• English
  • Business News
Friday, September 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Miƙa Mulki Daga Buhari Zuwa Tinubu: Abubuwan Da Suka Fi Jan Hankali

by Sulaiman
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Miƙa Mulki Daga Buhari Zuwa Tinubu: Abubuwan Da Suka Fi Jan Hankali
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Lokutan mika mulki na shugaban kasa lokuta ne na farin ciki a tsakanin al’umma sannan kuma lokuta ne mafi damuwa ga masu mika madafun iko. Lokutan mika mulki suna da wata alaka da damuwa da dimauta mai cike da dimbin rikici da kalubale.

Shugaban kasa mai barin gado, ba wai kawai zai cigaba da jagorancin kasa ba ne, dole ne ya fara shirya mika ragamar shugabancin ga sabon shugaba mai jiran gado da tawagarsa.

  • Hilda Bassey: ‘Yar Nijeriya Da Ta Kafa Tarihi A Fannin Girki A Duniya

A wannan lokaci, shugaba mai barin gado bai da wata cikakkiyar karfin guiwa sabida kusan duk al’amuran mulki da kwarjini a wurin Jama’a ya fara komawa wurin shugaba mai jiran gado.

Shugaban kasa da tawagarsa za su fara fuskantar halin da ake ji na rabuwa da mulki musamman na fara rasa abokai masu son alaka da makusanta kujerar shugaban kasa.

Ziyarar ban-girma da aka saba kaiwa shugaban kasa mai ci a sannu a hankali sai ta fara gushewa ta koma bangaren zababben shugaban kasa.

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

Wadannan halaye na siyasa – fara janyewa daga shugaba mai barin gado zuwa mai jiran gado, a karshe dai duk za su dusashe da zarar an mika mulki. Wannan rana ta bikin mika mulki ga shugaban kasa a Nijeriya, za a yi ta a ranar 29 ga watan Mayu, 2023.

A Nijeriya, daga 1999 zuwa yau, an yi bukukuwan mika mulki sau shida, amma sau uku daga shugaban kasa zuwa wani shugaba – Obasanjo zuwa ‘Yar’Adua/ Jonathan, Jonathan zuwa Buhari, yanzu kuma Buhari zuwa Tinubu.

Akwai nau’o’i biyu ne na mika mulki na shugaban kasa: akwai daga shugaban kasa zuwa shugaban kasa a karkashin jam’iyya daya sai kuma wanda ba a karkashin jam’iyya daya ba suka fito. Duka wadannan nau’ikan a Nijeriya mun dandanasu bisa tsarin dimokuradiyya, wannan alama ce na Nijeriya tana kan turbar Dimokuradiyya.

Kowane canji yana haifar da kalubale da firgici daban-daban da kiyayya. Amma kuma a wannan sauyin na halin yanzu akwai aminci sosai fiye da yadda aka saba ganin sabani tsakanin zababbe da mai barin gado – Shugaba Buhari na jam’iyyar APC zai mikawa zababben shugaban kasa Asiwaju Bola Ahmed Tinubu na jam’iyyar APC mulki.

Wannan shi ne bangare mafi sauki na wannan mika mulki na shugaban kasa da ke cike da cece-kuce kuma ya raba ra’ayoyin jama’a zuwa mabambantan ra’ayi – wasu suna kira da a dage rantsar da shugaban kasa sabida dalilai daban-daban na zato, wasu kuma suna nan kan cewa, babu wani dalili da zai hana rantsar da zababben shugaban kasa, bisa ga ka’ida da tanade-tanaden kundin tsarin mulkin mu. Duk suna da hakkin ra’ayinsu amma dole ne dokar kasa ta yi rinjaje.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Guguwa Ta Lalata Gidaje 200 A Jihar Bauchi

Next Post

Rikicin Addini: An Sanya Dokar Hana Fita A Jihar Taraba

Related

NNPP
Manyan Labarai

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

6 hours ago
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna
Manyan Labarai

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

8 hours ago
Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis
Manyan Labarai

Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

14 hours ago
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

15 hours ago
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB
Manyan Labarai

Sojoji Sun Cafke Babban Kwamandan IPOB

18 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

1 day ago
Next Post
Rikicin Addini: An Sanya Dokar Hana Fita A Jihar Taraba

Rikicin Addini: An Sanya Dokar Hana Fita A Jihar Taraba

LABARAI MASU NASABA

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

September 18, 2025
Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

September 18, 2025
Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

September 18, 2025
Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

September 18, 2025
Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

September 18, 2025
Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

September 18, 2025
An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

September 18, 2025
NNPP

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

September 18, 2025
Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

September 18, 2025
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

September 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.