• English
  • Business News
Monday, August 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manoman Kano Da Kaduna Za Su Amfana Da Shirin Yaki Da Cutar Tumatir

by Abubakar Abba
1 year ago
in Noma Da Kiwo
0
Manoman Kano Da Kaduna Za Su Amfana Da Shirin Yaki Da Cutar Tumatir
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wata gidauniyar shirin ‘ya’yan Itatuwa da ke gudanar da aikinta a Nijeriya, wato (HortiNigeria), ta wanzar da wani shiri nata na yakar cutar da ke lalata Tumatirin da manoma suka shuka, wanda a turance ake kira da suna ‘Tuta Absoluta’.

Gidauniyar ta wanzar da shirin ne a Jihohin Kano, Kaduna da kuma a sauran wasu jihohi uku, a karkashin shirin aikin noma na Kasar Jamus.

  • Yau Kotun Tarayya Za Ta Yanke Hukuncin Masarautar Kano
  • Daga Kai Kuɗin Fansa ‘Yan Bindiga Sun Kashe Shi A Dajin Kachiya

Har ila yau, ta yi hakan ne; domin sama wa manoma kayan aikin da za su yaki wannan cuta da ta jima shekara da shekaru tana addabar Tumatirin da manoma suka shuka.

Kazalika, Gidauniyar ta wanzar da wannan aikin ne ta hanyar yin hadaka da wasu masu ruwa da tsaki a wadannan jihohi da abin ya shafa.

A karkashin hadakar, manoma Tumatirin kimanin 60,000 ne za su amfana da sabbin kayan aikin na zamani, domin yakar cutar ta mai suna ‘Tuta absoluta’ a Jihohin Kano da Kaduna da kuma sauran wasu jihohi uku.

Labarai Masu Nasaba

Manoma Sun Caccaki Tinubu Kan Ƙarfafa Shigo Da Shinkafa Da Masara Daga Ƙasashen Waje

Manyan Ƙalubale Takwas Da Ke Shafar Farashin Tumatir

Jagoran aikin tare da fadakarwa na Gidauniyar, Malam Abdullahi Umar ya sanar da hakan ne a yayin taron wayar da kan manoman Tumatirin, wanda Gidanuniyar ta gudanar a gonakin wasu daga cikin manoman da cutar ta bulla a bangaren nasu.

Haka zalika, Gidauniyar ta yi taron ne a karkashin wani aikinta na kare kwarin da ke yi wa Tumatir din da aka shuka illa, wato (IPM).

A cewar Abdullahi, “Manoma Tumatirin sama da 60,000 da ke Jihohin Kano da Kaduna sauran wasu jihohi ne muke sa ran za su amfana da kayan aikin na zamani”.

Ya ci gaba da cewa, a karkashin aikin za a horar da manoma a yankuna daban-daban da ke fadin jihar.

“Mun jima muna karfafa wa manoman Tumatir gwiwa, musamman a kan cewa kada su sake su gaza wajen ci gaba da yin wannan noma na Tumatir, sakamakon bullar wannan cuta; domin kuwa muna da yakinin cewa; akwai yadda za a yi a iya magance cutar ba da jimawa ba, da yardar Allah”.

Kazalika, ya kuma sake bayyana cewa; muna nan muna ci gaba da kokarin sama wa wadannan manoman na Tumatir kasuwa, yadda za su rika sayar da shi cikin sauki tare kuma da samun kudaden shiga a cikin aljihunansu.

Shi ma a nasa bangaren, wani kwararre a cikin aikin; Mista Sabastine Agada Obaje ya yi nuni da cewa, yin gwajin na da matukar mahimmanci, domin kuwa ta hanyar yin gwajin ne za a iya taimaka wa manoman yin amfani da dabarun fasahar zamani wajen yin wannan noma na Tumatir.

Guda daga cikin manoman Tumatirin, Malam Uba Bello a nasa jawabin a wajen gwajin ya bayyana cewa, taron ya kara wa manoman Tumatirin kwarin gwaiwa, kan yadda za su tunkari kalubalen bullar cutar a gonakinsu.

A cewar tasa, sabuwar fasahar zamanin; tabbas za ta taimaka wa manoman Tumatir, kan yadda za su kara habaka sana’arsu ta wannan noma na Tumatir.

