• Leadership Hausa
Thursday, November 30, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Majalisar Dattawa Ta Amince Da Kudirin Gaggauta Aikin Makarantar Kwastam A Bauchi

by Bashir Bello, Abuja
4 months ago
in Labarai
0
Majalisar Dattawa Ta Amince Da Kudirin Gaggauta Aikin Makarantar Kwastam A Bauchi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Majalisar Dattawa ta umarci Gwamnatin Tarayya ta gaggauta kammala gina Makaratar Horas da Jami’an Hana Fasakwauri ta Kasa wato Kwastom da ke Jihar Bauchi don inganta samar da jami’ai kwararru da za su kawo gyara da ci gaba a kasar nan.

Majalisar ta bayar da wannan umarni ne ran Alhamis a lokacin da Sanata Mai Wakiltar Bauchi ta Kudu, Sanata Buba Umar Shehu ya gabatar da bukata ta musamman a gaban Majalisar.

Sanata Buba ya ce dalilin gabatar da wannan kuduri shi ne ya lura cewa an saka ginin wannan makaranta a cikin kasafin Kudi na shekara ta 2023 in da za a kashe kimanin kudi sama da Naira Biliyan 14 amma har ya zuwa yanzu shekara ta raba ba a yi komai akan gina makarantar ba.

  • An Nada Janar Tchiani Shugaban Rikon Kwarya A Nijar

Ya ce gina wannan makaranta zai kawo gagaramin ci gaba ga kasa baki daya ta hanyar samar da horo ga jami’an Hana Fasa Kwauri wanda zai yi sanadiyar kawo ci gaba ta fannin samar da kudin shiga da kwarewa da kawar da barna a gurare da dama a kasar nan.

Kudurin nasa wanda ya sami goyan bayan dukkanin Sanatocin Majalisar in da suka bayar da gudunmawa wajen ganin an ja hankalin gwamnatin Tarayya ta gaggauta ganin an samar da makarantar don amfanar ‘Yan Nijeriya.

Labarai Masu Nasaba

NNPP Ta Nemi EU, Amurka Da AU Su Kawo Mata Dauki Kan Zaben Gwamnan Kano

Sanatocin Arewacin Nijeriya Sun Matsa Wa Tinubu Lamba Kan Sake Bude Iyakar Nijar

Sanata Buba ya ce yana da kwarin gwiwa cewa Shugaban Kasa Bola Ahmad Tinubu zai bayar da umarni ba tare da bata lokaci ba wajen ganin an kammala makarantar sabo da muhimmancin ta ga kasa ta fannin tsaro da samar da kudaden shiga.

A wani bangaren kuma, Sanata Buba ya sha alwashin ganin an samar da ingantaccen tsaro a kasar nan ta hanyar tattaunawa da jami’an tsaro a kai a kai a matsayin sa na shugaban Kwamitin da aka kafa a Majalisar akan fannin Tsaro.

Ya ce tsaro shi ne ginshikin duk wani ci gaba sabo da haka ne ba zai yi kasa a gwiwa ba wajen ganin an samar da ingantaccen tsaro a kasarnan.

A hirarsa da ‘Yan Jaridu a ofishinsa, Sanata Buba ya yi kira da ‘Yan Nijeriya da su ba wa Jami’an tsaro hadin kai wajen ganin an samar da tsaro mai inganci a kasarnan. In da ya kara da cewa hakki ne da ya dogara a kan kowa tun da ba wanda zai magance mana barazanar tsaro a kasar nan sai mu da kammu mun hada gwiwa da jami’an tsaro.

A bangaren Ministoci da aka gabatar da sunayensu ranar Alhamis, ya yaba wa kokarin Shugaban Kasa na ganin ya gabatar da sunayen kamar yadda kundin tsarin mulki ya bukata.

Daga karshe dan majalisar ya yi kira da ‘Yan Nijeriya musamman wadanda ba a fadi sunayen Ministoci da ke Jihohin su ba da su kara hakuri cewa shugaban kasa ya yi alkawari gabatar da sauran sunayen watakila kafin a gama tantance sunayen wadanda aka gabatar.

