• English
  • Business News
Wednesday, October 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manoman Kano Da Kaduna Za Su Amfana Da Shirin Yaki Da Cutar Tumatir

by Abubakar Abba
1 year ago
Kano

Wata gidauniyar shirin ‘ya’yan Itatuwa da ke gudanar da aikinta a Nijeriya, wato (HortiNigeria), ta wanzar da wani shiri nata na yakar cutar da ke lalata Tumatirin da manoma suka shuka, wanda a turance ake kira da suna ‘Tuta Absoluta’.

Gidauniyar ta wanzar da shirin ne a Jihohin Kano, Kaduna da kuma a sauran wasu jihohi uku, a karkashin shirin aikin noma na Kasar Jamus.

  • Yau Kotun Tarayya Za Ta Yanke Hukuncin Masarautar Kano
  • Daga Kai Kuɗin Fansa ‘Yan Bindiga Sun Kashe Shi A Dajin Kachiya

Har ila yau, ta yi hakan ne; domin sama wa manoma kayan aikin da za su yaki wannan cuta da ta jima shekara da shekaru tana addabar Tumatirin da manoma suka shuka.

Kazalika, Gidauniyar ta wanzar da wannan aikin ne ta hanyar yin hadaka da wasu masu ruwa da tsaki a wadannan jihohi da abin ya shafa.

A karkashin hadakar, manoma Tumatirin kimanin 60,000 ne za su amfana da sabbin kayan aikin na zamani, domin yakar cutar ta mai suna ‘Tuta absoluta’ a Jihohin Kano da Kaduna da kuma sauran wasu jihohi uku.

LABARAI MASU NASABA

Sharhi Kan Noman Agwaluma A Nijeriya

Gwamnatin Jihar Taraba Ta Ayyana Yi Wa Kasuwannin Sayar Da Dabbobi 9 Garanbawul

Jagoran aikin tare da fadakarwa na Gidauniyar, Malam Abdullahi Umar ya sanar da hakan ne a yayin taron wayar da kan manoman Tumatirin, wanda Gidanuniyar ta gudanar a gonakin wasu daga cikin manoman da cutar ta bulla a bangaren nasu.

Haka zalika, Gidauniyar ta yi taron ne a karkashin wani aikinta na kare kwarin da ke yi wa Tumatir din da aka shuka illa, wato (IPM).

A cewar Abdullahi, “Manoma Tumatirin sama da 60,000 da ke Jihohin Kano da Kaduna sauran wasu jihohi ne muke sa ran za su amfana da kayan aikin na zamani”.

Ya ci gaba da cewa, a karkashin aikin za a horar da manoma a yankuna daban-daban da ke fadin jihar.

“Mun jima muna karfafa wa manoman Tumatir gwiwa, musamman a kan cewa kada su sake su gaza wajen ci gaba da yin wannan noma na Tumatir, sakamakon bullar wannan cuta; domin kuwa muna da yakinin cewa; akwai yadda za a yi a iya magance cutar ba da jimawa ba, da yardar Allah”.

Kazalika, ya kuma sake bayyana cewa; muna nan muna ci gaba da kokarin sama wa wadannan manoman na Tumatir kasuwa, yadda za su rika sayar da shi cikin sauki tare kuma da samun kudaden shiga a cikin aljihunansu.

Shi ma a nasa bangaren, wani kwararre a cikin aikin; Mista Sabastine Agada Obaje ya yi nuni da cewa, yin gwajin na da matukar mahimmanci, domin kuwa ta hanyar yin gwajin ne za a iya taimaka wa manoman yin amfani da dabarun fasahar zamani wajen yin wannan noma na Tumatir.

Guda daga cikin manoman Tumatirin, Malam Uba Bello a nasa jawabin a wajen gwajin ya bayyana cewa, taron ya kara wa manoman Tumatirin kwarin gwaiwa, kan yadda za su tunkari kalubalen bullar cutar a gonakinsu.

A cewar tasa, sabuwar fasahar zamanin; tabbas za ta taimaka wa manoman Tumatir, kan yadda za su kara habaka sana’arsu ta wannan noma na Tumatir.

Ya kara da cewa, hakan zai kuma bai wa sauran manoman; musamman wadanda cutar ta sa suka dakatar da yin noman Timatirin samun damar dawowa cikin sana’ar gadan-gadan.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sharhi Kan Noman Agwaluma A Nijeriya
Noma Da Kiwo

Sharhi Kan Noman Agwaluma A Nijeriya

October 18, 2025
‘Yansanda Sun Cafke Ɓarayi 13 Tare Da Ƙwato Shanu 27 A Kaduna
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Jihar Taraba Ta Ayyana Yi Wa Kasuwannin Sayar Da Dabbobi 9 Garanbawul

October 18, 2025
Dalilin Bankin AfDB Na Yin Hadaka Da WFP Da IFPRI
Noma Da Kiwo

Dalilin Bankin AfDB Na Yin Hadaka Da WFP Da IFPRI

October 18, 2025
Next Post
Firaministan Kasar Sin Zai Halarci Taron Summer Davos Na 2024

Firaministan Kasar Sin Zai Halarci Taron Summer Davos Na 2024

LABARAI MASU NASABA

Babaganaru Ya Zama Sabon Kocin Kano Pillars

Babaganaru Ya Zama Sabon Kocin Kano Pillars

October 22, 2025
ADC Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Amfani da Zargin Juyin Mulki Wajen Yaƙar ‘Yan Adawa

ADC Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Amfani da Zargin Juyin Mulki Wajen Yaƙar ‘Yan Adawa

October 22, 2025
ASUU Ta Dakatar Da Yajin Aiki, Ta Bai Wa Gwamnati Wa’adin Wata Guda Don Biyan Buƙatunta

ASUU Ta Dakatar Da Yajin Aiki, Ta Bai Wa Gwamnati Wa’adin Wata Guda Don Biyan Buƙatunta

October 22, 2025
Rashin Abinci Mai Gina Jiki Barazana Ce Ga Lafiyar Al’umma – Gwamna Lawal

Rashin Abinci Mai Gina Jiki Barazana Ce Ga Lafiyar Al’umma – Gwamna Lawal

October 22, 2025
Majalisa Ta Amince Da Dokar Ɗaurin Rai Da Rai Ga Masu Yi Wa Ƙananan Yara Fyaɗe

Majalisa Ta Amince Da Dokar Ɗaurin Rai Da Rai Ga Masu Yi Wa Ƙananan Yara Fyaɗe

October 22, 2025
Gobara Ta Tashi A Kasuwar Alaba Da Ke Legas

Gobara Ta Tashi A Kasuwar Alaba Da Ke Legas

October 22, 2025
Gwamnoni Sun Yi Ta’aziyyar Mutanen Da Suka Rasu A Fashewar Tankar Mai A Neja

Gwamnoni Sun Yi Ta’aziyyar Mutanen Da Suka Rasu A Fashewar Tankar Mai A Neja

October 22, 2025
Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

October 21, 2025
Sin Ta Kammala Ginin Cibiyar Adana Bayanai Mai Amfani Da Karfin Iska A Karkashin Ruwa

Sin Ta Kammala Ginin Cibiyar Adana Bayanai Mai Amfani Da Karfin Iska A Karkashin Ruwa

October 21, 2025
Aikin Jinya Kyauta: Gwamnatin Zamfara Ta Kammala Zagaye Na 10 Na Kula Da Marasa Lafiya 3,447

Aikin Jinya Kyauta: Gwamnatin Zamfara Ta Kammala Zagaye Na 10 Na Kula Da Marasa Lafiya 3,447

October 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.