Ya kara da cewa, hakan zai kuma bai wa sauran manoman; musamman wadanda cutar ta sa suka dakatar da yin noman Timatirin samun damar dawowa cikin sana’ar gadan-gadan.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KadunakanoManoma
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ministan Niger: Kullum Niger Tana Daukar Sin a Matsayin Abokiyar Hadin Kanta Ta Farko

Next Post

Firaministan Kasar Sin Zai Halarci Taron Summer Davos Na 2024

Related

Manoma Sun Caccaki Tinubu Kan Ƙarfafa Shigo Da Shinkafa Da Masara Daga Ƙasashen Waje
Noma Da Kiwo

Manoma Sun Caccaki Tinubu Kan Ƙarfafa Shigo Da Shinkafa Da Masara Daga Ƙasashen Waje

10 hours ago
Manyan Ƙalubale Takwas Da Ke Shafar Farashin Tumatir
Noma Da Kiwo

Manyan Ƙalubale Takwas Da Ke Shafar Farashin Tumatir

2 days ago
Sin Ta Gaggauta Aikin Gyara Da Kyautata Ababen Aikin Gona
Noma Da Kiwo

Asusun NADF, OCP Da Gwamnatin Katsina Sun Kaddamar Da Noman Hekta 50

1 week ago
Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

1 week ago
Abinci
Noma Da Kiwo

Dalilin Gwamnatin Tarayya Na Yin Hadaka Da Jihar Nasarawa Don Bunkasa Noma

2 weeks ago
Shettima
Noma Da Kiwo

Nijeriya Za Ta Rika Samun Naira Tiriliyan Uku A Aikin Tatsar Rogo Duk Shekara – Kashim

2 weeks ago
Next Post
Firaministan Kasar Sin Zai Halarci Taron Summer Davos Na 2024

Firaministan Kasar Sin Zai Halarci Taron Summer Davos Na 2024

LABARAI MASU NASABA

Wani Babban Jigon APC Ya Fice Daga Jam’iyyar A Katsina

Wani Babban Jigon APC Ya Fice Daga Jam’iyyar A Katsina

August 3, 2025
Sanata Shehu Buba Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Da Rigakafin Shanu A Bauchi

Sanata Shehu Buba Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Da Rigakafin Shanu A Bauchi

August 3, 2025
Waɗanne Ƙasashe Ne Suka Amince Da Kafa Ƙasar Falasɗinu?

Waɗanne Ƙasashe Ne Suka Amince Da Kafa Ƙasar Falasɗinu?

August 3, 2025
Dangote Ya Ɗauki Nauyin Bikin Baje Kolin Gidajen Afrika Da Mahalarta Ƙasashe 21

Dangote Ya Ɗauki Nauyin Bikin Baje Kolin Gidajen Afrika Da Mahalarta Ƙasashe 21

August 3, 2025
An Fara Bayar Da Hidimomin Da Suka Shafi Sauka Da Tashi Domin Gasar Wasanni Ta Duniya Ta Chengdu

An Fara Bayar Da Hidimomin Da Suka Shafi Sauka Da Tashi Domin Gasar Wasanni Ta Duniya Ta Chengdu

August 3, 2025
Rikici Ya Ɓarke A Zaɓen Ribas, Ƴan PDP Sun Fito A Matsayin Ƴan Takarar APC

Rikici Ya Ɓarke A Zaɓen Ribas, Ƴan PDP Sun Fito A Matsayin Ƴan Takarar APC

August 3, 2025
Ana Gaggauta Ayyukan Gyara Tituna Da Gadojin Da Ambaliya Ta Lalata A Arewacin Kasar Sin

Ana Gaggauta Ayyukan Gyara Tituna Da Gadojin Da Ambaliya Ta Lalata A Arewacin Kasar Sin

August 3, 2025
Shugabar Tanzania Ta Kaddamar Da Cibiyar Cinikayya Da Jigila Da Sin Ta Gina A Kasar

Shugabar Tanzania Ta Kaddamar Da Cibiyar Cinikayya Da Jigila Da Sin Ta Gina A Kasar

August 3, 2025
Manoma Sun Caccaki Tinubu Kan Ƙarfafa Shigo Da Shinkafa Da Masara Daga Ƙasashen Waje

Manoma Sun Caccaki Tinubu Kan Ƙarfafa Shigo Da Shinkafa Da Masara Daga Ƙasashen Waje

August 3, 2025
Amurka Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Zuwa Ƙasarta Domin Haihuwa

Amurka Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Zuwa Ƙasarta Domin Haihuwa

August 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.