• English
  • Business News
Saturday, September 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Majalisar Wakilai Ta Gabatar Da Kudirin Kara Yawan Membobi Daga 360 Zuwa 366

by Yusuf Shuaibu and Sulaiman
10 months ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
majalisar kasa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An gabatar da wani kudirin doka da ke da nufin gyara sashe na 49 na kundin tsarin mulkin kasar nan na shekarar 1999, wanda aka yi wa kwaskwarima, domin ware kujeru shida na musamman ga mata da nakasassu a majalisar wakilai.

Wannan shi ne karon farko da aka taba gabatar da irinsa a majalisar wakilai wanda har ya tsallake kaaratu na farko a ranar Laraba da ta gabata.

  • An Gabatar Da Nagartattun Shirye-Shiryen CMG A Brazil
  • Gwamnatin Tarayya Da EU Sun Kulla Yarjejeniyar Bunkasa Wutar Lantarki

Mai magana da yawun majalisar, Akintunde Rotimi (Ekiti, APC) ne ya gabatar da wannan kudiri na neman a kara yawan wakilai a majalisar daga 360 zuwa 366, na karin kujeru shida musamman na mata nakasassu.
A cewar kudurin dokar, za a raba kujerun na musamman a cikin shiyyoyin siyasa shida na Nijeriya, tare da tabbatar da wakilcin mutum daya daga kowace shiyya. Dole ne ‘yan takarar wadannan kujeru su cika dukkan ka’idar da ake bukata don zama mamba a majalisar wakilan Nijeriya.

Za a gudanar da zaben wadannan mukamai ne ta hanyar kwalejin zabe da ta kunshi mambobi daga kungiyoyin nakasassu na kasa, tare da gudunmawa daga matakan kasa da na yanki a cikin tsarin zabe mai yawa.

Da zarar an zabe su, wakilan za su yi wa’adi daya da sauran ‘yan majalisar kuma za su sami alfanu daidai wa daidai kamar yadda kudirin ya bayyana.

Labarai Masu Nasaba

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

2027: Idan Kana Son Tarwatsa PDP, To Ka Dawo Da Peter Obi – Wike

Rotimi ya bayyana cewa kudirin dokar na da nufin bunkasa wakilcin mata da nakasassu, wadanda galibi ke fuskantar cikas ga harkokin siyasa.

“Kirkiro wadannan kujeru na musamman zai tabbatar da cewa ana jin muryoyin kungiyoyin da ba su da wakilci a matakin kasa, tare da samar da daidaito da kuma tsarin majalisar dokokin Nijeriya,” in ji shi.
Idan dai za a iya tunawa, shugaban majalisar wakilai, Abbas Tajudeen, a ranar Litinin ya ba da shawarar yin kwaskwarima ga kundin tsarin mulkin kasar na tanadar kujerun majalisar dokoki ga mata da kuma tabbatar da shigar da su cikin mukamai a majalisar zartarwa.

A wani labarin kuma, Cibiyar Nazarin Dokokin Majalisa da Dimokuradiyya ta Kasa (NILDS), ta bayyana wakilcin mata a majalisar dokokin Nijeriya, wanda a halin yanzu bai kai kashi 10% a matsayin abin kunya ba.

Wakiliyar NILDS, Titilayo Daniel ta bayyana hakan ne a jiya a yayin wani taro da aka gudanar a garin Sagamu na Jihar Ogun, inda aka mayar da hankali kan wayar da kan ‘yan majalisar mata mai taken, “Karfafa wakilcin mata a siyasance.”

Da take jawabi ga ‘yan siyasa mata sama da 100, Daniel ta bayyana muhimmancin daidaita jinsi a majalisar dokoki ta kasa. Ta ce, “Mata ba su kai kashi 10 cikin 100 na ‘yan majalisar dokoki ta kasa ba, ma’ana cewa sama da rabin al’ummarmu ba sa cikin masu yanke hukunci. Wannan kididdigar abin kunya ce ga Nijeriya idan aka kwatanta da sauran kasashen Afirka kamar Rwanda, wacce ke da kashi 61.3% na wakilai.”

Daniel ta kara da cewa matan Nijeriya na ci gaba da fuskantar cikas da dama ga shiga harkokin siyasa, tana mai nuni da cewa tsarin majalisar dokokin na nuna san kai.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Gabatar Da Nagartattun Shirye-Shiryen CMG A Brazil

Next Post

Me Ya Sa Kamfanonin Waje Masu Yawa Suka Fara Nuna Sabbin Kayayyakinsu A CIIE?

Related

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

13 hours ago
Daraktoci Da Jami’an FCT 7 Na Fuskantar Tuhume-tuhume Kan Badakar Fili
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Idan Kana Son Tarwatsa PDP, To Ka Dawo Da Peter Obi – Wike

13 hours ago
ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro

7 days ago
katin zabe
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Bayyana Damuwarta Kan Katunan Zabe 360,000 Da Ba A Karba Ba A Kano

1 week ago
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

Shugabannin PDP Sun Shiga Dimuwa Yayin Da APC Ke Zawarcin Wasu Gwamnoninsu

1 week ago
Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC
Tambarin Dimokuradiyya

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

2 weeks ago
Next Post
Me Ya Sa Kamfanonin Waje Masu Yawa Suka Fara Nuna Sabbin Kayayyakinsu A CIIE?

Me Ya Sa Kamfanonin Waje Masu Yawa Suka Fara Nuna Sabbin Kayayyakinsu A CIIE?

LABARAI MASU NASABA

Sashen Cinikayyar Bayar Da Hidima Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni Bakwai Na Farkon Shekarar Bana

Sashen Cinikayyar Bayar Da Hidima Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni Bakwai Na Farkon Shekarar Bana

September 5, 2025
Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Wani Sabon Tauraron Dan Adam

Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Wani Sabon Tauraron Dan Adam

September 5, 2025
Jami’an Kasa Da Kasa Sun Yi Matukar Jinjinawa Jawabin Xi Jinping

Jami’an Kasa Da Kasa Sun Yi Matukar Jinjinawa Jawabin Xi Jinping

September 5, 2025
Za Mu Riƙe Wa Minista Tijjani Muƙaminsa Bayan Hamɓarar Da Tinubu A 2027 – El-Rufai 

Ana Ci Gaba Da Caccakar El-rufai Kan Kalamansa Game Da Tsaron Kasa

September 5, 2025
Kasar Sin Ta Kasance Muhimmin Karfi Dake Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya

Kasar Sin Ta Kasance Muhimmin Karfi Dake Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya

September 5, 2025
Yadda Al’ummar Da Ke Zaune Da ‘Yan Bindiga Ke Rayuwa A Zamfara

Duk Da Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ana Ci Gaba Da Kai Hare-hare Wasu Yankunan Zamfara

September 5, 2025
Antonio Guterres Ya Yi Maraba Da Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

Antonio Guterres Ya Yi Maraba Da Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

September 5, 2025
Ban Yi Kuskure Wajen Zaben Kashim A Matsayin Mataimaki Ba – Tinubu

Ban Yi Kuskure Wajen Zaben Kashim A Matsayin Mataimaki Ba – Tinubu

September 5, 2025
Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Bikin Baje Kolin Masana’antun Kirkirarriyar Basira

Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Bikin Baje Kolin Masana’antun Kirkirarriyar Basira

September 5, 2025
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi

’Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 2 Da Wasu 156 Kan Aikata Laifuka A Jigawa

September 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.