ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matar Aure Ta Bukaci Kotu Ta Raba Aurenta Da Mijinta Saboda Yawan Jima’i

by Sadiq
4 years ago
Jima'i

Wata matar aure mai suna Zainab Yunusa ta roki kotun shari’a musulunci da ke zamanta a Magajin Gari a Jihar Kaduna, da ta raba aurenta da mijinta, Alhaji Ali Garba, bisa yawan bukatar jima’i da yake yi.

Mai shigar da karar ta shaida wa kotu a ranar Laraba cewa Garba, ya kan bukaci yin jima’i da ita ko da tana jinin haila da kuma lokacin azumin Ramadan.

  • Matsalar Karancin Iskar Gas Na Addabar Turai Yayin Da Amurka Ke Kulla Makarkashiya
  • IMMOWA Ta Horar Da Mata Da Yaran Jami’an Shige Da Fice Sana’o’i  

Ta ce sun shafe shekara guda a matsayin ma’aurata, inda ta kara da cewa ta koma gidan iyayenta saboda girman abun.

ADVERTISEMENT

Mai shigar da karar ta bayyana cewa, a zaman da suke tare, Garba yakan dawo gida da rana lokacin da take jinin al’ada domin saduwa da ita, wanda hakan ya sabawa koyarwar addinin Musulunci.

“Lokacin azumin Ramadan, yakan dawo gida da rana ya nemi yin jima’i, duk lokacin da na ki, sai ya yi fushi.

LABARAI MASU NASABA

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

“Kuma idan na tambaye shi abinci, yawanci ya kan amsa cewa in je in hadu da saurayina ya ciyar da ni.

“Bai taba yarda da ni ba har bai taba barin wani daga ‘yan uwana maza ko mata su ziyarce ni ba,” kamar yadda ta shaida wa kotu.

Matar ta ce ta gudu daga gidan aurenta, saboda ba za ta iya gamsar da mijinta ba sakamakon tsananin sha’awa da yake da shi.

Don haka, ta roki kotu da ta raba auren, domin ba ta shirya saba wa Allah ba akan mijinta ba.

Sai dai mijin ya musanta zargin karar da matar tasa ta shigar a gaban kotu.

Garba, ya shaida wa kotun ta bakin lauyansa, Mista M.A Sambo, cewa mahaifiyar matarsa ​​ta je gidansa ba ya nan, ta kwashe kaya tare da sayar da kadarorinsa, kafin ta tafi da diyarta.

Ya ce mahaifiyar ta yi alkawarin mayar da duk abin da suka kwaso daga gidansa a wani zaman sulhu da aka yi.

Ya lissafa abubawan da aka kwashe masa da suka hada da kujeru na Naira 100,000, talabijin, firij guda biyu, faranti na Naira 35,000 da sauran kayayyakin kicin, kafet da katifa ta Naira 15,000.

Garba ya roki kotu da ta duba bukatarsa ​​ta a mayar masa da kadarorinsa a matsayin sharadin amincewa da bukatar sakin matar tasa.

Alkalin kotun, Murtala Nasir, bayan ya saurari dukkan bangarorin biyu, ya umarci mai kara da ta zo kotu tare da mahaifiyarta a zaman a gaba.

Ya dage sauraron karar zuwa ranar 27 ga watan Satumba domin ci gaba da sauraren karar.

MASU ALAKA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Next Post
’Yan Bindiga Sun Saki Mutane 43 Da Suka Sace A Masallaci, Sun Kashe Daya A Zamfara

’Yan Bindiga Sun Saki Mutane 43 Da Suka Sace A Masallaci, Sun Kashe Daya A Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.