• English
  • Business News
Wednesday, May 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masu Kiwon Kaji Da Manoman Rogo 700 Sun Samu Horo A Jihar Edo

by Abubakar Abba and Sulaiman
8 months ago
in Noma Da Kiwo
0
Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin tarayya ta horas da masu kiwon kajin gidan gona da kuma masu noman Rogo, kimanin su 700 a fannin aikin noma daban-daban a Jihar Edo.

 

A karkashin horaswar, masu kiwon kajin gidan gona 200 da kuma masu Rogo 500 ne suka amfana da horon.

  • Ministocin Da Ake Hasashen Za Su Tsallake Hisabin Tinubu
  • Rodri Ba Zai Sake Buga Kwallo A Wannan Kakar Ba Sakamakon Rauni

Jami’i a ma’aikatar aikin noma ta tarayya da ke jihar, Samuel Owoicho; a jawabinsa a wajen bayar da horon ya sanar da cewa, an taimakawa wadanda suka amfana da horon ne, domin inganta sana’arsu da kuma kara karfafa tattalin arzikin jihar.

 

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Ta Gabatar Da Wasu Shirye-shirye Na Bunƙasa Kiwon Shanu

Nazari Kan Dabarun Taimaka Wa Masu Kiwon Kifi Domin Jurewa Sauyin Yanayi

Horon, wanda aka gudanar da shi a garin Benin; babban birnin jihar, Owoicho ya sanar da cewa; horon ya nuna irin ci gaban da aka samar a jihar da kuma kasa baki-daya.

 

Haka zalika, ya bukaci a ci gaba da yin aiki kafada da kafada; domin tabbatar da dorewar fannin akin noman a wannan kasa baki-daya, musamman domin tabbatar da ganin cewa Jihar Edo ta ci gaba da kasancewa kan gaba a wannan fanni na aikin noma.

 

Owoicho ya kara da cewa, shirin bayar da horon; ya yi daidai da manufar ma’aikatar aikin noma ta tarayya na bunkasa fannin aikin noman tare da samar da wadataccen abinci da kuma inganta rayuwar kanannan manoma.

 

Jami’in ya ci gaba da cewa, shirin ya kuma nuna irin kokarin da Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu da Ministan Ma’aikatar Akin Noma da Samar da Wadataccen Abinci, Sanata Abubakar Kyari ke ci gaba da yi na bunkasa fannin da samar da wadataccen abinci a daukacin fadin kasar.

 

Haka zalika, ya kuma bayyana cewa; shirin zai kara samar da ilimi da kwarewa da kuma samar da karin kudaden shiga ga wadanda suka amfana da horon.

 

A cewar tasa, an samar da shirin tare da yin hadaka da sashen da ke kula da ayyukan malaman gona na ma’aikatar da kuma kamfanin ‘SANCT’ da ke cikin kasar.

 

Owoicho ya ce, babu shakka hadakar za ta taimaka wajen habaka fannin aikin noma tare da karfafafa fannin, musamman domin samar da wadataccen abinci da rage talauci da kuma kara habaka tattalin arzikin kasa baki-daya.

 

Haka zalika, ya kuma bukaci wadanda suka amfana da horon da su rungumi yin aiki ta hanyar yin noma da dabarun aikin noma na zamani da kuma yin aiki da ilimin zamani.

 

Sannan, ya kuma kwadaitar da su cewa, su ilimantar da sauran manoman da ba su samu damar amfana da wannan horo ba, su kuma shiga cikin kungiyoyin manoma domin samun tallafin aikin noma daga wurin  gwamnati.

 

Shi kuwa a nasa jawabin a wajen bayar da horon, babban sakatare a ma’aikatar aikin noma da samar da wadataccen abinci ta Jihar Edo, Peter Osagie; yaba wa gwamnatin ya yi kan horas da wadanda suka amfana da shirin.

 

Osagie ya kuma yi nuni da cewa, horon zai taimaka wajen ci gaba da habaka fannin aikin noma na jihar da kuma a kasa baki- daya, inda ya kara da cewa; wannan horon zai bai wa jihar karin damar zuba jari a fannin aikin noma na jihar.

 

Kazalika, ya bayar da tabbacin cewa; ma’aikatar aikin noma da samar da wadataccen abinci ta jihar, ba za ta yi kasa a guiwa ba wajen taimaka wa manoman jihar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaKiwon kajiTsadar kayayyakin abinci
ShareTweetSendShare
Previous Post

Mutane 9 Sun Rasu Sakamakon Kamuwa Da Cutar Kwalara A Yobe

Next Post

Babban Taron Samar Da Kayayyaki Na 2024 Ya Sa Kaimi Ga Kulla Ayyukan Hadin Gwiwa 718

Related

Gwamnatin Tarayya Ta Gabatar Da Wasu Shirye-shirye Na Bunƙasa Kiwon Shanu
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Gabatar Da Wasu Shirye-shirye Na Bunƙasa Kiwon Shanu

3 days ago
Nazari Kan Dabarun Taimaka Wa Masu Kiwon Kifi Domin Jurewa Sauyin Yanayi
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Dabarun Taimaka Wa Masu Kiwon Kifi Domin Jurewa Sauyin Yanayi

4 days ago
Noman 2025: Dole Ne Manoma Su Kiyaye Hasashen Hukumar NiMet
Noma Da Kiwo

Noman 2025: Dole Ne Manoma Su Kiyaye Hasashen Hukumar NiMet

4 days ago
Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma
Noma Da Kiwo

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

5 days ago
Nazari Kan Dabarun Gargajiya Domin Jawo Hankalin Zuma
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Dabarun Gargajiya Domin Jawo Hankalin Zuma

2 weeks ago
Ambaliya: Yankunan Da Ba Za Su Yi Noma A Kakar Bana Ba A Jihar Neja
Noma Da Kiwo

Ambaliya: Yankunan Da Ba Za Su Yi Noma A Kakar Bana Ba A Jihar Neja

2 weeks ago
Next Post
Babban Taron Samar Da Kayayyaki Na 2024 Ya Sa Kaimi Ga Kulla Ayyukan Hadin Gwiwa 718

Babban Taron Samar Da Kayayyaki Na 2024 Ya Sa Kaimi Ga Kulla Ayyukan Hadin Gwiwa 718

LABARAI MASU NASABA

Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

May 14, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

May 14, 2025
Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

May 14, 2025
Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

May 14, 2025
Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

May 14, 2025
‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi

May 14, 2025
Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa

Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa

May 14, 2025
Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

May 14, 2025
Ko Kanawa Za Su Yafe Wa Ganduje?

Kotu Ta Ce Za A Ci Gaba Da Shari’ar Ganduje Kan Zargin Aikata Rashawa A Kano

May 14, 2025
Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

May 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.