• English
  • Business News
Friday, June 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Miƙa Mulki Daga Buhari Zuwa Tinubu: Abubuwan Da Suka Fi Jan Hankali

by Sulaiman
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Miƙa Mulki Daga Buhari Zuwa Tinubu: Abubuwan Da Suka Fi Jan Hankali
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Lokutan mika mulki na shugaban kasa lokuta ne na farin ciki a tsakanin al’umma sannan kuma lokuta ne mafi damuwa ga masu mika madafun iko. Lokutan mika mulki suna da wata alaka da damuwa da dimauta mai cike da dimbin rikici da kalubale.

Shugaban kasa mai barin gado, ba wai kawai zai cigaba da jagorancin kasa ba ne, dole ne ya fara shirya mika ragamar shugabancin ga sabon shugaba mai jiran gado da tawagarsa.

  • Hilda Bassey: ‘Yar Nijeriya Da Ta Kafa Tarihi A Fannin Girki A Duniya

A wannan lokaci, shugaba mai barin gado bai da wata cikakkiyar karfin guiwa sabida kusan duk al’amuran mulki da kwarjini a wurin Jama’a ya fara komawa wurin shugaba mai jiran gado.

Shugaban kasa da tawagarsa za su fara fuskantar halin da ake ji na rabuwa da mulki musamman na fara rasa abokai masu son alaka da makusanta kujerar shugaban kasa.

Ziyarar ban-girma da aka saba kaiwa shugaban kasa mai ci a sannu a hankali sai ta fara gushewa ta koma bangaren zababben shugaban kasa.

Labarai Masu Nasaba

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

Wadannan halaye na siyasa – fara janyewa daga shugaba mai barin gado zuwa mai jiran gado, a karshe dai duk za su dusashe da zarar an mika mulki. Wannan rana ta bikin mika mulki ga shugaban kasa a Nijeriya, za a yi ta a ranar 29 ga watan Mayu, 2023.

A Nijeriya, daga 1999 zuwa yau, an yi bukukuwan mika mulki sau shida, amma sau uku daga shugaban kasa zuwa wani shugaba – Obasanjo zuwa ‘Yar’Adua/ Jonathan, Jonathan zuwa Buhari, yanzu kuma Buhari zuwa Tinubu.

Akwai nau’o’i biyu ne na mika mulki na shugaban kasa: akwai daga shugaban kasa zuwa shugaban kasa a karkashin jam’iyya daya sai kuma wanda ba a karkashin jam’iyya daya ba suka fito. Duka wadannan nau’ikan a Nijeriya mun dandanasu bisa tsarin dimokuradiyya, wannan alama ce na Nijeriya tana kan turbar Dimokuradiyya.

Kowane canji yana haifar da kalubale da firgici daban-daban da kiyayya. Amma kuma a wannan sauyin na halin yanzu akwai aminci sosai fiye da yadda aka saba ganin sabani tsakanin zababbe da mai barin gado – Shugaba Buhari na jam’iyyar APC zai mikawa zababben shugaban kasa Asiwaju Bola Ahmed Tinubu na jam’iyyar APC mulki.

Wannan shi ne bangare mafi sauki na wannan mika mulki na shugaban kasa da ke cike da cece-kuce kuma ya raba ra’ayoyin jama’a zuwa mabambantan ra’ayi – wasu suna kira da a dage rantsar da shugaban kasa sabida dalilai daban-daban na zato, wasu kuma suna nan kan cewa, babu wani dalili da zai hana rantsar da zababben shugaban kasa, bisa ga ka’ida da tanade-tanaden kundin tsarin mulkin mu. Duk suna da hakkin ra’ayinsu amma dole ne dokar kasa ta yi rinjaje.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Guguwa Ta Lalata Gidaje 200 A Jihar Bauchi

Next Post

Rikicin Addini: An Sanya Dokar Hana Fita A Jihar Taraba

Related

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano
Manyan Labarai

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

1 hour ago
Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

10 hours ago
Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi
Manyan Labarai

Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi

12 hours ago
Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa
Manyan Labarai

Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa

13 hours ago
Hukumar kashe gobara
Manyan Labarai

An Samu Asarar Dukiya ta Miliyan ₦273, Tare Da Mutuwar Mutum 5 A Kano – Hukuma

1 day ago
Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 
Manyan Labarai

Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 

1 day ago
Next Post
Rikicin Addini: An Sanya Dokar Hana Fita A Jihar Taraba

Rikicin Addini: An Sanya Dokar Hana Fita A Jihar Taraba

LABARAI MASU NASABA

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

June 6, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

June 6, 2025
Sallar Layya: Gwamnan Zamfara Ya Buƙaci Musulmin Su Tuna Da Muhimmancin Sadaukarwa Da Halin Ƙwarai

Sallar Layya: Gwamnan Zamfara Ya Buƙaci Musulmin Su Tuna Da Muhimmancin Sadaukarwa Da Halin Ƙwarai

June 6, 2025
Tsohon Babban Alƙalin Nijeriya  Mohammed Uwais Ya Rasu Ya Shekara 89

Tsohon Babban Alƙalin Nijeriya  Mohammed Uwais Ya Rasu Ya Shekara 89

June 6, 2025
Wajibi A Mayar Da Hankali Kan ‘Yancin Yara

Wajibi A Mayar Da Hankali Kan ‘Yancin Yara

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.