• English
  • Business News
Wednesday, October 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Majalisa Za Ta Gayyaci Emefiele Kan Bashin Tiriliyan 30 Da Buhari Ya Karba

by Sadiq
2 years ago
Emefiele

Majalisar Dattawa, za ta gayyaci tsohon gwamnan babban bankin (CBN), Godwin Emefiele domin amsa wasu tambayoyi game da bashin naira tiriliyan 30 da gwamnatin tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari ta karba.

Majalisar dai za ta bukaci Emefiele ya yi mata bayani a kan wani bashin Naira tiriliyan 30 da ya bai wa gwamnatin tarayya a zamanin tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari.

  • Gwamnatin Tarayya Ta Gano Mutane 9, ‘Yan Canjin Kudi 6 Masu Tallafawa Ta’addanci A Nijeriya 
  • CIYARWA [Falalarta Da Muhimmancinta] Na 1

Shugaban kwamitin kula da huldar kudi tsakanin gwamnatin tarayya da CBN, Sanata Jibrin Isah ne, ya bayyana hakan jim kadan bayan zaman kwamitin da wakilan CBN a ranar Talata.

Isa, ya ce alamu na nuna cewa Emefiele ya zartar da wadansu hukunce-hukunce da a ka’ida bai kamata ya yi su kai tsaye ba.

Ya ce akwai bukatar ya tuntubi mambobin kwamitinsa, mataimakinsa da kuma masu ruwa da tsaki a lamarin.

LABARAI MASU NASABA

Da Ɗumi-ɗumi: Hauhawar Farashin Kayayyaki A Nijeriya Ya Ƙara Raguwa Zuwa Kashi 18.02%

2027: Babu Ɗan Siyasar Da Zai Iya Ƙalubalantar Tinubu — Fadar Shugaban Ƙasa

Tuni dai majalisar ta kaddamar da wani kwarya-kwaryar kwamiti na musamman domin binciken yadda aka bayar da bashin da yadda aka kashe kudin da aka ranta.

Har wa yau, kwamitin da Sanata Jibrin Isah zai jagoranta zai binciki yadda aka bayar da bashin ‘Anchor Borrowers’ a zamanin gwamnatin Buhari.

Sanatan ya ce, “Mun duba kundin ‘ancho borrowers’ a gaban zauren majalisa, mun ga abubbuwa da yawa a cikinsa, mun dubi wadanda suka amfana da basukan.

“Wannan zai taimaka mana wajen gano gaskiyar abin da ya wakana a CBN a zamanin Emefiele.

“Babban abin da ya sa dole mu gayyaci tsohon gwamnan bankin shi ne wakilan CBN din da suka zo sun gaza amsa tambayoyin da mu ka yi musu, wanna shi ne zai tabbatar da cewa ba su da cikakken sanin abubuwan da suka wakana dangane da wadannan kudi da aka ranta wa gwamnatin tarayya.”

“Lallai idan shugabannin bankin na wannan lokacin suka gaza kawo mana bayanan da muke bukata, to ya zama wajibi mu gayyaci Emefielle ya gurfana a gabanmu domin fada mana yadda aka yi.”

Dangane da bashin manoma na ‘Anchor Borrowers’ kuwa, Isa cewa ya yi, “kawo yanzu an dawo da kaso 70, sauran kaso 30 din na wurin kananan manoma.

“Babban hatsarin da ke tattare da bai wa kananan manoma bashi, shi ne gaskiya ba su da wata dama ta kere sa’a, ko kuma kai wa ga tudun mun tsira, sakamakon yadda abubuwa suke.”

Shugaban kwamitin ya bayyana cewa “kananan manoma ba su da kwarewar aikin noma na zamani, kuma ba su da kayan aiki, wannan matsala ce da idan aka yi wasa za ta hana mu samun abin da muke so.

