Dan wasan tsakiya na Manchester City, Rodri ba zai buga sauran wasannin kakar wasa ta bana ba sakamakon raunin da ya ji a kafarsa.
Dan wasan mai shekaru 28, ya samu rauni ne a wasan da suka tashi 2 da 2 da Arsenal a ranar Lahadi a gasar Firimiyar Ingila, bayan da sun yi karo da Thomas Partey.
- Mace-mace Sakamakon Ibtila’o’in Da Ke Faruwa A Arewa
- Ya Kamata Gwamnati Ta Kula Da Marayun Da Aka Bari Sanadin Mummunan Hatsarin Motar Lere – Sharif Danlami
Kocin Manchester City Pep Guardiola ya ce yanzu an yi wa Rodri tiyata a gwiwarsa kuma ba zai buga sauran wasannin wannan kakar ba.
“An yi masa tiyata a safiyar yau saboda haka wannan kakar ta kare a wajensa sai dai zai buga kakar gaba,” in ji Guardiola.
Guardiola ya ce Rodri ya kasance dan wasan da ba za a iya maye gurbinsa ba a lokacin gasar cin kofin bara, inda City ta doke Arsenal kuma ta lashe kofin gasar Firimiya karo na hudu a jere.
A cikin wasanni biyar da Rodri bai samu bugawa a kakar wasannin bara ba City ta sha kashi a hudu daga cikinsu,hakan ya sa ake ganin City za ta sha wahala kafin ta murmure daga raunin da Rodri ya samu.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp