• English
  • Business News
Friday, November 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masu Garkuwa Sun Saki Tsohon Sakataren NFF, Hakimin Kauyen Zira Da Wasu

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Bauchi

Rundunar ‘yan sandan Jihar Bauchi, ta tabbatar da cewa Hakimin kauyen Zira da ke Toro a Jihar Bauchi, Yahaya Saleh Abubakar da dansa, Habibu Yahaya sun kubuta daga hannun wadanda suka sace su.

Kazalika, shi ma tsohon sakataren hukumar kwallon kafa ta Nijeriya, (NFF), Alhaji Sani Ahmed Toro, da tsohon mataimakin kocin Super Eagles, Garba Yila gami da Alhaji Isa Jah da aka yi garkuwa da su, su ma sun samu ‘yancinsu.

  • Adamu Yaki Cewa Uffan Kan Mika Sunan Lawan Da Akpabio Ga INEC
  • Hajjin Bana: Sarkin Musulmi Ya Nemi Mahajjata Su Yi Wa Kasa Addu’ar Shugabanni Na Gari A 2023

Kakakin ‘yan sandan jihar Bauchi, SP Ahmed Mohammed Wakil, ne ya tabbatar da batun kubutar nasu a ranar Talata, ya ce, dukkaninsu su na cikin koshin lafiya kuma cikakken bayani zai zo daga baya.

Idan za a iya tunawa dai Sarkin na kauyen Zira, Malam Yahaya da dansa sun shiga hannun masu garkuwa ne a ranar Asabar da daddare.

Har wa yau, wakilinmu ya labarto cewa, tsohon sakataren hukumar kwallon kafa ta Nijeriya, Sani Toro da Yila hadi da Jah sun samu ‘yancinsu ne a ranar Talata wajajen karfe biyar na Asuba kamar yadda majiyoyi suka shaida.

LABARAI MASU NASABA

Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna

Jerin Gwarazan Taurarinmu!

Wani makusancin wadanda lamarin ya shafa, ya shaida cewar sun kubuta cikin koshin lafiya amma za a kaisu asibiti domin tabbatar da halin lafiyarsu.

An labarto cewa, Sani Toro da Yila tare da Jah an yi garkuwa da su ne lokacin da suke kan hanyarsu na dawowa daga Abuja zuwa Bauchi a daidai kan hanyar Akwanga zuwa jihar Nasarawa bayan sun halarci daurin auren dan tsohon Shugaban NFF, Aminun Maigari a Abuja ranar Asabar din da ta wuce.

Daga baya masu garkuwan sun bukaci kudin fansa har naira miliyan 150 kafin su sake wadanda suka kama. Sai dai babu wani cikakken bayanin nawa aka fiya kafin sake su zuwa yanzu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

APC Da Uba Sani Ba Su Lashe Zaben Gwamnan Kaduna Ba -PDP
Labarai

Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna

November 7, 2025
Jerin Gwarazan Taurarinmu!
Rahotonni

Jerin Gwarazan Taurarinmu!

November 7, 2025
‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri 4, Sun Ƙwato Makamai A Filato
Labarai

Zaben Kananan Hukumomi A Neja Ya Bar Baya Da Kura

November 7, 2025
Next Post
2023: Tinubu Ne Magaji Na, Cewar Buhari

2023: Tinubu Ne Magaji Na, Cewar Buhari

LABARAI MASU NASABA

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

November 7, 2025
An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

November 7, 2025
APC Da Uba Sani Ba Su Lashe Zaben Gwamnan Kaduna Ba -PDP

Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna

November 7, 2025
Kasar Sin Ta Musanta Zargin Da Wakilin Amurka Ya Yi Game Da Batun Sauyin Yanayi

Kasar Sin Ta Musanta Zargin Da Wakilin Amurka Ya Yi Game Da Batun Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Halarci Taron COP30 A Brazil

Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Halarci Taron COP30 A Brazil

November 7, 2025
Jerin Gwarazan Taurarinmu!

Jerin Gwarazan Taurarinmu!

November 7, 2025
‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri 4, Sun Ƙwato Makamai A Filato

Zaben Kananan Hukumomi A Neja Ya Bar Baya Da Kura

November 7, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Ɗauki Malaman Makaranta 500 Aiki

Gwamnatin Zamfara Ta Ɗauki Malaman Makaranta 500 Aiki

November 7, 2025
GORON JUMA’A

GORON JUMA’A

November 7, 2025
Majalisar Wakilai Ta Yi Tir Da Harin Da Aka Kai Wa Tawagar Ɗan Majalisar Neja

Majalisar Wakilai Ta Yi Tir Da Harin Da Aka Kai Wa Tawagar Ɗan Majalisar Neja

November 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.