• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masana Sun Bayyana Matsalolin Fina-finan Hausa Da Hanyoyin Inganta Su

by Rabilu Sanusi Bena
10 months ago
in Nishadi
0
Masana Sun Bayyana Matsalolin Fina-finan Hausa Da Hanyoyin Inganta Su
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jami’ar Usmanu Danfodiyo da ke Sakkwato ta daura damarar dawo wa da kima da martabar fina-finan Hausa a idon duniya ta hanyar daidaita yadda ake shirya su domin su dace da al’adar Malam Bahaushe da zamantakewar magidanta a kasar Hausa.

  • Hajji 2024: Sarki Salman Na Saudiyya Ya Bai Wa Mahajjata Kyautar Al-Æ™ur’ani Mai Girma
  • Kwamitin Tsakiyar Jami’iyyar Kwaminis Ta Kasar Sin Ya Kira Taron Ba Mambobinsa Ba

A kan wannan ne jami’ar ta shirya taron masana da kwararru kan tasiri, matsaloli da alkiblar da ya kamata fina-finan su dosa, wanda aka gudanar ta manhajar zoom a kafar sadarwar intanet.

  • Rikicin Sarautar Kano: Yadda Gwamnatin Abba Ta Sauya Alkibla
  • A Watan Mayu Za A Bude Bikin Baje Kolin Motoci Na Afrika A Legas
  • Amurka: Sarkin Leken Asiri Na Neman Habaka Karfinta

Masana da masu ruwa da tsaki a farfajiyar ilimi sun tattauna tare da fitar da tsaki da tsakuwa a taron da aka yi wa taken “Fina-fiinan Hausa da Zamantakewar Magidanta: Ina Aka Dosa?” a karkashin jagorancin Farfesa Abdallah Uba Adamu na tsangayar sadarwa da ke jami’ar Bayero, Kano.

Shehunan Malaman jami’a, fitattun malaman addini da masu ruwa da tsaki a sha’anin fina-finan Hausa da suka tattauna a taron na yini daya su ne, Aliyu Muhammad Bunza wanda shi ne Farfesan al’adun Hausawa na farko a duniya, wanda ya gabatar da mukala mai taken “Zamantakewar Auren Hausawa da Al’adun Hausawa.” Haka ma Farfesa Ibrahim Aliyu Malumfashi ya gabatar da takarda mai taken “Samuwar Fina-finai da Canjin Manufarsu da Aka Samu.”

Fitaccen maruubuci, jarumi kuma mai shirya fina-finan Hausa, Ado Ahmed Gidan Dabino wanda shi ne shugaban kungiyar masu shirya fina-finan Hausa ta Jihar Kano (MOPPAN) ya gabatar da mukala mai taken ‘Manufa da Gudunmuwar Fina-finan Hausa ga Zamantakewar Hausawa.”

Labarai Masu Nasaba

Har Yanzu Da Bazar Mahaifina Nake Rawa -Hanafi Ibro

Rashin Hadin Kai Ke Dakile Ci Gaban Masana’antar Kannywood -Ayatullahi Tage

Ita kuwa Hadiza Salihu Koko daga kwalejin ilimi ta Shehu Shagari ta gabatar da kasida mai taken “Tasirin Fina-finan Hausa ga Zamantakewar Ma’aurata,” sai Sheikh Aminu Daurawa, shugaban Hukumar Hisbah Kano ya gabatar da takardar da ya rada wa sunan “Zamantakewar Ma’aurata a Addinin Musulunci Akasin yadda take a Fina-finan Hausa.”

Masanan sun cimma matsayar cewar fina-finan Hausa da aka fara shiryawa a

can baya an tsara su da gina su da haska su a akwatunan talabijin a bisa ga manufar fadakar da al’umma da ilmantar da su a kan shirye- shiryen ayyukan gwamnati akasin manufofin neman kudi na fina-finan wannan zamani.

“An lura da cewa al’umma suna taka muhimıniyar rawa wajen yaduwa da yawaitar kallon wadannan fina-finan Hausa da amfani da darussan da suke cikinsu masu alfanu da akasin haka.”

Tatttaunawa a taron an samu nasarar gano gurbatacciyar hanyar da masu shirya fina-finan suke ake yi wadda ke bukatar gyara domin kuwa sun cimma matsayar cewar, “fina-finan Hausa na wannan zamani sun saba wa al’adun Hausawa na asali baki daya na zamantakewa da kunya da sutura da tarbiyya, kuma suna haddasa matsalolin rashin fahimta da rabuwar aure atsakanin ma’aurata.”

