• English
  • Business News
Thursday, August 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manoma Na Bukatar A Yi Rangwamen Kayan Aikin Noma – Wasu Jami’ai

by Sulaiman and Abubakar Abba
1 year ago
in Noma Da Kiwo
0
IFAD
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Babban Sakatare a Ma’aikatar Aikin Noma ta Jihar Neja, Dakta Mathew Ahmed, ya yi kira da a samar wa da manoman jihar rangwamen farashin takin zamani da sauran kayan aikin noma, don samar da wadataccen abinci, duba da karancin abinci da ake a ci gaba da fuskanta a wannan kasa.

A hirarsa da kamfanin dillancin labarai na Minna, babban birnin jihar; Mathew ya yi nuni da cewa, ya kamata gwamnatin tarayya ta rage wa manoman kasar farashin takin zamani tare kuma da samar musu da kayan aikin noma, wanda ya ce; yin hakan zai bai wa manoman damar shafe shekara guda suna yin noma.

  • Noma: Gwamnan Zamfara Ya Nemo Masu Zuba Jari Daga Ƙasar Turkiyya
  • Ginin Makaranta Ya Rufta A Jos, Ɗalibai Da Dama Sun Maƙale

Kazalika ya yi nuni da cewa, samar wa da moman kayan aikin noman rani sau uku a shekara, zai taimaka wajen kara samar da wadataccen abinci da kuma kara habaka tattalin arzikin wannan kasa baki-daya.

Haka zalika sanar da cewa, Gwamnatin Umaru Bago; tuni ta bazama wajen farfado da aikin noma a jihar, inda ta samar da taraktocin noma guda 1,000, injinan aikin noma guda 10,000 da sauransu ga manoman jihar.

Bugu da kari ya kuma kara da cewa, gwamnatin ta kuma samar da injinan yin girbi guda 100 da sauran kayan aikin noma, don bai wa mata da matasan jihar damar rungumar akin noma.

Labarai Masu Nasaba

Manoma Sun Caccaki Tinubu Kan Ƙarfafa Shigo Da Shinkafa Da Masara Daga Ƙasashen Waje

Manyan Ƙalubale Takwas Da Ke Shafar Farashin Tumatir

Ya ci gaba da cewa, gwamnati ta kuma samar da guraren yin noman ranin na gwaji guda 100, inda ya sanar da cewa; a yanzu haka gwamnatin na kan noma hekta miliyan daya, wanda a kowace karamar hukuma guda a jihar; aka ware mata hekta 10,000.

Sannan, a kan kokarin da gwamnatin jihar ke yi na magance kalubalen rashin tsaro ya ce, Gwamnan Jihar ya kirkiro da ma’aikatun kula da gonaki tare da samar da tsaro da kuma ta kula da harkokin makiyaya, musamman domin dakile rikicin manoma da makiyaya a fadin jihar.

Ya kara da cewa, kirkiro da wadannan ma’aikatu ko shakka babu; za su taimaka wajen tabbatar da bayar da kariya ga al’ummomin da ke a jihar daga hare-haren ‘yan bindiga da kuma satar mutane, a daukacin kananan hukumomi 25 na jihar.

Kazalika ya ci gaba da cewa, Gwamnan Jihar na ganawa da Sarakunan Gargajiya akai-akai, domin duba a kan kalubalen rashin tsaron; ya kuma kara karfafa kungoyin tsaro na sa kai, yadda za su yi aiki tare da hukumin  tsaro kafada da kafada, domin manoman jihar su samu damar noma gonakinsu tare kuma da kara magance kalubalen rashin wadataccen abinci a jihar.

A kokarinta na magance karancin abinci, Gwamnatin Jihar Nassarawa ta bayyana cewa, ta fara noman Shinkafa, Kantu, Gero da kuma Masara kimanin hekta 10,000 a yankin  Jangwa da ke          Karamar Hu

Gwamnatin tarayya ta sanya matasa 200 cikin shirinta na bunkasa noma, wanda ake kira da ‘ATASP-1’.

Matasan da za su amfana da wannan shiri, an zabo su ne daga sassa daban-daban guda hudu na fadin kasar nan.

Jami’in shirin na kasa, mai kula da shiyoyin Jihohin Kano da Jigawa; Dakta Ibrahim Muhammed Arabi ne, ya sanar da hakan a lokacin bude taron shirin.

Arabi, wanda jami’in da ke kula da aikin noma; domin riba na kasa kan shirin, Dakta Kunle Alege ya wakilce shi a wajen taron; ya ce a karkashin shirin za a horas da matasa 50 wadanda aka zabo daga kowace shiyya guda ta kasar nan, wanda hakan ya sanya adadin matasan suka kai 200.

Ya kara da cewa, za a koyar da matasan yadda za su aiwatar da noman, don kasuwancin zamani tare kuma da yin amfani da dabarun zamani; domin cimma nasarar shirin.

A cewarsa, bayan an horar da matasan za kuma ci gaba da biyan su tare da tallafa masu da kudade; domin samun damar gudanar da aikin yadda ya kamata.

