ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masu Kiwon Kaji Da Manoman Rogo 700 Sun Samu Horo A Jihar Edo

by Abubakar Abba and Sulaiman
2 years ago
Nijeriya

Gwamnatin tarayya ta horas da masu kiwon kajin gidan gona da kuma masu noman Rogo, kimanin su 700 a fannin aikin noma daban-daban a Jihar Edo.

 

A karkashin horaswar, masu kiwon kajin gidan gona 200 da kuma masu Rogo 500 ne suka amfana da horon.

ADVERTISEMENT
  • Ministocin Da Ake Hasashen Za Su Tsallake Hisabin Tinubu
  • Rodri Ba Zai Sake Buga Kwallo A Wannan Kakar Ba Sakamakon Rauni

Jami’i a ma’aikatar aikin noma ta tarayya da ke jihar, Samuel Owoicho; a jawabinsa a wajen bayar da horon ya sanar da cewa, an taimakawa wadanda suka amfana da horon ne, domin inganta sana’arsu da kuma kara karfafa tattalin arzikin jihar.

 

LABARAI MASU NASABA

Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

Horon, wanda aka gudanar da shi a garin Benin; babban birnin jihar, Owoicho ya sanar da cewa; horon ya nuna irin ci gaban da aka samar a jihar da kuma kasa baki-daya.

 

Haka zalika, ya bukaci a ci gaba da yin aiki kafada da kafada; domin tabbatar da dorewar fannin akin noman a wannan kasa baki-daya, musamman domin tabbatar da ganin cewa Jihar Edo ta ci gaba da kasancewa kan gaba a wannan fanni na aikin noma.

 

Owoicho ya kara da cewa, shirin bayar da horon; ya yi daidai da manufar ma’aikatar aikin noma ta tarayya na bunkasa fannin aikin noman tare da samar da wadataccen abinci da kuma inganta rayuwar kanannan manoma.

 

Jami’in ya ci gaba da cewa, shirin ya kuma nuna irin kokarin da Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu da Ministan Ma’aikatar Akin Noma da Samar da Wadataccen Abinci, Sanata Abubakar Kyari ke ci gaba da yi na bunkasa fannin da samar da wadataccen abinci a daukacin fadin kasar.

 

Haka zalika, ya kuma bayyana cewa; shirin zai kara samar da ilimi da kwarewa da kuma samar da karin kudaden shiga ga wadanda suka amfana da horon.

 

A cewar tasa, an samar da shirin tare da yin hadaka da sashen da ke kula da ayyukan malaman gona na ma’aikatar da kuma kamfanin ‘SANCT’ da ke cikin kasar.

 

Owoicho ya ce, babu shakka hadakar za ta taimaka wajen habaka fannin aikin noma tare da karfafafa fannin, musamman domin samar da wadataccen abinci da rage talauci da kuma kara habaka tattalin arzikin kasa baki-daya.

 

Haka zalika, ya kuma bukaci wadanda suka amfana da horon da su rungumi yin aiki ta hanyar yin noma da dabarun aikin noma na zamani da kuma yin aiki da ilimin zamani.

 

Sannan, ya kuma kwadaitar da su cewa, su ilimantar da sauran manoman da ba su samu damar amfana da wannan horo ba, su kuma shiga cikin kungiyoyin manoma domin samun tallafin aikin noma daga wurin  gwamnati.

 

Shi kuwa a nasa jawabin a wajen bayar da horon, babban sakatare a ma’aikatar aikin noma da samar da wadataccen abinci ta Jihar Edo, Peter Osagie; yaba wa gwamnatin ya yi kan horas da wadanda suka amfana da shirin.

 

Osagie ya kuma yi nuni da cewa, horon zai taimaka wajen ci gaba da habaka fannin aikin noma na jihar da kuma a kasa baki- daya, inda ya kara da cewa; wannan horon zai bai wa jihar karin damar zuba jari a fannin aikin noma na jihar.

 

Kazalika, ya bayar da tabbacin cewa; ma’aikatar aikin noma da samar da wadataccen abinci ta jihar, ba za ta yi kasa a guiwa ba wajen taimaka wa manoman jihar.

Kaji
Abubakar Abba
+ posts Bio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Yadda Bikin Girke-girke Ya Karfafa Alaka Tsakanin Musulmai Da Kiristoci A Kaduna
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood
Kaji
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

MASU ALAKA

Abin Da Ya Sa Gidauniyar NADF Da Bankin Manoma Suka Yi Haḍaka
Noma Da Kiwo

Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma

August 1, 2026
Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya
Noma Da Kiwo

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

July 18, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Next Post
Babban Taron Samar Da Kayayyaki Na 2024 Ya Sa Kaimi Ga Kulla Ayyukan Hadin Gwiwa 718

Babban Taron Samar Da Kayayyaki Na 2024 Ya Sa Kaimi Ga Kulla Ayyukan Hadin Gwiwa 718

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.