Duka baya ga wannan kusoshin taron sun yi iyo da ninkaya tare da fito da shawarwari da hanyoyin da suke ganin su ne mafita wajen shirya fina-finan da Hausa da Hausawa za su yi alfahari da su a duniyar Malam Bahaushe, wadanda suka hada da: “shirya fina-finan Hausa wadanda suke

nuna darussan kyawawan al’adun zamantakewar auren Hausawa na tarbiyya da kunya da biyayya tsakanin ma’aurata da ‘ya’yansu kamar yadda wasannin kwaikwayo na da suka nuna.”

A cewarsu, “Bai kamata fina-finan Hausa na wannan zamani su mayar da hankali ga sana’ar neman kudi kawai ba, akasin fadakarwa da ilmantarwa da koyar da kyawawan al’adu da dabi’un Hausawa. Akwai bukatar magidanta da sauran al’ummar Hausawa su kauce wa kallon fina-finan Hausa na wannan zamani wadanda suka saba wa al’adu da addini da tarbiyyar Hausawa, wannan zai rage yaduwar fina-finan da amfani da miyagun darussan da ke cikinsu.”

Jagororin taron wadanda suka bayyana cewar za a ci gaba da gudanar da taron a nan gaba sun kuma ba da shawarar cewar, masana da manazarta su mayar da hankali sosai wajen rubutawa da shirya fina-finan Hausa masu koyar da kyawawan al’adu da dabi’un Hausawa, Gwamnati kuwa ta tallafa wajen daukar nauyin samar da su da yada su.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Adam ZangoAli NuhuFilmHausa FilmKannywood
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Sace Wayoyin Salula Sama Da Dubu 83 A Ingila A Cewar Rahotan ‘Yansandan Ƙasar

Next Post

HaÆ™ar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba: Nijeriya Na Asarar Naira Biliyan 9 Duk Shekara – Majalisa

Related

Har Yanzu Da Bazar Mahaifina Nake Rawa -Hanafi Ibro
Nishadi

Har Yanzu Da Bazar Mahaifina Nake Rawa -Hanafi Ibro

4 days ago
Rashin Hadin Kai Ke Dakile Ci Gaban Masana’antar Kannywood -Ayatullahi Tage
Nishadi

Rashin Hadin Kai Ke Dakile Ci Gaban Masana’antar Kannywood -Ayatullahi Tage

4 days ago
Ya Kamata Mata ‘Yan Fim Su Rike Mutuncin Kansu – Aisha Tafida Gombe
Nishadi

Ya Kamata Mata ‘Yan Fim Su Rike Mutuncin Kansu – Aisha Tafida Gombe

2 weeks ago
Saboda In Nuna Wa Duniya Asalin Al’adar Bahaushe Ya Sa Na Fara Fina-finan Turanci A Arewacin Nijeriya – Jammaje
Nishadi

Saboda In Nuna Wa Duniya Asalin Al’adar Bahaushe Ya Sa Na Fara Fina-finan Turanci A Arewacin Nijeriya – Jammaje

3 weeks ago
Daga Kaina An Gama Harkar Fim A Zuri’ata – Moda
Nishadi

Daga Kaina An Gama Harkar Fim A Zuri’ata – Moda

3 weeks ago
Rarara Zai Angwance Da Aisha Humaira Yau A Maiduguri
Manyan Labarai

Rarara Zai Angwance Da Aisha Humaira Yau A Maiduguri

3 weeks ago
Next Post
HaÆ™ar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba: Nijeriya Na Asarar Naira Biliyan 9 Duk Shekara – Majalisa

Haƙar Ma'adinai Ba Bisa Ƙa'ida Ba: Nijeriya Na Asarar Naira Biliyan 9 Duk Shekara - Majalisa

LABARAI MASU NASABA

Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Yi Karin Haske Kan Huldar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Yi Karin Haske Kan Huldar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

May 15, 2025
An Kaddamar Da Yankin Gwajin Aikin Gona Da Sin Ta Gina A Zimbabwe

An Kaddamar Da Yankin Gwajin Aikin Gona Da Sin Ta Gina A Zimbabwe

May 15, 2025
HOTO: Ofishin Tsohon Shugaban Kasa Shagari Bayan Shekara 42

HOTO: Ofishin Tsohon Shugaban Kasa Shagari Bayan Shekara 42

May 15, 2025
Shawarwarin Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Sun Haifar Da Managarcin Sakamako

Shawarwarin Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Sun Haifar Da Managarcin Sakamako

May 15, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta ÆŠaya A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta ÆŠaya A Kogi

May 15, 2025
Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

May 15, 2025
An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

May 15, 2025
NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

May 15, 2025
Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

May 15, 2025
Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

May 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.