• English
  • Business News
Monday, September 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Majalisa Za Ta Gayyaci Emefiele Kan Bashin Tiriliyan 30 Da Buhari Ya Karba

by Sadiq
1 year ago
in Manyan Labarai
0
Majalisa Za Ta Gayyaci Emefiele Kan Bashin Tiriliyan 30 Da Buhari Ya Karba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Majalisar Dattawa, za ta gayyaci tsohon gwamnan babban bankin (CBN), Godwin Emefiele domin amsa wasu tambayoyi game da bashin naira tiriliyan 30 da gwamnatin tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari ta karba.

Majalisar dai za ta bukaci Emefiele ya yi mata bayani a kan wani bashin Naira tiriliyan 30 da ya bai wa gwamnatin tarayya a zamanin tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari.

  • Gwamnatin Tarayya Ta Gano Mutane 9, ‘Yan Canjin Kudi 6 Masu Tallafawa Ta’addanci A Nijeriya 
  • CIYARWA [Falalarta Da Muhimmancinta] Na 1

Shugaban kwamitin kula da huldar kudi tsakanin gwamnatin tarayya da CBN, Sanata Jibrin Isah ne, ya bayyana hakan jim kadan bayan zaman kwamitin da wakilan CBN a ranar Talata.

Isa, ya ce alamu na nuna cewa Emefiele ya zartar da wadansu hukunce-hukunce da a ka’ida bai kamata ya yi su kai tsaye ba.

Ya ce akwai bukatar ya tuntubi mambobin kwamitinsa, mataimakinsa da kuma masu ruwa da tsaki a lamarin.

Labarai Masu Nasaba

KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano

Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba

Tuni dai majalisar ta kaddamar da wani kwarya-kwaryar kwamiti na musamman domin binciken yadda aka bayar da bashin da yadda aka kashe kudin da aka ranta.

Har wa yau, kwamitin da Sanata Jibrin Isah zai jagoranta zai binciki yadda aka bayar da bashin ‘Anchor Borrowers’ a zamanin gwamnatin Buhari.

Sanatan ya ce, “Mun duba kundin ‘ancho borrowers’ a gaban zauren majalisa, mun ga abubbuwa da yawa a cikinsa, mun dubi wadanda suka amfana da basukan.

“Wannan zai taimaka mana wajen gano gaskiyar abin da ya wakana a CBN a zamanin Emefiele.

“Babban abin da ya sa dole mu gayyaci tsohon gwamnan bankin shi ne wakilan CBN din da suka zo sun gaza amsa tambayoyin da mu ka yi musu, wanna shi ne zai tabbatar da cewa ba su da cikakken sanin abubuwan da suka wakana dangane da wadannan kudi da aka ranta wa gwamnatin tarayya.”

“Lallai idan shugabannin bankin na wannan lokacin suka gaza kawo mana bayanan da muke bukata, to ya zama wajibi mu gayyaci Emefielle ya gurfana a gabanmu domin fada mana yadda aka yi.”

Dangane da bashin manoma na ‘Anchor Borrowers’ kuwa, Isa cewa ya yi, “kawo yanzu an dawo da kaso 70, sauran kaso 30 din na wurin kananan manoma.

“Babban hatsarin da ke tattare da bai wa kananan manoma bashi, shi ne gaskiya ba su da wata dama ta kere sa’a, ko kuma kai wa ga tudun mun tsira, sakamakon yadda abubuwa suke.”

Shugaban kwamitin ya bayyana cewa “kananan manoma ba su da kwarewar aikin noma na zamani, kuma ba su da kayan aiki, wannan matsala ce da idan aka yi wasa za ta hana mu samun abin da muke so.

Kwamitin majalisar ya bayyana cewa kudin da ke hannun kananan manoma yakai Naira Biliyan 358, amma inda ake sa ran samun sauki shi ne, an raba wannan rance ne ta hannun bankunan ‘yan kasuwa, don haka yanzu su za su san yadda za su yi su karbo kudin gwamnati.

CBN dai ya bai wa Gwamnatin Buhari rancen kudi kan tsaron da ake yi wa lakabi da “ways and means” a turance domin cike gibin kasafin kudi.

A yanzu haka dai Emefiele na tsare a hannun DSS, inda ya ke fuskantar tuhume-tuhume da suka hada da mallakar makamai ba bisa ka’ida ba, da cin amanar kasa da sauransu a kotu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BashiBuhariEmefielemajalisaManomaRancen Anchor Borrower
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Tarayya Ta Gano Mutane 9, ‘Yan Canjin Kudi 6 Masu Tallafawa Ta’addanci A Nijeriya 

Next Post

Sin Ta Harba Tauraron Dan Adam Na Queqiao-2

Related

KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano
Manyan Labarai

KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano

2 hours ago
Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba
Manyan Labarai

Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba

15 hours ago
Shugabanci A Nijeriya: A Ina Ne Gizo Ke Saƙar?
Manyan Labarai

Shugabanci A Nijeriya: A Ina Ne Gizo Ke Saƙar?

19 hours ago
Sojojin Nijeriya Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 139, Sun Cafke 132 A Cikin Sati 2 —Hedikwatar Tsaro
Manyan Labarai

Sojoji Sun Ceto Mutane 30 Da Aka Yi Garkuwa Da Su, Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Dama

23 hours ago
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina
Manyan Labarai

Dawowa Hutu Ya Tayar Da Hankalin Iyaye Saboda Ƙarin Kuɗin Makaranta

1 day ago
Likitoci
Manyan Labarai

NARD Ta Janye Yajin Aikin Gargaɗi Da Ta Fara

1 day ago
Next Post
sin

Sin Ta Harba Tauraron Dan Adam Na Queqiao-2

LABARAI MASU NASABA

Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago

Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago

September 15, 2025
KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano

KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano

September 15, 2025
Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Fasinjoji 17 A Zamfara

Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Fasinjoji 17 A Zamfara

September 15, 2025
Barcelona Ta Farfaɗo Zuwa Matsayi Na Biyu Bayan Lallasa Valencia A Johan Cruyff

Barcelona Ta Farfaɗo Zuwa Matsayi Na Biyu Bayan Lallasa Valencia A Johan Cruyff

September 15, 2025
Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)

Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)

September 14, 2025
Sin Da Amurka Sun Fara Gudanar Da Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Madrid

Sin Da Amurka Sun Fara Gudanar Da Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Madrid

September 14, 2025
An Gano Gawar Yarinyar da Ruwan Sama Ya Tafi Da ita A Zariya

An Gano Gawar Yarinyar da Ruwan Sama Ya Tafi Da ita A Zariya

September 14, 2025
Kano Pillars Ta Samu Nasarar Farko A Gasar Firimiyar Nijeriya Ta Bana

Kano Pillars Ta Samu Nasarar Farko A Gasar Firimiyar Nijeriya Ta Bana

September 14, 2025
Za A Kaddamar Da Fim Mai Taken 731 A Sassan Duniya

Za A Kaddamar Da Fim Mai Taken 731 A Sassan Duniya

September 14, 2025
Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba

Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba

September 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.