ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manoma Na Bukatar A Yi Rangwamen Kayan Aikin Noma – Wasu Jami’ai

by Sulaiman and Abubakar Abba
2 years ago
IFAD

Babban Sakatare a Ma’aikatar Aikin Noma ta Jihar Neja, Dakta Mathew Ahmed, ya yi kira da a samar wa da manoman jihar rangwamen farashin takin zamani da sauran kayan aikin noma, don samar da wadataccen abinci, duba da karancin abinci da ake a ci gaba da fuskanta a wannan kasa.

A hirarsa da kamfanin dillancin labarai na Minna, babban birnin jihar; Mathew ya yi nuni da cewa, ya kamata gwamnatin tarayya ta rage wa manoman kasar farashin takin zamani tare kuma da samar musu da kayan aikin noma, wanda ya ce; yin hakan zai bai wa manoman damar shafe shekara guda suna yin noma.

  • Noma: Gwamnan Zamfara Ya Nemo Masu Zuba Jari Daga Ƙasar Turkiyya
  • Ginin Makaranta Ya Rufta A Jos, Ɗalibai Da Dama Sun Maƙale

Kazalika ya yi nuni da cewa, samar wa da moman kayan aikin noman rani sau uku a shekara, zai taimaka wajen kara samar da wadataccen abinci da kuma kara habaka tattalin arzikin wannan kasa baki-daya.

ADVERTISEMENT

Haka zalika sanar da cewa, Gwamnatin Umaru Bago; tuni ta bazama wajen farfado da aikin noma a jihar, inda ta samar da taraktocin noma guda 1,000, injinan aikin noma guda 10,000 da sauransu ga manoman jihar.

Bugu da kari ya kuma kara da cewa, gwamnatin ta kuma samar da injinan yin girbi guda 100 da sauran kayan aikin noma, don bai wa mata da matasan jihar damar rungumar akin noma.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

Ya ci gaba da cewa, gwamnati ta kuma samar da guraren yin noman ranin na gwaji guda 100, inda ya sanar da cewa; a yanzu haka gwamnatin na kan noma hekta miliyan daya, wanda a kowace karamar hukuma guda a jihar; aka ware mata hekta 10,000.

Sannan, a kan kokarin da gwamnatin jihar ke yi na magance kalubalen rashin tsaro ya ce, Gwamnan Jihar ya kirkiro da ma’aikatun kula da gonaki tare da samar da tsaro da kuma ta kula da harkokin makiyaya, musamman domin dakile rikicin manoma da makiyaya a fadin jihar.

Ya kara da cewa, kirkiro da wadannan ma’aikatu ko shakka babu; za su taimaka wajen tabbatar da bayar da kariya ga al’ummomin da ke a jihar daga hare-haren ‘yan bindiga da kuma satar mutane, a daukacin kananan hukumomi 25 na jihar.

Kazalika ya ci gaba da cewa, Gwamnan Jihar na ganawa da Sarakunan Gargajiya akai-akai, domin duba a kan kalubalen rashin tsaron; ya kuma kara karfafa kungoyin tsaro na sa kai, yadda za su yi aiki tare da hukumin  tsaro kafada da kafada, domin manoman jihar su samu damar noma gonakinsu tare kuma da kara magance kalubalen rashin wadataccen abinci a jihar.

A kokarinta na magance karancin abinci, Gwamnatin Jihar Nassarawa ta bayyana cewa, ta fara noman Shinkafa, Kantu, Gero da kuma Masara kimanin hekta 10,000 a yankin  Jangwa da ke          Karamar Hu

Gwamnatin tarayya ta sanya matasa 200 cikin shirinta na bunkasa noma, wanda ake kira da ‘ATASP-1’.

Matasan da za su amfana da wannan shiri, an zabo su ne daga sassa daban-daban guda hudu na fadin kasar nan.

Jami’in shirin na kasa, mai kula da shiyoyin Jihohin Kano da Jigawa; Dakta Ibrahim Muhammed Arabi ne, ya sanar da hakan a lokacin bude taron shirin.

Arabi, wanda jami’in da ke kula da aikin noma; domin riba na kasa kan shirin, Dakta Kunle Alege ya wakilce shi a wajen taron; ya ce a karkashin shirin za a horas da matasa 50 wadanda aka zabo daga kowace shiyya guda ta kasar nan, wanda hakan ya sanya adadin matasan suka kai 200.

Ya kara da cewa, za a koyar da matasan yadda za su aiwatar da noman, don kasuwancin zamani tare kuma da yin amfani da dabarun zamani; domin cimma nasarar shirin.

A cewarsa, bayan an horar da matasan za kuma ci gaba da biyan su tare da tallafa masu da kudade; domin samun damar gudanar da aikin yadda ya kamata.

Shi ma wani jami’i, a sashen cibiyar aikin noma ta (IITA), Dakta Alpha Kamara ya bukaci matasan da su yi amfani da horon da aka ba su, don zama masu dogaro da kawunansu ta hanyar aikin noma.kumar  Awe ta jihar.

Gwamnan Jihar, Abdullahi Sule ne ya sanar da hakan jim kadan bayan ya duba aikin, inda ya bayyana cewa; aikin na daya daga cikin ajandar shirin Gwamnatin Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu na samar da tsaro.

Sule ya sanar da cewa, Allah ya albarkaci Jihar Nassarawa  da kasar noma mai matukar kyawun gaske, wanda hakan ya sa al’ummar jihar ke yin noma; don zama masu dogaro da kawunansu.

Gwamnan ya ci gaba da cewa, ana yin aikin ne a karkashin shirin gwamnatin na  bunkasa aikin noma wato (NADP).

Sule ya kara da cewa, za a sanya manoman jihar a cikin tsarin aikin noman, wanda hakan zai ba su damar samun ingantaccen Irin noma da sauran kayan aikin noma.

manoma
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku
  • Sulaiman
    Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito
  • Sulaiman
    An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing
  • Sulaiman
    2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed
manoma
Abubakar Abba
+ posts Bio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Gwamnatin Kwara Na Zuba Dala Biliyan 70 A Fannin Kiwon Dabbobi
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Cibiyar IAR Ta Gudanar Da Ayyukan Bincike 140 Kan Sabbin Amfanin Gona 

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

May 31, 2026
Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
Noma Da Kiwo

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

May 31, 2026
Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Noma Da Kiwo

IAR Ta Fara Horas Da Malaman Gona Don Fuskantar Daminar Bana

May 24, 2026
Next Post
2027: A Kasar Da Babu Manufa Kadai Kwankwaso Zai Iya Zama Shugaban Kasa – APC

2027: A Kasar Da Babu Manufa Kadai Kwankwaso Zai Iya Zama Shugaban Kasa – APC

LABARAI MASU NASABA

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.