ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Majalisa Ba Ta Amince Da Sayo Sabon Jirgin Shugaban Ƙasa Ba’

by Abubakar Sulaiman
2 years ago
Majalisa

An sami rahotannin cewa gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ta sayi sabon jirgin shugaban ƙasa ba tare da amincewar Majalisar Ƙasa ba. A cewar binciken jaridar Daily Trust, an sayi sabon jirgin Airbus A330 daga wani babban bankin Jamus bayan da aka kwace shi daga wani Yariman ƙasar Larabawa da ya kasa biyan bashinsa.

Majalisar ƙasa bata tabbatar da samun wata buƙata daga fadar shugaban ƙasa dangane da sayan jirgin ba, inda shugaban majalisar dattawa, Godswill Akpabio, ya bayyana a baya cewa ba a gabatar da irin wannan buƙatar ba. Sai dai ya ce idan har an gabatar da buƙatar, za a yi nazari a kanta idan tana da alaƙa da tsaron ƙasa da jin daɗin al’ummar Nijeriya.

  • Manoma Sun Nemi Tinubu Ya Kara Yawan Tallafin Noma 
  • Shugaba Tinubu Ya Amince A Sake Gina Gadar Wagga Da Ta Rushe

Wani saɓani ya ƙara bayyana lokacin da wata kotun Faransa ta umarci a kwace jirage uku na Nijeriya yayin wata taƙaddama ta doka tsakanin wani kamfanin Sin da gwamnatin jihar Ogun. An ce kamfanin Sin ɗin ya saki jirgin Airbus A330 domin bai wa Shugaba Tinubu damar halartar taro da Shugaban ƙasar Faransa Emmanuel Macron.

ADVERTISEMENT

Majalisa

Ko da yake babu wani bayani na cikakken yadda aka sayi jirgin, wasu majiyoyi sun ce za a iya sayen shi ne da kuɗin umarnin kai tsaye daga fadar shugaban ƙasa wanda ba lallai sai an nemi izinin majalisa ba.

LABARAI MASU NASABA

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

Ƴan majalisar Dattijai da ta Wakilai sun bayyana mamaki kan wannan cefane, suna masu cewa ba a sanar da su komai game da yarjejeniyar ba. Amma majiyoyin gwamnati sun yi nuni da cewa lamarin na iya kasancewa cikin tanade-tanaden kasafin kuɗin da ba a bayyana su ba.

Lokacin da aka tuntubi wakilan fadar shugaban ƙasa da ma’aikatar tsaro, ba su bayar da wata amsa ba. Ofishin mai ba da shawara kan tsaro na ƙasa shi ma ya bayyana cewa ba su da masaniya game da cikakkun bayanai na sayen jirgin.

Majalisa
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya
  • Abubakar Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Za Ta Ƙaddamar Da Tsarin Daƙile Rugujewar Gine-Gine
  • Abubakar Sulaiman
    Kotu Ta Hana INEC Amincewa Da Tarukan ADC Ƙarƙashin Jagorancin David Mark
  • Abubakar Sulaiman
    Mahara Sun Kashe Mutane 9 Ƴan Gida Ɗaya, Har Da Jariri Ɗan Wata 2 A Filato

MASU ALAKA

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu
Manyan Labarai

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai
Siyasa

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

July 16, 2026
M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin  Mataimakinsa
Manyan Labarai

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

July 16, 2026
Next Post
Gwamnati Za Ta Hukunta Jami’o’in Da Suka Gaza Miƙa Sunayen Ɗalibansu Kan Lokaci

Gwamnati Za Ta Hukunta Jami'o'in Da Suka Gaza Miƙa Sunayen Ɗalibansu Kan Lokaci

LABARAI MASU NASABA

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

July 16, 2026
Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 16, 2026
Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

July 16, 2026
Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

July 16, 2026
Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

July 16, 2026
Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

July 16, 2026
Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

July 16, 2026
Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

July 16, 2026
Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026
An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

July 16, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.