• English
  • Business News
Saturday, November 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matsalar Ciwon Kwakwalwa A Gidajen Yarin Kasar Nan

by Leadership Hausa and Sulaiman
2 months ago
Fyade

A kwanan baya ne, Hukumar Kula da Gidajen Gayran Hali ta Kasa ta fitar da wani rahoton da ke nuna cewa, akalla masu zama a gidan Jarun guda 8,246 a daukacin fadin kasar nan ke fuskantar matsalar Ciwon Kwakwalwa.

Mataimakin Kwantirola Janar na Hukumar da ke kula da lafiiyar ayyukan bangaren kiwon lafiya Dakta Glory Essien ne ya bayyana haka, a yayin wani sauraron bayanai kan binciken da ake yi wa Hukumar na zarge-zargen cin hanci da rashawa da yin amfani da karfin iko ba baisa ka’ida ba da ganawa masu zaman gidan kaso azaba da kuma sauran nau’ukan cin zarafi.

A cewarsa, duk da irin daukin kudi da ake samar wa domin magance matsalar, amma lamarin na ciwon kwakwalar a gidan yari na ci gaba da karuwa, hakan na neman ya gagari Kundila.

Hukumar Kula da Lafiya ta Duniya wato WHO, ta jannyo wasu daga cikin jerin nau’ukan ciwon Kwakwalwa da suka hadda da, jirkewar dabi’ar wadanda suka samu matsalar da shiga cikin yanayin damauwa da kangin talauci da fuskantar tashe-tashen hankula da sauransu.

Koda yake dai, a Nijeriya babu wasu cikakkun alkamun da ake da su, na masu fama da larurar, amma wasu kwararrun a fannin kiwon lafiya a kasar, sun kiyasata cewa, ‘yan Nijeriya akalla miliyan 40 ne, ke fuskantar matsalar.

LABARAI MASU NASABA

Batun Yin Afuwa Ga ‘Yan Yankin Ogoni Huɗu

Burin ‘Yan Nijeriya Bai Cika Ba Tun Bayan Samun ‘Yancin Kai

Wannan ya nuna yadda a halin yanzu irin yanayin da masu zaman a gidajen Yarin ke ci gaba da zama a gidajen, musamman saboda rashin kulawa da su yadda ya kamata.

Sai dai, Dakta Essien ya dora laifin kan rashin samu ‘yanci ga masu zaman gidan Jarun din.

Gidajen Yarin kasar guda 246 yau shekaru 100 ke nan da gina su, wadanda akasarinsu, duk sun tsufa, inda kuma dakunan da ‘yan jarun din ke kwana, ba su da wani sararin da masu zaman jarun din za su iya wani watayawa.

A cewar Essien, jimlar masu zama a gidan jarun ciki har da wadanda aka ajiye da suke jiran Shari’a, sun kai 81,122, wanda a ka’ida kamata ya yi su kai 50,153.

Kazalika, daga cikin wannan adadin, jimlar masu zaman jarun a a daukacin gidajen Yarin da ke kasar nan guda 3,688 a yanzu suke jiran a yanke masu hukuncin kisa.

Wannan yawan na masu zaman jarun din, ya kai kashi 136.7, wanda haka ke nuna karancin kudi na tafiyar da gidajen da kuma rashin kayan aiki.

A kwanan baya mun wallafa wani rahoton a wannan shafin kan irin yadda ake nuna rashin adalaci da tauye wa masu zaman jarun ‘yancinsu.

Muna sane da irin yadda ake fuskantar jinkiri wajen yanke wa wadanda ake zargi hukunci, musamman na yanke hukuncin kisa, inda wadannan matsaloli, suke kara haddasa karuwar cunkso a gidajen yarin kasa.

A ra’ayin wannan Jaridar, wannan jinkirin na yanke hukuncin, da kuma irn yanayin da gidajen Yarin hakan na kara haddasa wa masu zaman jarun din matsalar hauka.

Akasarin su da suke jiran hukunci, tuni, sun fitar da rai daga samun ‘yanci, saboda ci gaba da tsare su, da ake yi.

