• English
  • Business News
Friday, November 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Makiyayi Ya Datse Hannun Manomi A Bauchi

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Makiyayi

Rundunar ‘yansandan jihar Bauchi ta cafke wani yaro dan shekara 15 a duniya, Adamu Ibrahim, bisa zarginsa da sara hannun hagun wani manomi biyo bayan rashin jituwar da ta shiga tsakaninsu.

Binciken ‘yansanda ya nuna musu cewa a ranar 24 ga watan Agustan 2023, wanda ake zargi (Adamu Ibrahim) dauke da sanda da adda ya shiga cikin gonan wanda lamarin ya shafa tare da lalata masa amfanin gonar da har yanzu ba a kiyasce adadinsu ba.

  • EFCC Da CCB Sun Gayyaci Muhyi Magaji Rimin Gado
  • Mutane 12 Sun Mutu, 80 Sun Jikkata A Bikin Bude Wasanni A Madagascar

A wata sanarwa da kakakin ‘yansandan jihar Bauchi, Ahmad Muhammad Wakil ya fitar a ranar Asabar, ya ce, bayan barkewar rashin jituwa a tsakaninsu, wanda ake zargin ya sara hannun manomin da adda biyo bayan neman da ya yi masa da ya fice masa daga cikin gona.

Wakil ya ce, “Shi wanda ake zargin ya zaro adda tare da daba wa hannun daman manomin.”

Kazalika, binciken ‘yansanda ya kara gano musu cewa shi Adamun ya saba shiga cikin gonar manomin da shanunsa domin kiwo.

LABARAI MASU NASABA

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna

Ya ce, an fara kai ruwa-rana tsakaninsu ne biyo bayan jerin korafe-korafen da manomin ya kai wa mahaifin Adamu da ke cewa yana shiga gonarsa domin lalata masa amfanin gona.

“Bayan samun faruwar lamarin, kwamandan ‘yanki ya tashi tsaye domin shiga cikin lamarin domin kauce wa matakin da zai kai a je matakin fada tsakanin manomi da makiyayi wanda hakan ya sanya suka kamo wanda ake zargi,” in ji jami’in watsa labaran.

An garzaya da manomin zuwa asibitin koyarwa na ATBUTH kuma a halin yanzu yana kan murmurewa.

Kwamishinan ‘yansandan jihar Bauchi CP Auwal Musa Mohammed, ya gargadi manoma da suke kauce wa shiga cikin gonakan mutane a fadin jihar domin kauce wa samun rashin fahimta.

Kwamishinan ya umarci a gurfanar da wanda ake zargin a gaban kotu idan aka kammala bincike.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma
Manyan Labarai

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

November 7, 2025
APC Da Uba Sani Ba Su Lashe Zaben Gwamnan Kaduna Ba -PDP
Labarai

Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna

November 7, 2025
Jerin Gwarazan Taurarinmu!
Rahotonni

Jerin Gwarazan Taurarinmu!

November 7, 2025
Next Post
Tsohon Kakakin Sojoji, Janar Onyeuko Ya Kwanta Dama

Tsohon Kakakin Sojoji, Janar Onyeuko Ya Kwanta Dama

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Shirin Shugaba Tinubu Na ‘Renewed Hope’ Zai Karfafa Wa Manoma Gwiwa – Oyebanji

November 7, 2025
Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

November 7, 2025
Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

November 7, 2025
An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

November 7, 2025
Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

November 7, 2025
An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

November 7, 2025
APC Da Uba Sani Ba Su Lashe Zaben Gwamnan Kaduna Ba -PDP

Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna

November 7, 2025
Kasar Sin Ta Musanta Zargin Da Wakilin Amurka Ya Yi Game Da Batun Sauyin Yanayi

Kasar Sin Ta Musanta Zargin Da Wakilin Amurka Ya Yi Game Da Batun Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Halarci Taron COP30 A Brazil

Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Halarci Taron COP30 A Brazil

November 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.