• English
  • Business News
Saturday, July 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Majalisar Dattawa Ta Amince Da Kudirin Gaggauta Aikin Makarantar Kwastam A Bauchi

by Bashir Bello, Abuja
2 years ago
in Labarai
0
Majalisar Dattawa Ta Amince Da Kudirin Gaggauta Aikin Makarantar Kwastam A Bauchi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Majalisar Dattawa ta umarci Gwamnatin Tarayya ta gaggauta kammala gina Makaratar Horas da Jami’an Hana Fasakwauri ta Kasa wato Kwastom da ke Jihar Bauchi don inganta samar da jami’ai kwararru da za su kawo gyara da ci gaba a kasar nan.

Majalisar ta bayar da wannan umarni ne ran Alhamis a lokacin da Sanata Mai Wakiltar Bauchi ta Kudu, Sanata Buba Umar Shehu ya gabatar da bukata ta musamman a gaban Majalisar.

Sanata Buba ya ce dalilin gabatar da wannan kuduri shi ne ya lura cewa an saka ginin wannan makaranta a cikin kasafin Kudi na shekara ta 2023 in da za a kashe kimanin kudi sama da Naira Biliyan 14 amma har ya zuwa yanzu shekara ta raba ba a yi komai akan gina makarantar ba.

  • An Nada Janar Tchiani Shugaban Rikon Kwarya A Nijar

Ya ce gina wannan makaranta zai kawo gagaramin ci gaba ga kasa baki daya ta hanyar samar da horo ga jami’an Hana Fasa Kwauri wanda zai yi sanadiyar kawo ci gaba ta fannin samar da kudin shiga da kwarewa da kawar da barna a gurare da dama a kasar nan.

Kudurin nasa wanda ya sami goyan bayan dukkanin Sanatocin Majalisar in da suka bayar da gudunmawa wajen ganin an ja hankalin gwamnatin Tarayya ta gaggauta ganin an samar da makarantar don amfanar ‘Yan Nijeriya.

Labarai Masu Nasaba

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

Biyan ‘Yan Fansho Naira Biliyan 22: NUP Da NLC Sun Bukaci A Yi Koyi Da Gwamna Abba

Sanata Buba ya ce yana da kwarin gwiwa cewa Shugaban Kasa Bola Ahmad Tinubu zai bayar da umarni ba tare da bata lokaci ba wajen ganin an kammala makarantar sabo da muhimmancin ta ga kasa ta fannin tsaro da samar da kudaden shiga.

A wani bangaren kuma, Sanata Buba ya sha alwashin ganin an samar da ingantaccen tsaro a kasar nan ta hanyar tattaunawa da jami’an tsaro a kai a kai a matsayin sa na shugaban Kwamitin da aka kafa a Majalisar akan fannin Tsaro.

Ya ce tsaro shi ne ginshikin duk wani ci gaba sabo da haka ne ba zai yi kasa a gwiwa ba wajen ganin an samar da ingantaccen tsaro a kasarnan.

A hirarsa da ‘Yan Jaridu a ofishinsa, Sanata Buba ya yi kira da ‘Yan Nijeriya da su ba wa Jami’an tsaro hadin kai wajen ganin an samar da tsaro mai inganci a kasarnan. In da ya kara da cewa hakki ne da ya dogara a kan kowa tun da ba wanda zai magance mana barazanar tsaro a kasar nan sai mu da kammu mun hada gwiwa da jami’an tsaro.

A bangaren Ministoci da aka gabatar da sunayensu ranar Alhamis, ya yaba wa kokarin Shugaban Kasa na ganin ya gabatar da sunayen kamar yadda kundin tsarin mulki ya bukata.

Daga karshe dan majalisar ya yi kira da ‘Yan Nijeriya musamman wadanda ba a fadi sunayen Ministoci da ke Jihohin su ba da su kara hakuri cewa shugaban kasa ya yi alkawari gabatar da sauran sunayen watakila kafin a gama tantance sunayen wadanda aka gabatar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan NijeriyaKwastammajalisa
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Nada Janar Tchiani Shugaban Rikon Kwarya A Nijar

Next Post

Shugaba Xi Ya Sanar Da Bude Gasar Wasannin Motsa Jiki Ta Daliban Jami’o’in Kasa Da Kasa A Lokacin Zafi Karo Na 31 A Chengdu

Related

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya
Labarai

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

7 hours ago
Biyan Tukuici: Gwamna Yusuf Ya Ƙaddamar Da Tallafin Naira 50,000 Ga Mata 5,200 Duk Wata A Kano
Labarai

Biyan ‘Yan Fansho Naira Biliyan 22: NUP Da NLC Sun Bukaci A Yi Koyi Da Gwamna Abba

7 hours ago
Kasar Sin Ta Nuna Alhinin Rasuwar Tsohon Shugaban Nijeriya Buhari
Labarai

Za A Dinga Tunawa Da Buhari A Matsayin Waliyyi A Siyasar Nijeriya —Dakta Zangina

8 hours ago
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Manyan Labarai

Tinubu Ya Nada Ɗan Babangida A Matsayin Shugaban Bankin Manoma

9 hours ago
‘Yan Kasuwa Na Shirin Yi Wa Dangote Zanga-zanga Kan Rage Farashin Gas
Labarai

‘Yan Kasuwa Na Shirin Yi Wa Dangote Zanga-zanga Kan Rage Farashin Gas

9 hours ago
Lai Ching-Te Bai Cancanci Zama Jagoran Yankin Taiwan Ba
Ra'ayi Riga

Lai Ching-Te Bai Cancanci Zama Jagoran Yankin Taiwan Ba

10 hours ago
Next Post
Shugaba Xi Ya Sanar Da Bude Gasar Wasannin Motsa Jiki Ta Daliban Jami’o’in Kasa Da Kasa A Lokacin Zafi Karo Na 31 A Chengdu

Shugaba Xi Ya Sanar Da Bude Gasar Wasannin Motsa Jiki Ta Daliban Jami’o’in Kasa Da Kasa A Lokacin Zafi Karo Na 31 A Chengdu

LABARAI MASU NASABA

Dangote

Dalilin Da Ya Sa Dangote Ya Jinjina Wa Hukumar NPA

July 18, 2025
Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

July 18, 2025
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

July 18, 2025
Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

July 18, 2025
majalisar kasa

Kirkirar Sabbin Jihohi Da Kananan Hukumomi Sun Dabaibaye Sauraron Jin Ra’ayoyin Gyaran Tsarin Mulki

July 18, 2025
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

July 18, 2025
Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

July 18, 2025
A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

July 18, 2025
Biyan Tukuici: Gwamna Yusuf Ya Ƙaddamar Da Tallafin Naira 50,000 Ga Mata 5,200 Duk Wata A Kano

Biyan ‘Yan Fansho Naira Biliyan 22: NUP Da NLC Sun Bukaci A Yi Koyi Da Gwamna Abba

July 18, 2025
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

July 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.