• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manoman Kano Da Kaduna Za Su Amfana Da Shirin Yaki Da Cutar Tumatir

by Abubakar Abba
12 months ago
in Noma Da Kiwo
0
Manoman Kano Da Kaduna Za Su Amfana Da Shirin Yaki Da Cutar Tumatir
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wata gidauniyar shirin ‘ya’yan Itatuwa da ke gudanar da aikinta a Nijeriya, wato (HortiNigeria), ta wanzar da wani shiri nata na yakar cutar da ke lalata Tumatirin da manoma suka shuka, wanda a turance ake kira da suna ‘Tuta Absoluta’.

Gidauniyar ta wanzar da shirin ne a Jihohin Kano, Kaduna da kuma a sauran wasu jihohi uku, a karkashin shirin aikin noma na Kasar Jamus.

  • Yau Kotun Tarayya Za Ta Yanke Hukuncin Masarautar Kano
  • Daga Kai Kuɗin Fansa ‘Yan Bindiga Sun Kashe Shi A Dajin Kachiya

Har ila yau, ta yi hakan ne; domin sama wa manoma kayan aikin da za su yaki wannan cuta da ta jima shekara da shekaru tana addabar Tumatirin da manoma suka shuka.

Kazalika, Gidauniyar ta wanzar da wannan aikin ne ta hanyar yin hadaka da wasu masu ruwa da tsaki a wadannan jihohi da abin ya shafa.

A karkashin hadakar, manoma Tumatirin kimanin 60,000 ne za su amfana da sabbin kayan aikin na zamani, domin yakar cutar ta mai suna ‘Tuta absoluta’ a Jihohin Kano da Kaduna da kuma sauran wasu jihohi uku.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

Jagoran aikin tare da fadakarwa na Gidauniyar, Malam Abdullahi Umar ya sanar da hakan ne a yayin taron wayar da kan manoman Tumatirin, wanda Gidanuniyar ta gudanar a gonakin wasu daga cikin manoman da cutar ta bulla a bangaren nasu.

Haka zalika, Gidauniyar ta yi taron ne a karkashin wani aikinta na kare kwarin da ke yi wa Tumatir din da aka shuka illa, wato (IPM).

A cewar Abdullahi, “Manoma Tumatirin sama da 60,000 da ke Jihohin Kano da Kaduna sauran wasu jihohi ne muke sa ran za su amfana da kayan aikin na zamani”.

Ya ci gaba da cewa, a karkashin aikin za a horar da manoma a yankuna daban-daban da ke fadin jihar.

“Mun jima muna karfafa wa manoman Tumatir gwiwa, musamman a kan cewa kada su sake su gaza wajen ci gaba da yin wannan noma na Tumatir, sakamakon bullar wannan cuta; domin kuwa muna da yakinin cewa; akwai yadda za a yi a iya magance cutar ba da jimawa ba, da yardar Allah”.

Kazalika, ya kuma sake bayyana cewa; muna nan muna ci gaba da kokarin sama wa wadannan manoman na Tumatir kasuwa, yadda za su rika sayar da shi cikin sauki tare kuma da samun kudaden shiga a cikin aljihunansu.

Shi ma a nasa bangaren, wani kwararre a cikin aikin; Mista Sabastine Agada Obaje ya yi nuni da cewa, yin gwajin na da matukar mahimmanci, domin kuwa ta hanyar yin gwajin ne za a iya taimaka wa manoman yin amfani da dabarun fasahar zamani wajen yin wannan noma na Tumatir.

Guda daga cikin manoman Tumatirin, Malam Uba Bello a nasa jawabin a wajen gwajin ya bayyana cewa, taron ya kara wa manoman Tumatirin kwarin gwaiwa, kan yadda za su tunkari kalubalen bullar cutar a gonakinsu.

A cewar tasa, sabuwar fasahar zamanin; tabbas za ta taimaka wa manoman Tumatir, kan yadda za su kara habaka sana’arsu ta wannan noma na Tumatir.

Ya kara da cewa, hakan zai kuma bai wa sauran manoman; musamman wadanda cutar ta sa suka dakatar da yin noman Timatirin samun damar dawowa cikin sana’ar gadan-gadan.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KadunakanoManoma
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ministan Niger: Kullum Niger Tana Daukar Sin a Matsayin Abokiyar Hadin Kanta Ta Farko

Next Post

Firaministan Kasar Sin Zai Halarci Taron Summer Davos Na 2024

Related

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

2 hours ago
Neja
Noma Da Kiwo

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

9 hours ago
Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani
Noma Da Kiwo

Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani

1 week ago
Gwamnonin Arewa Na Kokarin Farfado Da Hadin Kan Yankin
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Jihar Gombe Ta Rattaba Hannu Kan Yarjejeniya Domin Gina Mayankar Dabbobi

1 week ago
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima
Noma Da Kiwo

Nau’ikan Amfanin Gona Da Ke Saurin Girma Cikin ‘Yan Watanni

1 week ago
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci A Sama Wa Manoma Masu Renon Tsirrai Rancen Kudi

2 weeks ago
Next Post
Firaministan Kasar Sin Zai Halarci Taron Summer Davos Na 2024

Firaministan Kasar Sin Zai Halarci Taron Summer Davos Na 2024

LABARAI MASU NASABA

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025
Kano

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.