• English
  • Business News
Wednesday, October 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masu Kiwon Kaji Da Manoman Rogo 700 Sun Samu Horo A Jihar Edo

by Abubakar Abba and Sulaiman
1 year ago
Nijeriya

Gwamnatin tarayya ta horas da masu kiwon kajin gidan gona da kuma masu noman Rogo, kimanin su 700 a fannin aikin noma daban-daban a Jihar Edo.

 

A karkashin horaswar, masu kiwon kajin gidan gona 200 da kuma masu Rogo 500 ne suka amfana da horon.

  • Ministocin Da Ake Hasashen Za Su Tsallake Hisabin Tinubu
  • Rodri Ba Zai Sake Buga Kwallo A Wannan Kakar Ba Sakamakon Rauni

Jami’i a ma’aikatar aikin noma ta tarayya da ke jihar, Samuel Owoicho; a jawabinsa a wajen bayar da horon ya sanar da cewa, an taimakawa wadanda suka amfana da horon ne, domin inganta sana’arsu da kuma kara karfafa tattalin arzikin jihar.

 

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Osun Ta Horar Da Mata 500 Amfani Da Takin Gargajiya

Dalilin IFAD Na Zuba Naira Biliyan 16 A Fannin Noma A Benuwe

Horon, wanda aka gudanar da shi a garin Benin; babban birnin jihar, Owoicho ya sanar da cewa; horon ya nuna irin ci gaban da aka samar a jihar da kuma kasa baki-daya.

 

Haka zalika, ya bukaci a ci gaba da yin aiki kafada da kafada; domin tabbatar da dorewar fannin akin noman a wannan kasa baki-daya, musamman domin tabbatar da ganin cewa Jihar Edo ta ci gaba da kasancewa kan gaba a wannan fanni na aikin noma.

 

Owoicho ya kara da cewa, shirin bayar da horon; ya yi daidai da manufar ma’aikatar aikin noma ta tarayya na bunkasa fannin aikin noman tare da samar da wadataccen abinci da kuma inganta rayuwar kanannan manoma.

 

Jami’in ya ci gaba da cewa, shirin ya kuma nuna irin kokarin da Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu da Ministan Ma’aikatar Akin Noma da Samar da Wadataccen Abinci, Sanata Abubakar Kyari ke ci gaba da yi na bunkasa fannin da samar da wadataccen abinci a daukacin fadin kasar.

 

Haka zalika, ya kuma bayyana cewa; shirin zai kara samar da ilimi da kwarewa da kuma samar da karin kudaden shiga ga wadanda suka amfana da horon.

 

A cewar tasa, an samar da shirin tare da yin hadaka da sashen da ke kula da ayyukan malaman gona na ma’aikatar da kuma kamfanin ‘SANCT’ da ke cikin kasar.

 

Owoicho ya ce, babu shakka hadakar za ta taimaka wajen habaka fannin aikin noma tare da karfafafa fannin, musamman domin samar da wadataccen abinci da rage talauci da kuma kara habaka tattalin arzikin kasa baki-daya.

 

Haka zalika, ya kuma bukaci wadanda suka amfana da horon da su rungumi yin aiki ta hanyar yin noma da dabarun aikin noma na zamani da kuma yin aiki da ilimin zamani.

 

Sannan, ya kuma kwadaitar da su cewa, su ilimantar da sauran manoman da ba su samu damar amfana da wannan horo ba, su kuma shiga cikin kungiyoyin manoma domin samun tallafin aikin noma daga wurin  gwamnati.

 

Shi kuwa a nasa jawabin a wajen bayar da horon, babban sakatare a ma’aikatar aikin noma da samar da wadataccen abinci ta Jihar Edo, Peter Osagie; yaba wa gwamnatin ya yi kan horas da wadanda suka amfana da shirin.

 

Osagie ya kuma yi nuni da cewa, horon zai taimaka wajen ci gaba da habaka fannin aikin noma na jihar da kuma a kasa baki- daya, inda ya kara da cewa; wannan horon zai bai wa jihar karin damar zuba jari a fannin aikin noma na jihar.