Dokar kasar ta bai wa duk wani da aka kama da aikata wani laifi, damar daukar Lauya, domin samun beli, amma saoda son rai, da nuna karfi, ba su samun hakan.

Akasarin wadanda ake tsare da su a gidajen Yarin, sun yi ikirarin cewa, sai sun bai wa ‘yansanda cin hanci, sannan suke ke gabatar da su a gaban kuliya ko kuma a wasu lokutan, su sake su.

Damuwar mu, saboda irin lalacewar da gidajen Yarin kasa ke ciki, kusan zai yi matukar wuya, a iya gyarasu, duk da cewa dokar kasar, ta bayar da damar a gyarasu.

Bugu da kari, dokar shekarar 2019 da ta kafa gidan Yarin kasar, ta bayar da damar a mayar da su zuwa na zamani, yadda za su yi daidai da na duniya, wanda kuma dokar, ta jaddda kula da ‘yancin masu zaman jarun

Ra’ayinmu a nan shi ne, akwai matukar bukatar a magance cunkson da ake da shi, a daukacin gidajen Yarin kasar da kuma yadda ake tauye hakkin masu zama a gidajen, wanda ya zama wajbi a dauki matakan magance wadannan matsalolin, ta hanyar samar da sauye-sauye da dabaru, masu dogon zango.

Samar da ingantattun kayan aiki a gidajen zai taimaka wajen rage cunkoson da gidajen ke ci gaba da fuskanta, wanda za a iya samun hakan ne kawai, idan Gwamnatin ta kara yawan kudaden da ake ware wa gidajen domin su tafi daidai da irin na kasashen duniya.

Kazalika, samar da sauye-sauye a bangaren shari’a da kuma kafa kotunan tafi da gidanka na yanke ‘yan kananan laifuka, hakan zai taimaka wajen yanke hukunci a kan lokaci, musamman domin a dakile yawan samun cunkoso a gidajen.

Kare ‘yancin masu zaman gidan na da matukar mahimmanci kuma ya kamata a samar da wasu kungiyoyi masu zaman kansu da za su rinka zuwa gidajen domin sanya a ido kan irin yanayin da gidajen suke ciki da kuma gudanar da bincike, kan batun cin zarafin masu zaman jarun.

Ya kuma kamata a rinka shirya wa ma’aikatan gidajen horo musamman kan yadda za su rinka bin ka’idar kiyaye hakkokin masu zaman gidajen.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tinubu
Ra'ayinmu

Batun Yin Afuwa Ga ‘Yan Yankin Ogoni Huɗu

October 17, 2025
Yari
Ra'ayinmu

Burin ‘Yan Nijeriya Bai Cika Ba Tun Bayan Samun ‘Yancin Kai

October 10, 2025
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna
Ra'ayinmu

A Daina Gaggawar Murnar Samun Nasara Kan Ta’addanci A Nijeriya

August 29, 2025
Next Post
Mun Tara Kuɗi Sama Da Naira Miliyan 170 Na Fatun Layya – Sheikh Bala Lau 

Mun Tara Kuɗi Sama Da Naira Miliyan 170 Na Fatun Layya - Sheikh Bala Lau 

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Shirin Shugaba Tinubu Na ‘Renewed Hope’ Zai Karfafa Wa Manoma Gwiwa – Oyebanji

November 7, 2025
Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

November 7, 2025
Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

November 7, 2025
An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

November 7, 2025
Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

November 7, 2025
An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

November 7, 2025
APC Da Uba Sani Ba Su Lashe Zaben Gwamnan Kaduna Ba -PDP

Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna

November 7, 2025
Kasar Sin Ta Musanta Zargin Da Wakilin Amurka Ya Yi Game Da Batun Sauyin Yanayi

Kasar Sin Ta Musanta Zargin Da Wakilin Amurka Ya Yi Game Da Batun Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Halarci Taron COP30 A Brazil

Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Halarci Taron COP30 A Brazil

November 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.