ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masu Kiwon Kaji Da Manoman Rogo 700 Sun Samu Horo A Jihar Edo

by Abubakar Abba and Sulaiman
2 years ago
Nijeriya

Gwamnatin tarayya ta horas da masu kiwon kajin gidan gona da kuma masu noman Rogo, kimanin su 700 a fannin aikin noma daban-daban a Jihar Edo.

 

A karkashin horaswar, masu kiwon kajin gidan gona 200 da kuma masu Rogo 500 ne suka amfana da horon.

ADVERTISEMENT
  • Ministocin Da Ake Hasashen Za Su Tsallake Hisabin Tinubu
  • Rodri Ba Zai Sake Buga Kwallo A Wannan Kakar Ba Sakamakon Rauni

Jami’i a ma’aikatar aikin noma ta tarayya da ke jihar, Samuel Owoicho; a jawabinsa a wajen bayar da horon ya sanar da cewa, an taimakawa wadanda suka amfana da horon ne, domin inganta sana’arsu da kuma kara karfafa tattalin arzikin jihar.

 

LABARAI MASU NASABA

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

Horon, wanda aka gudanar da shi a garin Benin; babban birnin jihar, Owoicho ya sanar da cewa; horon ya nuna irin ci gaban da aka samar a jihar da kuma kasa baki-daya.

 

Haka zalika, ya bukaci a ci gaba da yin aiki kafada da kafada; domin tabbatar da dorewar fannin akin noman a wannan kasa baki-daya, musamman domin tabbatar da ganin cewa Jihar Edo ta ci gaba da kasancewa kan gaba a wannan fanni na aikin noma.

 

Owoicho ya kara da cewa, shirin bayar da horon; ya yi daidai da manufar ma’aikatar aikin noma ta tarayya na bunkasa fannin aikin noman tare da samar da wadataccen abinci da kuma inganta rayuwar kanannan manoma.

 

Jami’in ya ci gaba da cewa, shirin ya kuma nuna irin kokarin da Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu da Ministan Ma’aikatar Akin Noma da Samar da Wadataccen Abinci, Sanata Abubakar Kyari ke ci gaba da yi na bunkasa fannin da samar da wadataccen abinci a daukacin fadin kasar.

 

Haka zalika, ya kuma bayyana cewa; shirin zai kara samar da ilimi da kwarewa da kuma samar da karin kudaden shiga ga wadanda suka amfana da horon.

 

A cewar tasa, an samar da shirin tare da yin hadaka da sashen da ke kula da ayyukan malaman gona na ma’aikatar da kuma kamfanin ‘SANCT’ da ke cikin kasar.

 

Owoicho ya ce, babu shakka hadakar za ta taimaka wajen habaka fannin aikin noma tare da karfafafa fannin, musamman domin samar da wadataccen abinci da rage talauci da kuma kara habaka tattalin arzikin kasa baki-daya.

 

Haka zalika, ya kuma bukaci wadanda suka amfana da horon da su rungumi yin aiki ta hanyar yin noma da dabarun aikin noma na zamani da kuma yin aiki da ilimin zamani.

 

Sannan, ya kuma kwadaitar da su cewa, su ilimantar da sauran manoman da ba su samu damar amfana da wannan horo ba, su kuma shiga cikin kungiyoyin manoma domin samun tallafin aikin noma daga wurin  gwamnati.

 

Shi kuwa a nasa jawabin a wajen bayar da horon, babban sakatare a ma’aikatar aikin noma da samar da wadataccen abinci ta Jihar Edo, Peter Osagie; yaba wa gwamnatin ya yi kan horas da wadanda suka amfana da shirin.

 

Osagie ya kuma yi nuni da cewa, horon zai taimaka wajen ci gaba da habaka fannin aikin noma na jihar da kuma a kasa baki- daya, inda ya kara da cewa; wannan horon zai bai wa jihar karin damar zuba jari a fannin aikin noma na jihar.

 

Kazalika, ya bayar da tabbacin cewa; ma’aikatar aikin noma da samar da wadataccen abinci ta jihar, ba za ta yi kasa a guiwa ba wajen taimaka wa manoman jihar.

Kaji
Abubakar Abba
+ posts Bio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    “Mutunta Ƴancin Addinai Ita Ce Hanyar Wanzar Da Zaman Lafiya A Kaduna”
Kaji
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai
  • Sulaiman
    Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas
  • Sulaiman
    Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
  • Sulaiman
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu
Noma Da Kiwo

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

July 4, 2026
Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana
Noma Da Kiwo

Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana

July 3, 2026
Next Post
Babban Taron Samar Da Kayayyaki Na 2024 Ya Sa Kaimi Ga Kulla Ayyukan Hadin Gwiwa 718

Babban Taron Samar Da Kayayyaki Na 2024 Ya Sa Kaimi Ga Kulla Ayyukan Hadin Gwiwa 718

LABARAI MASU NASABA

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.