• English
  • Business News
Thursday, October 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Majalisar Wakilai Ta Yi Kira Da A Sasanta Kan Zanga-Zangar Cire Tallafin Mai

by Abubakar Abba
2 years ago
Zanga-zanga

Majalisar wakilai ta yi kira ga kungiyar kwadago ta kasa (NLC) da sauran kungiyoyin da suka yi hadaka da su dakatar da zanga-zangar lumana da suke kan gudanarwa a fadin kasar nan kan cire tallafin man fetur da gwamnatin tarayya ta yi. 

Majalisar ta yi wannan kiran ne cikin sanarwar da mai magana da yawun majalisar Hon. Akin Rotimi ya fitar.

  • Tsohon Shugaban Kasar Ivory Coast, Konan Bedie, Ya Rasu
  • Badakalar Biliyan 1.3: EFCC Ta Maka Sule Lamido Da Wasu A Kotun Koli

A cewarsa, maimakon shiga zanga-zangar, abin da ya fi dacewa shi ne a dare teburin sulhu wanda kuma hakan ne babbar mafita ga ma’aikatan kasar ba tare da jefa rayuwar ‘yan Nijeriya a cikin wani mawuyacin hali ba.

Ya ce, duk da rokon da gwamnatin tarayya ta yi wa NLC na ta dakatar da shiga zanga-zangar ta lumana a yau Laraba, amma mu a matsayin mu na shuwagabannin jama’a, muna tausayawa ‘yan Nijeriya halin kuncin da cire tallafin man ya jefa su a ciki.

Kazalika, “Mana sane da cewa, NLC na da ‘yancin gudanar da zanga-zangar lumana domin samarwa ma’aikata da ‘yan Nijeriya saukin rayuwa kan kalubalen da kasar ke ciki a yanzu.”

LABARAI MASU NASABA

Majalisar Dattawa Ta Amince Da Amupitan A Matsayin Shugaban INEC

Amupitan Ya Isa Majalisar Dattawa Domin Tantance Shi A Matsayin Sabon Shugaban INEC

Ya kara da cewa, “Kamar sauran ‘yan Nijeriya, muna sane da cewa, ciyar da Nijeriya a gaba abu ne da ke bukatar zagewa domin a dauki matakai don amfanin kowane dan kasar, musamman da kuma yin duba ga matakan da gwamnatin tarayya ta ke kan dauka na gajeren zango domin ta saita tattalin arzikin Nijeriya.”

Ya bayyana cewa, matakan da gwamnatin tarayya tabke dauka don rage zafin radadin cire tallafin man na gajeren zango ne.

Bugu da kari, ya kuma yi kira ga shugabannin NLC da sauran kungiyoyin kwadago da suka yi hadaka da su hada hannu da majalisar wakilai a kan ci gaban da ta ke yi na tattaunawa da gwamnatin tarayya domin wanzar da shiye-shiryen da za su samar wa ‘yan Nijeriya saukin rayuwa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sabbin Ministoci
Manyan Labarai

Majalisar Dattawa Ta Amince Da Amupitan A Matsayin Shugaban INEC

October 16, 2025
Amupitan Ya Isa Majalisar Dattawa Domin Tantance Shi A Matsayin Sabon Shugaban INEC
Manyan Labarai

Amupitan Ya Isa Majalisar Dattawa Domin Tantance Shi A Matsayin Sabon Shugaban INEC

October 16, 2025
Majalisar Dattawa Ta Fara Tantance Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC
Manyan Labarai

Majalisar Dattawa Ta Fara Tantance Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC

October 16, 2025
Next Post
Da Dumi-dumi: Tinubu Ya Aika Wa Majalisar Dattawa Karin Sunayen Ministoci

Da Dumi-dumi: Tinubu Ya Aika Wa Majalisar Dattawa Karin Sunayen Ministoci

LABARAI MASU NASABA

Xi Jinping Ya Yi Kira Da a Kara Horar Da Kwararrun Masana A Fannin Aikin Gona

Xi Jinping Ya Yi Kira Da a Kara Horar Da Kwararrun Masana A Fannin Aikin Gona

October 16, 2025
Gwamna Lawal Ya Yi Alhinin Kisan Jami’an Tsaro A Zamfara

Gwamna Lawal Ya Yi Alhinin Kisan Jami’an Tsaro A Zamfara

October 16, 2025
Shugabannin Kasashe Da Dama Sun Yaba Wa Sin Kan Gudummawar Da Ta Bayar A Fannin Tabbatar Da Daidaiton Jinsi

Shugabannin Kasashe Da Dama Sun Yaba Wa Sin Kan Gudummawar Da Ta Bayar A Fannin Tabbatar Da Daidaiton Jinsi

October 16, 2025
Sabbin Ministoci

Majalisar Dattawa Ta Amince Da Amupitan A Matsayin Shugaban INEC

October 16, 2025
Ɗaga Matsayin Dangantakar Zambia Da Sin Ya Haifar Da Manyan Nasarori

Ɗaga Matsayin Dangantakar Zambia Da Sin Ya Haifar Da Manyan Nasarori

October 16, 2025
Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Fursunoni Bayan Kammala Zaman Kurkuku

Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Fursunoni Bayan Kammala Zaman Kurkuku

October 16, 2025
Amupitan Ya Isa Majalisar Dattawa Domin Tantance Shi A Matsayin Sabon Shugaban INEC

Amupitan Ya Isa Majalisar Dattawa Domin Tantance Shi A Matsayin Sabon Shugaban INEC

October 16, 2025
Majalisar Dattawa Ta Fara Tantance Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC

Majalisar Dattawa Ta Fara Tantance Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC

October 16, 2025
An Dakatar Da Tashi Da Saukar Jirage A Kenya Don Karɓar Gawar Raila Odinga

An Dakatar Da Tashi Da Saukar Jirage A Kenya Don Karɓar Gawar Raila Odinga

October 16, 2025
Gwamnan Edo Ya Umarci Kwamishinoni Su Riƙa Sanya Hular Tinubu

Gwamnan Edo Ya Umarci Kwamishinoni Su Riƙa Sanya Hular Tinubu

October 16, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.