Tags: 'Yan NijeriyaKwastammajalisa
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Nada Janar Tchiani Shugaban Rikon Kwarya A Nijar

Next Post

Shugaba Xi Ya Sanar Da Bude Gasar Wasannin Motsa Jiki Ta Daliban Jami’o’in Kasa Da Kasa A Lokacin Zafi Karo Na 31 A Chengdu

Related

NNPP
Manyan Labarai

NNPP Ta Nemi EU, Amurka Da AU Su Kawo Mata Dauki Kan Zaben Gwamnan Kano

4 hours ago
Sanatocin Arewacin Nijeriya Sun Matsa Wa Tinubu Lamba Kan Sake Bude Iyakar Nijar
Labarai

Sanatocin Arewacin Nijeriya Sun Matsa Wa Tinubu Lamba Kan Sake Bude Iyakar Nijar

6 hours ago
Da Dumi-dumi: Kotun Daukaka Kara Ta Ayyana Ranar Yanke Hukunci Kan Kujerar Gwamnan Adamawa
Labarai

Da Dumi-dumi: Kotun Daukaka Kara Ta Ayyana Ranar Yanke Hukunci Kan Kujerar Gwamnan Adamawa

8 hours ago
Tinubu Ya Gabatar Da Kudurin Kasafin Kudin 2024 A Gaban Majalisa
Manyan Labarai

Tinubu Ya Gabatar Da Kudurin Kasafin Kudin 2024 A Gaban Majalisa

14 hours ago
Za Mu Gudanar Da Bincike Kan Kundin Takardun Shari’ar Zaben Gwamnan Kano – NJC
Manyan Labarai

Za Mu Gudanar Da Bincike Kan Kundin Takardun Shari’ar Zaben Gwamnan Kano – NJC

15 hours ago
Al’ummar Jihohi 9 Na Arewacin Nijeriya Sun Gamsu Da Shirin ‘New Incentives For All’
Labarai

Al’ummar Jihohi 9 Na Arewacin Nijeriya Sun Gamsu Da Shirin ‘New Incentives For All’

16 hours ago
Next Post
Shugaba Xi Ya Sanar Da Bude Gasar Wasannin Motsa Jiki Ta Daliban Jami’o’in Kasa Da Kasa A Lokacin Zafi Karo Na 31 A Chengdu

Shugaba Xi Ya Sanar Da Bude Gasar Wasannin Motsa Jiki Ta Daliban Jami’o’in Kasa Da Kasa A Lokacin Zafi Karo Na 31 A Chengdu

LABARAI MASU NASABA

NNPP

NNPP Ta Nemi EU, Amurka Da AU Su Kawo Mata Dauki Kan Zaben Gwamnan Kano

November 29, 2023
Ya Dace Kasashen Da Suka Ci Gaba Su Cika Alkawuran Da Suka Yi Game Da Sauyin Yanayi

Ministan Wajen Sin Ya Jaddada Shawarar Kafa Kasashe 2 A Matsayin Hanyar Warware Rikicin Falasdinu Da Isra’ila

November 29, 2023
Auto Draft

Ya Dace Kasashen Da Suka Ci Gaba Su Cika Alkawuran Da Suka Yi Game Da Sauyin Yanayi

November 29, 2023
Labarin Zamanintarwa Irin Na Kasar Sin: Kimiyya Na Taimakawa Manoma Fita Daga Kangin Talauci

Labarin Zamanintarwa Irin Na Kasar Sin: Kimiyya Na Taimakawa Manoma Fita Daga Kangin Talauci

November 29, 2023
OECD: Gdpn Sin Zai Karu Da Kashi 5.2 A 2023

OECD: Gdpn Sin Zai Karu Da Kashi 5.2 A 2023

November 29, 2023
Sanatocin Arewacin Nijeriya Sun Matsa Wa Tinubu Lamba Kan Sake Bude Iyakar Nijar

Sanatocin Arewacin Nijeriya Sun Matsa Wa Tinubu Lamba Kan Sake Bude Iyakar Nijar

November 29, 2023
Sin Na Ba Da Gudummawa Wajen Samar Da Abinci Da Tsarin Samar Da Kaya A Duniya

Sin Na Ba Da Gudummawa Wajen Samar Da Abinci Da Tsarin Samar Da Kaya A Duniya

November 29, 2023
An Kammala Aikin Bututun Karkashin Ruwa Na Sabuwar Hanyar Sin Da Ta Ratsa Teku

An Kammala Aikin Bututun Karkashin Ruwa Na Sabuwar Hanyar Sin Da Ta Ratsa Teku

November 29, 2023
Da Dumi-dumi: Kotun Daukaka Kara Ta Ayyana Ranar Yanke Hukunci Kan Kujerar Gwamnan Adamawa

Da Dumi-dumi: Kotun Daukaka Kara Ta Ayyana Ranar Yanke Hukunci Kan Kujerar Gwamnan Adamawa

November 29, 2023
Xi Ya Kai Rangadin Aiki A Birnin Shanghai

Xi Ya Kai Rangadin Aiki A Birnin Shanghai

November 29, 2023
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.