ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, November 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ministan Ma’adanai Ya Bukaci Masu Harkar Ma’adanai A Jihar Nasarawa Su Zauna Lafiya

by Leadership Hausa
1 year ago
ma'adan

Ministan ma’aikatar bunkasar harkokin ma’adanaiwta tarayya (ministry of Solid Minerals Development), Dele Alake ya yi kira na musamman ga dukkan hukumomi masu harkokin haka da sarrafa ma’adanai musamman a karamar hukumar Nasarawa da jihar baki daya su zauna lafiya da juna ayayin da suke gudanar da harkokinsu.

Alake ya yi kiran ne jim kadan bayan wani zama na musamman da ya yi da Gwamnan Jihar Nasarawa Injiniya Abdullahi Sule da wasu mukarraban gwamnatinsa a gidan gwamnati da ke birnin Lafiya, fadar jihar ranar Litinin.

  • NNPC Ya Ƙara Farashin Man Fetur Zuwa 855 Kan Kowace Lita 

Dele Alake wanda darakta janar na sashin ma’aikatar da ake kira “Cadastry” a turance ya wakilce shi ya ce ba shakka kiran ya zama wajibi idan aka yi la’akari da mahimmancin zaman lafiya a tsakanin masu harkokin ma’adanan don ta haka ne kawai za su samu ci gaba da bunkasar harkokin nasu a dukkan matakai.
A cewarsa, dole ne hukumomin daban-daban a jihar su hada kai su koma teburin sasantawa don warware duka rigingimu da ke tsakanin su kasancewar sai da zaman lafiya da fahimtar juna tsakanin su kadai hukumomi masu zuba jari daga gida Nijeriya da ƙasashen waje za su samu damar ci gaba da zuba jari a harkokin ma’adanan karamar hukumar ta Nasarawa da jihar baki daya.

ADVERTISEMENT

Ministan Dele Alake ya kuma yaba wa gwamnan jihar Injiniya Abdullahi Sule dangane da abin da ya bayyana a matsayin gagarumin gudunmawa da gwamnatin sa ke bayarwa a kai-a kai wajen bunkasar harkokin ma’adanan da safarar su a dukkam matakai inda ya ce tabbas hakan ne ma ya aza jihar a mataki na gaba-gaba a ƙasar nan a fannin ci gaba da bunkasar ma’adanan a yanzu haka.

Daganan sai ministan ya kuma yi amfani da wannan damar inda ya sanar cewa tuni ma’aikatarsa ta yanke shawarar gudanar da wani gagarumin taro a watan Nuwambar shekarar 2024 kuma ma’aikatar ta zabi jihar Nasarawa a matsayin wajen da za a gudanar da taron bisa la’akari da gagarumin gudunmawa da take bayarwa wajen bunkasar harkokin ma’adananta da ta ƙasa baki daya.
Da yake jawabi, Gwamna Abdullahi Sule, bayan ya gode wa bakin nasa dangane da ziyarar da kuma zabar jihar tasa a matsayin inda za a gudanar da babban taron ma’adanan ya kuma tabbatar masu da cewa a shirye gwamnatinsa take ta ci gaba da bai wa fannin fifiko kasancewar Allah ya albarkaci jihar da dinbin ma’adanai iri daban-daban.
Sauran manyan baki da suka yi jawabi a yayin ziyarar har da kwamishinan ma’aikatar ma’adanai da albarkatun kasa na jihar ta Nasarawa, Honorabu Kwanta Yakubu inda suka yi fatan alheri da samun nasarorin da ake fatan gani a fannin na ma’adanai.

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025

Kuratan Sojoji 1,196 Aka Yaye A Makarantar Horar Da Sojoji Ta Zariya

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025
Labaran Kasuwanci

Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025

July 12, 2025
Kuratan Sojoji 1,196 Aka Yaye A Makarantar Horar Da Sojoji Ta Zariya
Labaran Kasuwanci

Kuratan Sojoji 1,196 Aka Yaye A Makarantar Horar Da Sojoji Ta Zariya

June 21, 2025
Za Mu Tabbatar Da Samun Kyakkyawar Alaka Da Gwamnati Don Ci Gaban Kasuwar Kofar Ruwa – ‘Yanleman
Labaran Kasuwanci

Za Mu Tabbatar Da Samun Kyakkyawar Alaka Da Gwamnati Don Ci Gaban Kasuwar Kofar Ruwa – ‘Yanleman

January 11, 2025
Next Post
Dangote Ya Ceto Nijeriya Daga Durƙushewa – Otedola

Dangote Ya Ceto Nijeriya Daga Durƙushewa - Otedola

LABARAI MASU NASABA

Wasu Mahara Sun Kashe Mata 2, Tare Da da Ƙona Gidansu A Tudun Yola

Wasu Mahara Sun Kashe Mata 2, Tare Da da Ƙona Gidansu A Tudun Yola

November 15, 2025
Rundunar Sojin Nijeriya Ta Bayyana Dalilan Hana Jami’anta Auren ‘Yan Kasashen Waje

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Bayyana Dalilan Hana Jami’anta Auren ‘Yan Kasashen Waje

November 15, 2025
Fashi Da Makami: An Yanke Wa ’Yan Nijeriya Hudu Mazauna Birtaniya Hukuncin Daurin Shekara 55 A Gidan Yari

Fashi Da Makami: An Yanke Wa ’Yan Nijeriya Hudu Mazauna Birtaniya Hukuncin Daurin Shekara 55 A Gidan Yari

November 15, 2025
Shugaban APC Na Kano Ya Nemi Afuwa Daga Al’ummar Fagge Kan Kalamansa

Shugaban APC Na Kano Ya Nemi Afuwa Daga Al’ummar Fagge Kan Kalamansa

November 15, 2025
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Cafke Wani Da Ake Zargin Dan Ta’adda Ne A Jihar Kebbi

November 15, 2025
Bangaren Sauka Na Kumbon Shenzhou-21 Ya Iso Doron Duniya

Bangaren Sauka Na Kumbon Shenzhou-21 Ya Iso Doron Duniya

November 14, 2025
NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026

NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026

November 14, 2025
NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano

NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano

November 14, 2025
Gwamnan Gombe Ya Gabatar Da Naira Biliyan 535.69 A Matsayin Kasafin 2026

Gwamnan Gombe Ya Gabatar Da Naira Biliyan 535.69 A Matsayin Kasafin 2026

November 14, 2025
Sin Za Ta Mayar Da Martani Idan Har Japan Ta Aiwatar Da Matakin Da Bai Dace Ba

Sin Za Ta Mayar Da Martani Idan Har Japan Ta Aiwatar Da Matakin Da Bai Dace Ba

November 14, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.