• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Majalisa Za Ta Gayyaci Emefiele Kan Bashin Tiriliyan 30 Da Buhari Ya Karba

by Sadiq
1 year ago
in Manyan Labarai
0
Majalisa Za Ta Gayyaci Emefiele Kan Bashin Tiriliyan 30 Da Buhari Ya Karba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Majalisar Dattawa, za ta gayyaci tsohon gwamnan babban bankin (CBN), Godwin Emefiele domin amsa wasu tambayoyi game da bashin naira tiriliyan 30 da gwamnatin tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari ta karba.

Majalisar dai za ta bukaci Emefiele ya yi mata bayani a kan wani bashin Naira tiriliyan 30 da ya bai wa gwamnatin tarayya a zamanin tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari.

  • Gwamnatin Tarayya Ta Gano Mutane 9, ‘Yan Canjin Kudi 6 Masu Tallafawa Ta’addanci A Nijeriya 
  • CIYARWA [Falalarta Da Muhimmancinta] Na 1

Shugaban kwamitin kula da huldar kudi tsakanin gwamnatin tarayya da CBN, Sanata Jibrin Isah ne, ya bayyana hakan jim kadan bayan zaman kwamitin da wakilan CBN a ranar Talata.

Isa, ya ce alamu na nuna cewa Emefiele ya zartar da wadansu hukunce-hukunce da a ka’ida bai kamata ya yi su kai tsaye ba.

Ya ce akwai bukatar ya tuntubi mambobin kwamitinsa, mataimakinsa da kuma masu ruwa da tsaki a lamarin.

Labarai Masu Nasaba

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

Tuni dai majalisar ta kaddamar da wani kwarya-kwaryar kwamiti na musamman domin binciken yadda aka bayar da bashin da yadda aka kashe kudin da aka ranta.

Har wa yau, kwamitin da Sanata Jibrin Isah zai jagoranta zai binciki yadda aka bayar da bashin ‘Anchor Borrowers’ a zamanin gwamnatin Buhari.

Sanatan ya ce, “Mun duba kundin ‘ancho borrowers’ a gaban zauren majalisa, mun ga abubbuwa da yawa a cikinsa, mun dubi wadanda suka amfana da basukan.

“Wannan zai taimaka mana wajen gano gaskiyar abin da ya wakana a CBN a zamanin Emefiele.

“Babban abin da ya sa dole mu gayyaci tsohon gwamnan bankin shi ne wakilan CBN din da suka zo sun gaza amsa tambayoyin da mu ka yi musu, wanna shi ne zai tabbatar da cewa ba su da cikakken sanin abubuwan da suka wakana dangane da wadannan kudi da aka ranta wa gwamnatin tarayya.”

“Lallai idan shugabannin bankin na wannan lokacin suka gaza kawo mana bayanan da muke bukata, to ya zama wajibi mu gayyaci Emefielle ya gurfana a gabanmu domin fada mana yadda aka yi.”

Dangane da bashin manoma na ‘Anchor Borrowers’ kuwa, Isa cewa ya yi, “kawo yanzu an dawo da kaso 70, sauran kaso 30 din na wurin kananan manoma.

“Babban hatsarin da ke tattare da bai wa kananan manoma bashi, shi ne gaskiya ba su da wata dama ta kere sa’a, ko kuma kai wa ga tudun mun tsira, sakamakon yadda abubuwa suke.”

Shugaban kwamitin ya bayyana cewa “kananan manoma ba su da kwarewar aikin noma na zamani, kuma ba su da kayan aiki, wannan matsala ce da idan aka yi wasa za ta hana mu samun abin da muke so.

Kwamitin majalisar ya bayyana cewa kudin da ke hannun kananan manoma yakai Naira Biliyan 358, amma inda ake sa ran samun sauki shi ne, an raba wannan rance ne ta hannun bankunan ‘yan kasuwa, don haka yanzu su za su san yadda za su yi su karbo kudin gwamnati.

CBN dai ya bai wa Gwamnatin Buhari rancen kudi kan tsaron da ake yi wa lakabi da “ways and means” a turance domin cike gibin kasafin kudi.

A yanzu haka dai Emefiele na tsare a hannun DSS, inda ya ke fuskantar tuhume-tuhume da suka hada da mallakar makamai ba bisa ka’ida ba, da cin amanar kasa da sauransu a kotu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BashiBuhariEmefielemajalisaManomaRancen Anchor Borrower
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Tarayya Ta Gano Mutane 9, ‘Yan Canjin Kudi 6 Masu Tallafawa Ta’addanci A Nijeriya 

Next Post

Sin Ta Harba Tauraron Dan Adam Na Queqiao-2

Related

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta
Manyan Labarai

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

43 minutes ago
Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

5 hours ago
An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa
Manyan Labarai

An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa

5 hours ago
Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta
Manyan Labarai

Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

6 hours ago
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina
Manyan Labarai

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

9 hours ago
Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido
Manyan Labarai

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

1 day ago
Next Post
sin

Sin Ta Harba Tauraron Dan Adam Na Queqiao-2

LABARAI MASU NASABA

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

September 13, 2025
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

September 13, 2025
Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

September 13, 2025
Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

September 13, 2025
Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

September 13, 2025
Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

September 13, 2025
Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

September 13, 2025
An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa

An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa

September 13, 2025
Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

September 13, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.