Shi ma wani jami’i, a sashen cibiyar aikin noma ta (IITA), Dakta Alpha Kamara ya bukaci matasan da su yi amfani da horon da aka ba su, don zama masu dogaro da kawunansu ta hanyar aikin noma.kumar  Awe ta jihar.

Gwamnan Jihar, Abdullahi Sule ne ya sanar da hakan jim kadan bayan ya duba aikin, inda ya bayyana cewa; aikin na daya daga cikin ajandar shirin Gwamnatin Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu na samar da tsaro.

Sule ya sanar da cewa, Allah ya albarkaci Jihar Nassarawa  da kasar noma mai matukar kyawun gaske, wanda hakan ya sa al’ummar jihar ke yin noma; don zama masu dogaro da kawunansu.

Gwamnan ya ci gaba da cewa, ana yin aikin ne a karkashin shirin gwamnatin na  bunkasa aikin noma wato (NADP).

Sule ya kara da cewa, za a sanya manoman jihar a cikin tsarin aikin noman, wanda hakan zai ba su damar samun ingantaccen Irin noma da sauran kayan aikin noma.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Gwamnatin TarayyaRashin TsaroTsadar Taki
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasar Sin Ta Yi Kakkausar Suka Kan Kalaman Tsokana Da Sakatare Janar Na Kungiyar Tsaro Ta NATO Ya Yi Kan Kasar

Next Post

2027: A Kasar Da Babu Manufa Kadai Kwankwaso Zai Iya Zama Shugaban Kasa – APC

Related

Manoma Sun Caccaki Tinubu Kan Ƙarfafa Shigo Da Shinkafa Da Masara Daga Ƙasashen Waje
Noma Da Kiwo

Manoma Sun Caccaki Tinubu Kan Ƙarfafa Shigo Da Shinkafa Da Masara Daga Ƙasashen Waje

4 days ago
Manyan Ƙalubale Takwas Da Ke Shafar Farashin Tumatir
Noma Da Kiwo

Manyan Ƙalubale Takwas Da Ke Shafar Farashin Tumatir

5 days ago
Sin Ta Gaggauta Aikin Gyara Da Kyautata Ababen Aikin Gona
Noma Da Kiwo

Asusun NADF, OCP Da Gwamnatin Katsina Sun Kaddamar Da Noman Hekta 50

2 weeks ago
Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

2 weeks ago
Abinci
Noma Da Kiwo

Dalilin Gwamnatin Tarayya Na Yin Hadaka Da Jihar Nasarawa Don Bunkasa Noma

3 weeks ago
Shettima
Noma Da Kiwo

Nijeriya Za Ta Rika Samun Naira Tiriliyan Uku A Aikin Tatsar Rogo Duk Shekara – Kashim

3 weeks ago
Next Post
2027: A Kasar Da Babu Manufa Kadai Kwankwaso Zai Iya Zama Shugaban Kasa – APC

2027: A Kasar Da Babu Manufa Kadai Kwankwaso Zai Iya Zama Shugaban Kasa – APC

LABARAI MASU NASABA

Nijeriya Da Indiya Za Su Haɗa Kai Wajen Yaƙi Da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya Da Indiya Za Su Haɗa Kai Wajen Yaƙi Da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi

August 7, 2025
Al Hilal Za Ta Biya Yuro Miliyan 53 Don Ɗaukar Nunez Daga Liverpool

Al Hilal Za Ta Biya Yuro Miliyan 53 Don Ɗaukar Nunez Daga Liverpool

August 7, 2025
Masu Ƙwacen Waya Sun Kashe Ɗalibin BUK A Kano

Masu Ƙwacen Waya Sun Kashe Ɗalibin BUK A Kano

August 7, 2025
Jami’an Tsaro Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga A Zamfara, Sun Ƙwato Bindigogi

Jami’an Tsaro Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga A Zamfara, Sun Ƙwato Bindigogi

August 7, 2025
An Bude Bikin Fina-Finan Kasar Sin A Zimbabwe

An Bude Bikin Fina-Finan Kasar Sin A Zimbabwe

August 7, 2025
Jama’a Suke Tona Asirin Gurɓatattun Jami’anmu – Kwamishinan ‘Yansandan Kano

Jama’a Suke Tona Asirin Gurɓatattun Jami’anmu – Kwamishinan ‘Yansandan Kano

August 7, 2025
Yawancin ‘Yan Siyasar Nijeriya Ba Su Da Tarbiyya – Sarki Sanusi II

Yawancin ‘Yan Siyasar Nijeriya Ba Su Da Tarbiyya – Sarki Sanusi II

August 7, 2025
Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Ziyarar Boris Johnson A Taiwan

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Ziyarar Boris Johnson A Taiwan

August 6, 2025
Yanzu-yanzu: WAEC Ta Rufe Shafin Duba Jarabawar WASSCE 2025

Yanzu-yanzu: WAEC Ta Rufe Shafin Duba Jarabawar WASSCE 2025

August 6, 2025
Hukumar Kwastam Ta Kama Tankar Mai Dauke Da Buhunan Shinkafa A Kaduna

Hukumar Kwastam Ta Kama Tankar Mai Dauke Da Buhunan Shinkafa A Kaduna

August 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.