ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Majalisa Za Ta Gayyaci Emefiele Kan Bashin Tiriliyan 30 Da Buhari Ya Karba

by Sadiq
2 years ago
Emefiele

Majalisar Dattawa, za ta gayyaci tsohon gwamnan babban bankin (CBN), Godwin Emefiele domin amsa wasu tambayoyi game da bashin naira tiriliyan 30 da gwamnatin tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari ta karba.

Majalisar dai za ta bukaci Emefiele ya yi mata bayani a kan wani bashin Naira tiriliyan 30 da ya bai wa gwamnatin tarayya a zamanin tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari.

  • Gwamnatin Tarayya Ta Gano Mutane 9, ‘Yan Canjin Kudi 6 Masu Tallafawa Ta’addanci A Nijeriya 
  • CIYARWA [Falalarta Da Muhimmancinta] Na 1

Shugaban kwamitin kula da huldar kudi tsakanin gwamnatin tarayya da CBN, Sanata Jibrin Isah ne, ya bayyana hakan jim kadan bayan zaman kwamitin da wakilan CBN a ranar Talata.

ADVERTISEMENT

Isa, ya ce alamu na nuna cewa Emefiele ya zartar da wadansu hukunce-hukunce da a ka’ida bai kamata ya yi su kai tsaye ba.

Ya ce akwai bukatar ya tuntubi mambobin kwamitinsa, mataimakinsa da kuma masu ruwa da tsaki a lamarin.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tuni dai majalisar ta kaddamar da wani kwarya-kwaryar kwamiti na musamman domin binciken yadda aka bayar da bashin da yadda aka kashe kudin da aka ranta.

Har wa yau, kwamitin da Sanata Jibrin Isah zai jagoranta zai binciki yadda aka bayar da bashin ‘Anchor Borrowers’ a zamanin gwamnatin Buhari.

Sanatan ya ce, “Mun duba kundin ‘ancho borrowers’ a gaban zauren majalisa, mun ga abubbuwa da yawa a cikinsa, mun dubi wadanda suka amfana da basukan.

“Wannan zai taimaka mana wajen gano gaskiyar abin da ya wakana a CBN a zamanin Emefiele.

“Babban abin da ya sa dole mu gayyaci tsohon gwamnan bankin shi ne wakilan CBN din da suka zo sun gaza amsa tambayoyin da mu ka yi musu, wanna shi ne zai tabbatar da cewa ba su da cikakken sanin abubuwan da suka wakana dangane da wadannan kudi da aka ranta wa gwamnatin tarayya.”

“Lallai idan shugabannin bankin na wannan lokacin suka gaza kawo mana bayanan da muke bukata, to ya zama wajibi mu gayyaci Emefielle ya gurfana a gabanmu domin fada mana yadda aka yi.”

Dangane da bashin manoma na ‘Anchor Borrowers’ kuwa, Isa cewa ya yi, “kawo yanzu an dawo da kaso 70, sauran kaso 30 din na wurin kananan manoma.

“Babban hatsarin da ke tattare da bai wa kananan manoma bashi, shi ne gaskiya ba su da wata dama ta kere sa’a, ko kuma kai wa ga tudun mun tsira, sakamakon yadda abubuwa suke.”

Shugaban kwamitin ya bayyana cewa “kananan manoma ba su da kwarewar aikin noma na zamani, kuma ba su da kayan aiki, wannan matsala ce da idan aka yi wasa za ta hana mu samun abin da muke so.

Kwamitin majalisar ya bayyana cewa kudin da ke hannun kananan manoma yakai Naira Biliyan 358, amma inda ake sa ran samun sauki shi ne, an raba wannan rance ne ta hannun bankunan ‘yan kasuwa, don haka yanzu su za su san yadda za su yi su karbo kudin gwamnati.

CBN dai ya bai wa Gwamnatin Buhari rancen kudi kan tsaron da ake yi wa lakabi da “ways and means” a turance domin cike gibin kasafin kudi.

A yanzu haka dai Emefiele na tsare a hannun DSS, inda ya ke fuskantar tuhume-tuhume da suka hada da mallakar makamai ba bisa ka’ida ba, da cin amanar kasa da sauransu a kotu.

MASU ALAKA

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya
Manyan Labarai

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Next Post
sin

Sin Ta Harba Tauraron Dan Adam Na Queqiao-2

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.