• English
  • Business News
Friday, July 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Majalisar Dattawa Ta Amince Da Kudirin Gaggauta Aikin Makarantar Kwastam A Bauchi

by Bashir Bello, Abuja
2 years ago
in Labarai
0
Majalisar Dattawa Ta Amince Da Kudirin Gaggauta Aikin Makarantar Kwastam A Bauchi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Majalisar Dattawa ta umarci Gwamnatin Tarayya ta gaggauta kammala gina Makaratar Horas da Jami’an Hana Fasakwauri ta Kasa wato Kwastom da ke Jihar Bauchi don inganta samar da jami’ai kwararru da za su kawo gyara da ci gaba a kasar nan.

Majalisar ta bayar da wannan umarni ne ran Alhamis a lokacin da Sanata Mai Wakiltar Bauchi ta Kudu, Sanata Buba Umar Shehu ya gabatar da bukata ta musamman a gaban Majalisar.

Sanata Buba ya ce dalilin gabatar da wannan kuduri shi ne ya lura cewa an saka ginin wannan makaranta a cikin kasafin Kudi na shekara ta 2023 in da za a kashe kimanin kudi sama da Naira Biliyan 14 amma har ya zuwa yanzu shekara ta raba ba a yi komai akan gina makarantar ba.

  • An Nada Janar Tchiani Shugaban Rikon Kwarya A Nijar

Ya ce gina wannan makaranta zai kawo gagaramin ci gaba ga kasa baki daya ta hanyar samar da horo ga jami’an Hana Fasa Kwauri wanda zai yi sanadiyar kawo ci gaba ta fannin samar da kudin shiga da kwarewa da kawar da barna a gurare da dama a kasar nan.

Kudurin nasa wanda ya sami goyan bayan dukkanin Sanatocin Majalisar in da suka bayar da gudunmawa wajen ganin an ja hankalin gwamnatin Tarayya ta gaggauta ganin an samar da makarantar don amfanar ‘Yan Nijeriya.

Labarai Masu Nasaba

Akwai Bukatar Hada Kai Da Aiki Tare Tsakanin Hukumomin Tsaro

Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

Sanata Buba ya ce yana da kwarin gwiwa cewa Shugaban Kasa Bola Ahmad Tinubu zai bayar da umarni ba tare da bata lokaci ba wajen ganin an kammala makarantar sabo da muhimmancin ta ga kasa ta fannin tsaro da samar da kudaden shiga.

A wani bangaren kuma, Sanata Buba ya sha alwashin ganin an samar da ingantaccen tsaro a kasar nan ta hanyar tattaunawa da jami’an tsaro a kai a kai a matsayin sa na shugaban Kwamitin da aka kafa a Majalisar akan fannin Tsaro.

Ya ce tsaro shi ne ginshikin duk wani ci gaba sabo da haka ne ba zai yi kasa a gwiwa ba wajen ganin an samar da ingantaccen tsaro a kasarnan.

A hirarsa da ‘Yan Jaridu a ofishinsa, Sanata Buba ya yi kira da ‘Yan Nijeriya da su ba wa Jami’an tsaro hadin kai wajen ganin an samar da tsaro mai inganci a kasarnan. In da ya kara da cewa hakki ne da ya dogara a kan kowa tun da ba wanda zai magance mana barazanar tsaro a kasar nan sai mu da kammu mun hada gwiwa da jami’an tsaro.

A bangaren Ministoci da aka gabatar da sunayensu ranar Alhamis, ya yaba wa kokarin Shugaban Kasa na ganin ya gabatar da sunayen kamar yadda kundin tsarin mulki ya bukata.

Daga karshe dan majalisar ya yi kira da ‘Yan Nijeriya musamman wadanda ba a fadi sunayen Ministoci da ke Jihohin su ba da su kara hakuri cewa shugaban kasa ya yi alkawari gabatar da sauran sunayen watakila kafin a gama tantance sunayen wadanda aka gabatar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan NijeriyaKwastammajalisa
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Nada Janar Tchiani Shugaban Rikon Kwarya A Nijar

Next Post

Shugaba Xi Ya Sanar Da Bude Gasar Wasannin Motsa Jiki Ta Daliban Jami’o’in Kasa Da Kasa A Lokacin Zafi Karo Na 31 A Chengdu

Related

Yunkurin Magance Matsalar Tsaro Da Rigingimu A Arewa…
Manyan Labarai

Akwai Bukatar Hada Kai Da Aiki Tare Tsakanin Hukumomin Tsaro

11 minutes ago
Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

10 hours ago
An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano
Labarai

An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

11 hours ago
Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta
Labarai

Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

13 hours ago
Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin

13 hours ago
EFCC Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Ɓullar Sabbin Hanyoyin Damfarar Kuɗi
Labarai

EFCC Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Ɓullar Sabbin Hanyoyin Damfarar Kuɗi

14 hours ago
Next Post
Shugaba Xi Ya Sanar Da Bude Gasar Wasannin Motsa Jiki Ta Daliban Jami’o’in Kasa Da Kasa A Lokacin Zafi Karo Na 31 A Chengdu

Shugaba Xi Ya Sanar Da Bude Gasar Wasannin Motsa Jiki Ta Daliban Jami’o’in Kasa Da Kasa A Lokacin Zafi Karo Na 31 A Chengdu

LABARAI MASU NASABA

Yunkurin Magance Matsalar Tsaro Da Rigingimu A Arewa…

Akwai Bukatar Hada Kai Da Aiki Tare Tsakanin Hukumomin Tsaro

July 11, 2025
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

July 10, 2025
Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

July 10, 2025
Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

July 10, 2025
Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

July 10, 2025
Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

July 10, 2025
An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

July 10, 2025
Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam

Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam

July 10, 2025
Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

July 10, 2025
An Bude Taron Ministoci Kan Wayewar Kai A Birnin Beijing

An Bude Taron Ministoci Kan Wayewar Kai A Birnin Beijing

July 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.