ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Majalisar Tsaron Jihar Zamfara Ta Tantance Nasarorin Da Ake Samu Kan Yaƙi Da ‘Yan Bindiga

by Leadership Hausa
2 years ago
tsaro

Gwamna Dauda Lawal ya jaddada ƙudirin gwamnatinsa na inganta tsaro da bayar da ƙarin tallafi ga dakarun da ke yaƙi da ’yan bindiga a Zamfara.

A ranar Alhamis ne gwamnan ya jagoranci zaman Majalisar Tsaro ta Jihar Zamfara a fadar gwamnati da ke Gusau, babban birnin jihar.

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan Jihar Zamfara, Sulaiman Bala Idris, ya fitar ta bayyana cewa an tattauna muhimman batutuwa kan matsalar tsaro a jihar da kuma hare-haren da ’yan bindiga ke kaiwa.

ADVERTISEMENT
  • Wata Sabuwa: Wani Alkali Daga Amurka YA Dakatar Da Sake Nada Sarki Sanusi II

 

A cewarsa, taron ya samu halartar dukkan shugabannin hukumomin tsaro na jihar da suka haɗa da sojoji, ’yansanda, DSS, da dai sauransu.

LABARAI MASU NASABA

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

Yayin da yake jawabi ga shugabannin hukumomin tsaro, Gwamna Lawal ya yaba wa sojojin bisa nasarorin da aka samu kawo yanzu a yaƙin da ake yi da ’yan ta’adda.

“Taron na yau zai duba yanayin matsalar tsaro da jihar ke fama da shi, da kuma tantance irin ci gaban da muka samu, da kuma tantance wuraren da ke buƙatar ƙara ƙaimi wajen inganta tsaron rayuka da dukiyoyin jama’armu.

“Kamar yadda na sha nanata wa majalisar tsaro a ko da yaushe, fifikon gwamnatina shi ne tsaron rayuka da dukiyoyi. Don haka a ko da yaushe a shirye muke mu bayar da dukkan goyon bayan da ya kamata ga hukumomin tsaro daban-daban na jihar domin taimaka musu wajen gudanar da ayyukansu yadda ya kamata.

“Ina so in gode wa Gwamnatin Tarayya da sojoji saboda tura ƙarin dakaru zuwa Zamfara. Wannan mataki na nufin kawar da duk ‘yan bindiga, kuma mun fara ganin sakamako.

“Na kuma yaba da nasarar cafke gungun masu garkuwa da mutane a Gusau tare da kuɓutar da waɗanda aka yi garkuwa da su a faɗin jihar da suka haɗa da Gusau, Maradun, Kauran Namoda, da sauran ƙananan hukumomin. Waɗannan nasarorin da aka samu shaida ce da ke nuna tasirin ayyukan soji da ake yi a jihar.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Kotu Da Ɗansanda

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani
Manyan Labarai

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN
Labarai

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

December 21, 2025
Next Post
zamfara

Ganawar Tsoffin Gwamnonin Zamfara Ta Siyasa Ce Ba Tsaro Ba – Gwamnan Jihar

LABARAI MASU NASABA

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

December 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

December 21, 2025
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

December 20, 2025
Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

December 20, 2025
Matasa Miliyan 80 Ne Ba Su Da Aikin Yi A Nijeriya

Matasa Miliyan 80 Ne Ba Su Da Aikin Yi A Nijeriya

December 20, 2025
An Nuna Jigo Da Tambarin Shagalin Murnar Bikin Bazara Na Shekarar 2026 A Moscow

An Nuna Jigo Da Tambarin Shagalin Murnar Bikin Bazara Na Shekarar 2026 A Moscow

December 20, 2025
Auren Da Ya Fi Auren Gidan Daula Dadi Ga Mace

Auren Da Ya Fi Auren Gidan Daula Dadi Ga Mace

December 20, 2025
An Fara Aiki Da Na’urar Fasahar Samar Da Lantarki Daga Iskar CO₂ Da Aka Sarrafa A Lardin Guizhou Na Kasar Sin

An Fara Aiki Da Na’urar Fasahar Samar Da Lantarki Daga Iskar CO₂ Da Aka Sarrafa A Lardin Guizhou Na Kasar Sin

December 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.