• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Majalisar Wakilai Ta Gabatar Da Kudirin Kara Yawan Membobi Daga 360 Zuwa 366

by Yusuf Shuaibu and Sulaiman
8 months ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
majalisar kasa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An gabatar da wani kudirin doka da ke da nufin gyara sashe na 49 na kundin tsarin mulkin kasar nan na shekarar 1999, wanda aka yi wa kwaskwarima, domin ware kujeru shida na musamman ga mata da nakasassu a majalisar wakilai.

Wannan shi ne karon farko da aka taba gabatar da irinsa a majalisar wakilai wanda har ya tsallake kaaratu na farko a ranar Laraba da ta gabata.

  • An Gabatar Da Nagartattun Shirye-Shiryen CMG A Brazil
  • Gwamnatin Tarayya Da EU Sun Kulla Yarjejeniyar Bunkasa Wutar Lantarki

Mai magana da yawun majalisar, Akintunde Rotimi (Ekiti, APC) ne ya gabatar da wannan kudiri na neman a kara yawan wakilai a majalisar daga 360 zuwa 366, na karin kujeru shida musamman na mata nakasassu.
A cewar kudurin dokar, za a raba kujerun na musamman a cikin shiyyoyin siyasa shida na Nijeriya, tare da tabbatar da wakilcin mutum daya daga kowace shiyya. Dole ne ‘yan takarar wadannan kujeru su cika dukkan ka’idar da ake bukata don zama mamba a majalisar wakilan Nijeriya.

Za a gudanar da zaben wadannan mukamai ne ta hanyar kwalejin zabe da ta kunshi mambobi daga kungiyoyin nakasassu na kasa, tare da gudunmawa daga matakan kasa da na yanki a cikin tsarin zabe mai yawa.

Da zarar an zabe su, wakilan za su yi wa’adi daya da sauran ‘yan majalisar kuma za su sami alfanu daidai wa daidai kamar yadda kudirin ya bayyana.

Labarai Masu Nasaba

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya

Rotimi ya bayyana cewa kudirin dokar na da nufin bunkasa wakilcin mata da nakasassu, wadanda galibi ke fuskantar cikas ga harkokin siyasa.

“Kirkiro wadannan kujeru na musamman zai tabbatar da cewa ana jin muryoyin kungiyoyin da ba su da wakilci a matakin kasa, tare da samar da daidaito da kuma tsarin majalisar dokokin Nijeriya,” in ji shi.
Idan dai za a iya tunawa, shugaban majalisar wakilai, Abbas Tajudeen, a ranar Litinin ya ba da shawarar yin kwaskwarima ga kundin tsarin mulkin kasar na tanadar kujerun majalisar dokoki ga mata da kuma tabbatar da shigar da su cikin mukamai a majalisar zartarwa.

A wani labarin kuma, Cibiyar Nazarin Dokokin Majalisa da Dimokuradiyya ta Kasa (NILDS), ta bayyana wakilcin mata a majalisar dokokin Nijeriya, wanda a halin yanzu bai kai kashi 10% a matsayin abin kunya ba.

Wakiliyar NILDS, Titilayo Daniel ta bayyana hakan ne a jiya a yayin wani taro da aka gudanar a garin Sagamu na Jihar Ogun, inda aka mayar da hankali kan wayar da kan ‘yan majalisar mata mai taken, “Karfafa wakilcin mata a siyasance.”

Da take jawabi ga ‘yan siyasa mata sama da 100, Daniel ta bayyana muhimmancin daidaita jinsi a majalisar dokoki ta kasa. Ta ce, “Mata ba su kai kashi 10 cikin 100 na ‘yan majalisar dokoki ta kasa ba, ma’ana cewa sama da rabin al’ummarmu ba sa cikin masu yanke hukunci. Wannan kididdigar abin kunya ce ga Nijeriya idan aka kwatanta da sauran kasashen Afirka kamar Rwanda, wacce ke da kashi 61.3% na wakilai.”

Daniel ta kara da cewa matan Nijeriya na ci gaba da fuskantar cikas da dama ga shiga harkokin siyasa, tana mai nuni da cewa tsarin majalisar dokokin na nuna san kai.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Gabatar Da Nagartattun Shirye-Shiryen CMG A Brazil

Next Post

Me Ya Sa Kamfanonin Waje Masu Yawa Suka Fara Nuna Sabbin Kayayyakinsu A CIIE?

Related

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai
Tambarin Dimokuradiyya

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

2 weeks ago
APC
Tambarin Dimokuradiyya

Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya

2 weeks ago
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

3 weeks ago
‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

4 weeks ago
Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

1 month ago
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Adawa Na Cacakar APC A Yankin Arewa Maso Yamma Bisa Goyon Bayan Tazarcen Tinubu

1 month ago
Next Post
Me Ya Sa Kamfanonin Waje Masu Yawa Suka Fara Nuna Sabbin Kayayyakinsu A CIIE?

Me Ya Sa Kamfanonin Waje Masu Yawa Suka Fara Nuna Sabbin Kayayyakinsu A CIIE?

LABARAI MASU NASABA

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Ƙoƙarin Ƙungiyoyin Afrika A Gasar Kofin Duniya

June 28, 2025
Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

June 28, 2025
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

June 28, 2025
Za a Binne Ɗantata A Madina, Za Ai Yi Sallar Ga’ibi A Kano

Za a Binne Ɗantata A Madina, Za Ai Yi Sallar Ga’ibi A Kano

June 28, 2025
Me Ya Sa Syria Ta Bari Ana Amfani Da Sararin Samaniyarta Wajen Kai Wa Iran Hari?

Me Ya Sa Syria Ta Bari Ana Amfani Da Sararin Samaniyarta Wajen Kai Wa Iran Hari?

June 28, 2025
Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?

Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?

June 28, 2025
Ƙasashen Afrika 10 Da Suka Fi Girman Kasafin Kudi A 2025

Ƙasashen Afrika 10 Da Suka Fi Girman Kasafin Kudi A 2025

June 28, 2025
Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato

Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato

June 28, 2025
Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu

Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu

June 28, 2025
Hoton Tallan Taliyar Indomie

Indomie Ta Kaddamar Da Shirin Gangamin Abinci Mai Gina Jiki Na ‘Ingantaccen Abinci Domin Nasara’

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.