Kwamitin majalisar ya bayyana cewa kudin da ke hannun kananan manoma yakai Naira Biliyan 358, amma inda ake sa ran samun sauki shi ne, an raba wannan rance ne ta hannun bankunan ‘yan kasuwa, don haka yanzu su za su san yadda za su yi su karbo kudin gwamnati.

CBN dai ya bai wa Gwamnatin Buhari rancen kudi kan tsaron da ake yi wa lakabi da “ways and means” a turance domin cike gibin kasafin kudi.

A yanzu haka dai Emefiele na tsare a hannun DSS, inda ya ke fuskantar tuhume-tuhume da suka hada da mallakar makamai ba bisa ka’ida ba, da cin amanar kasa da sauransu a kotu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

sallah
Manyan Labarai

Da Ɗumi-ɗumi: Hauhawar Farashin Kayayyaki A Nijeriya Ya Ƙara Raguwa Zuwa Kashi 18.02%

October 15, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Manyan Labarai

2027: Babu Ɗan Siyasar Da Zai Iya Ƙalubalantar Tinubu — Fadar Shugaban Ƙasa

October 15, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Hana Manoma Girbi A Zamfara, Al’umma Na Neman Taimako

October 15, 2025
Next Post
sin

Sin Ta Harba Tauraron Dan Adam Na Queqiao-2

LABARAI MASU NASABA

Da Ɗumi-ɗumi: Ladan Bosso Ya Ajiye Aikin Horar Da Barau Fc 

Da Ɗumi-ɗumi: Ladan Bosso Ya Ajiye Aikin Horar Da Barau Fc 

October 15, 2025
An Bude Bikin Baje Kolin Kasuwanci Na Kasa Da Kasa Na 138 A Guangzhou

An Bude Bikin Baje Kolin Kasuwanci Na Kasa Da Kasa Na 138 A Guangzhou

October 15, 2025
sallah

Da Ɗumi-ɗumi: Hauhawar Farashin Kayayyaki A Nijeriya Ya Ƙara Raguwa Zuwa Kashi 18.02%

October 15, 2025
Mujallar “Qiushi” Za Ta Wallafa Muhimmiyar Kasidar Shugaba Xi Jinping Kan Muhimman Shawarwari Hudu Da Ya Gabatar

Mujallar “Qiushi” Za Ta Wallafa Muhimmiyar Kasidar Shugaba Xi Jinping Kan Muhimman Shawarwari Hudu Da Ya Gabatar

October 15, 2025
Sojoji Sun Fatattaki ‘Yan Ta’adda A Dajin Taraba

Sojoji Sun Fatattaki ‘Yan Ta’adda A Dajin Taraba

October 15, 2025
Xi Jinping Ya Taya Patrick Herminie Murnar Lashe Zaben Shugaban Kasar Seychelles

Xi Jinping Ya Taya Patrick Herminie Murnar Lashe Zaben Shugaban Kasar Seychelles

October 15, 2025
Yajin Aikin: Ɗalibai Sun Bai Wa ASUU Da Gwamnatin Tarayya Wa’adin Kwana 7 Su Warware Rikicinsu

Yajin Aikin: Ɗalibai Sun Bai Wa ASUU Da Gwamnatin Tarayya Wa’adin Kwana 7 Su Warware Rikicinsu

October 15, 2025
Gwamna Diri Da ’Yan Majalisa 23 Na Bayelsa Sun Fice Daga PDP

Gwamna Diri Da ’Yan Majalisa 23 Na Bayelsa Sun Fice Daga PDP

October 15, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

2027: Babu Ɗan Siyasar Da Zai Iya Ƙalubalantar Tinubu — Fadar Shugaban Ƙasa

October 15, 2025
Tinubu Ya Nemi Jihohi Su Dakatar Da Karbar Haraji A Kan Masu Safarar Kayan Abinci

Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba Barazana Ce Ga Tsaro A Yammacin Afirka – Tinubu

October 15, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.