

Ƴan majalisar Dattijai da ta Wakilai sun bayyana mamaki kan wannan cefane, suna masu cewa ba a sanar da su komai game da yarjejeniyar ba. Amma majiyoyin gwamnati sun yi nuni da cewa lamarin na iya kasancewa cikin tanade-tanaden kasafin kuɗin da ba a bayyana su ba.

Lokacin da aka tuntubi wakilan fadar shugaban ƙasa da ma’aikatar tsaro, ba su bayar da wata amsa ba. Ofishin mai ba da shawara kan tsaro na ƙasa shi ma ya bayyana cewa ba su da masaniya game da cikakkun bayanai na sayen jirgin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan Majalisar WakilaiJirgiTinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Shugaba Tinubu Ya Amince A Sake Gina Gadar Wagga Da Ta Rushe

Next Post

Gwamnati Za Ta Hukunta Jami’o’in Da Suka Gaza Miƙa Sunayen Ɗalibansu Kan Lokaci

Related

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 
Wasanni

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

15 hours ago
Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson
Siyasa

Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson

20 hours ago
An Kama Mutane 4 Da Ake Zargi Da Haƙar Ma’adanai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja
Manyan Labarai

An Kama Mutane 4 Da Ake Zargi Da Haƙar Ma’adanai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

21 hours ago
Gwamnatin Kano Ta Gabatar Da Buƙatu 10 A Gaban Kwamitin Gyaran Tsarin Mulkin Nijeriya
Da ɗumi-ɗuminsa

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincikar Kwamishinan Sufuri Kan Karɓar Belin Dilan Ƙwaya A Kano

1 day ago
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

Dangote Ya Ajiye Muƙamin Shugabancin Kamfaninsa Na Siminti

2 days ago
Ganawar Tinubu Da Kwankwaso Alkairi Ce – Mataimakin Shugaban FUDMA
Manyan Labarai

Tinubu Na Yi Wa Arewa Manyan Ayyuka – Martanin Fadar Shugaban Ƙasa Ga Kwankwaso 

2 days ago
Next Post
Gwamnati Za Ta Hukunta Jami’o’in Da Suka Gaza Miƙa Sunayen Ɗalibansu Kan Lokaci

Gwamnati Za Ta Hukunta Jami'o'in Da Suka Gaza Miƙa Sunayen Ɗalibansu Kan Lokaci

LABARAI MASU NASABA

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

July 27, 2025
Super Falcons Za Su Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

Super Falcons Za Su Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

July 27, 2025
ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

July 27, 2025
Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

July 27, 2025
Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

July 27, 2025
aure

Ko Kin San… Matsalolin Mahaifa Da Suke Hana Haihuwa 

July 27, 2025
VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

July 27, 2025
Yadda Ake Faten Acca

Yadda Ake Faten Acca

July 27, 2025
Hanyoyin Gyaran Gashi

Hanyoyin Gyaran Gashi

July 27, 2025
Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

July 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.