ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matar Aure Ta Bukaci Kotu Ta Raba Aurenta Da Mijinta Saboda Yawan Jima’i

by Sadiq
4 years ago
Jima'i

Wata matar aure mai suna Zainab Yunusa ta roki kotun shari’a musulunci da ke zamanta a Magajin Gari a Jihar Kaduna, da ta raba aurenta da mijinta, Alhaji Ali Garba, bisa yawan bukatar jima’i da yake yi.

Mai shigar da karar ta shaida wa kotu a ranar Laraba cewa Garba, ya kan bukaci yin jima’i da ita ko da tana jinin haila da kuma lokacin azumin Ramadan.

  • Matsalar Karancin Iskar Gas Na Addabar Turai Yayin Da Amurka Ke Kulla Makarkashiya
  • IMMOWA Ta Horar Da Mata Da Yaran Jami’an Shige Da Fice Sana’o’i  

Ta ce sun shafe shekara guda a matsayin ma’aurata, inda ta kara da cewa ta koma gidan iyayenta saboda girman abun.

ADVERTISEMENT

Mai shigar da karar ta bayyana cewa, a zaman da suke tare, Garba yakan dawo gida da rana lokacin da take jinin al’ada domin saduwa da ita, wanda hakan ya sabawa koyarwar addinin Musulunci.

“Lokacin azumin Ramadan, yakan dawo gida da rana ya nemi yin jima’i, duk lokacin da na ki, sai ya yi fushi.

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

“Kuma idan na tambaye shi abinci, yawanci ya kan amsa cewa in je in hadu da saurayina ya ciyar da ni.

“Bai taba yarda da ni ba har bai taba barin wani daga ‘yan uwana maza ko mata su ziyarce ni ba,” kamar yadda ta shaida wa kotu.

Matar ta ce ta gudu daga gidan aurenta, saboda ba za ta iya gamsar da mijinta ba sakamakon tsananin sha’awa da yake da shi.

Don haka, ta roki kotu da ta raba auren, domin ba ta shirya saba wa Allah ba akan mijinta ba.

Sai dai mijin ya musanta zargin karar da matar tasa ta shigar a gaban kotu.

Garba, ya shaida wa kotun ta bakin lauyansa, Mista M.A Sambo, cewa mahaifiyar matarsa ​​ta je gidansa ba ya nan, ta kwashe kaya tare da sayar da kadarorinsa, kafin ta tafi da diyarta.

Ya ce mahaifiyar ta yi alkawarin mayar da duk abin da suka kwaso daga gidansa a wani zaman sulhu da aka yi.

Ya lissafa abubawan da aka kwashe masa da suka hada da kujeru na Naira 100,000, talabijin, firij guda biyu, faranti na Naira 35,000 da sauran kayayyakin kicin, kafet da katifa ta Naira 15,000.

Garba ya roki kotu da ta duba bukatarsa ​​ta a mayar masa da kadarorinsa a matsayin sharadin amincewa da bukatar sakin matar tasa.

Alkalin kotun, Murtala Nasir, bayan ya saurari dukkan bangarorin biyu, ya umarci mai kara da ta zo kotu tare da mahaifiyarta a zaman a gaba.

Ya dage sauraron karar zuwa ranar 27 ga watan Satumba domin ci gaba da sauraren karar.

MASU ALAKA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

June 3, 2026
Next Post
’Yan Bindiga Sun Saki Mutane 43 Da Suka Sace A Masallaci, Sun Kashe Daya A Zamfara

’Yan Bindiga Sun Saki Mutane 43 Da Suka Sace A Masallaci, Sun Kashe Daya A Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.