ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matar Aure Ta Bukaci Kotu Ta Raba Aurenta Da Mijinta Saboda Yawan Jima’i

by Sadiq
4 years ago
Jima'i

Wata matar aure mai suna Zainab Yunusa ta roki kotun shari’a musulunci da ke zamanta a Magajin Gari a Jihar Kaduna, da ta raba aurenta da mijinta, Alhaji Ali Garba, bisa yawan bukatar jima’i da yake yi.

Mai shigar da karar ta shaida wa kotu a ranar Laraba cewa Garba, ya kan bukaci yin jima’i da ita ko da tana jinin haila da kuma lokacin azumin Ramadan.

  • Matsalar Karancin Iskar Gas Na Addabar Turai Yayin Da Amurka Ke Kulla Makarkashiya
  • IMMOWA Ta Horar Da Mata Da Yaran Jami’an Shige Da Fice Sana’o’i  

Ta ce sun shafe shekara guda a matsayin ma’aurata, inda ta kara da cewa ta koma gidan iyayenta saboda girman abun.

ADVERTISEMENT

Mai shigar da karar ta bayyana cewa, a zaman da suke tare, Garba yakan dawo gida da rana lokacin da take jinin al’ada domin saduwa da ita, wanda hakan ya sabawa koyarwar addinin Musulunci.

“Lokacin azumin Ramadan, yakan dawo gida da rana ya nemi yin jima’i, duk lokacin da na ki, sai ya yi fushi.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

“Kuma idan na tambaye shi abinci, yawanci ya kan amsa cewa in je in hadu da saurayina ya ciyar da ni.

“Bai taba yarda da ni ba har bai taba barin wani daga ‘yan uwana maza ko mata su ziyarce ni ba,” kamar yadda ta shaida wa kotu.

Matar ta ce ta gudu daga gidan aurenta, saboda ba za ta iya gamsar da mijinta ba sakamakon tsananin sha’awa da yake da shi.

Don haka, ta roki kotu da ta raba auren, domin ba ta shirya saba wa Allah ba akan mijinta ba.

Sai dai mijin ya musanta zargin karar da matar tasa ta shigar a gaban kotu.

Garba, ya shaida wa kotun ta bakin lauyansa, Mista M.A Sambo, cewa mahaifiyar matarsa ​​ta je gidansa ba ya nan, ta kwashe kaya tare da sayar da kadarorinsa, kafin ta tafi da diyarta.

Ya ce mahaifiyar ta yi alkawarin mayar da duk abin da suka kwaso daga gidansa a wani zaman sulhu da aka yi.

Ya lissafa abubawan da aka kwashe masa da suka hada da kujeru na Naira 100,000, talabijin, firij guda biyu, faranti na Naira 35,000 da sauran kayayyakin kicin, kafet da katifa ta Naira 15,000.

Garba ya roki kotu da ta duba bukatarsa ​​ta a mayar masa da kadarorinsa a matsayin sharadin amincewa da bukatar sakin matar tasa.

Alkalin kotun, Murtala Nasir, bayan ya saurari dukkan bangarorin biyu, ya umarci mai kara da ta zo kotu tare da mahaifiyarta a zaman a gaba.

Ya dage sauraron karar zuwa ranar 27 ga watan Satumba domin ci gaba da sauraren karar.

MASU ALAKA

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan
Manyan Labarai

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Next Post
’Yan Bindiga Sun Saki Mutane 43 Da Suka Sace A Masallaci, Sun Kashe Daya A Zamfara

’Yan Bindiga Sun Saki Mutane 43 Da Suka Sace A Masallaci, Sun Kashe Daya A Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.