 

Kazalika, ya bayar da tabbacin cewa; ma’aikatar aikin noma da samar da wadataccen abinci ta jihar, ba za ta yi kasa a guiwa ba wajen taimaka wa manoman jihar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwamnatin Osun Ta Horar Da Mata 500 Amfani Da Takin Gargajiya
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Osun Ta Horar Da Mata 500 Amfani Da Takin Gargajiya

October 11, 2025
Dalilin IFAD Na Zuba Naira Biliyan 16 A Fannin Noma A Benuwe
Noma Da Kiwo

Dalilin IFAD Na Zuba Naira Biliyan 16 A Fannin Noma A Benuwe

October 11, 2025
Yadda Haɗa Jinsin Shanu A Zamance Zai Ƙara Samar Da Madara
Noma Da Kiwo

Yadda Haɗa Jinsin Shanu A Zamance Zai Ƙara Samar Da Madara

October 11, 2025
Next Post
Babban Taron Samar Da Kayayyaki Na 2024 Ya Sa Kaimi Ga Kulla Ayyukan Hadin Gwiwa 718

Babban Taron Samar Da Kayayyaki Na 2024 Ya Sa Kaimi Ga Kulla Ayyukan Hadin Gwiwa 718

LABARAI MASU NASABA

Ma’aikatar Kasuwancin Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Shiga Tattaunawar Cinikayya Da Sahihiyar Zuciya

Ma’aikatar Kasuwancin Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Shiga Tattaunawar Cinikayya Da Sahihiyar Zuciya

October 14, 2025
Uwar Gidan Shugaban Sin Ta Ziyarci Wajen Nune-nunen Karfafawa Mata Gwiwa A Bangaren Fasahohin Zamani

Uwar Gidan Shugaban Sin Ta Ziyarci Wajen Nune-nunen Karfafawa Mata Gwiwa A Bangaren Fasahohin Zamani

October 14, 2025
Gidauniyar Sheikh Dahiru Bauchi Ta Tura Ɗalibai 117 Karatu Ƙasar Algeria 

Gidauniyar Sheikh Dahiru Bauchi Ta Tura Ɗalibai 117 Karatu Ƙasar Algeria 

October 14, 2025
Sin Tana Adawa Da Matakan Kuntatawa Na Amurka Kan Bangarorin Kasar Da Suka Shafi Harkokin Teku Da Jigila Da Ginin Jiragen Ruwa 

Sin Tana Adawa Da Matakan Kuntatawa Na Amurka Kan Bangarorin Kasar Da Suka Shafi Harkokin Teku Da Jigila Da Ginin Jiragen Ruwa 

October 14, 2025
Kotu

Kotu A Kano Ta Tsare Wani Mai Gidan Marayu Bisa Zargin Satar Yara Da Safararsu Zuwa Delta

October 14, 2025
Kowacce Mace Tauraruwa Ce A Kasar Sin

Kowacce Mace Tauraruwa Ce A Kasar Sin

October 14, 2025
Shawarwarin Sin Sun Bude Sabuwar Hanyar Bunkasa Ci Gaban Mata A Duniya

Shawarwarin Sin Sun Bude Sabuwar Hanyar Bunkasa Ci Gaban Mata A Duniya

October 14, 2025
Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Benin A Uyo

Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Benin A Uyo

October 14, 2025
Asuu

An Janye Wajibcin Samun Kiredit A Darasin Lissafi Ga Ɗaliban Fannin Zamantakewa Don Shiga Manyan Makarantu 

October 14, 2025
Al’ummun Kasashe Daban-Daban Sun Yabawa Shawarwarin Sin Dake Taimakawa Wajen Dunkulewa Don Hanzarta Ci Gaban Mata

Al’ummun Kasashe Daban-Daban Sun Yabawa Shawarwarin Sin Dake Taimakawa Wajen Dunkulewa Don Hanzarta Ci Gaban Mata

October 14, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.