ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, November 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ministar Jin Kai Ta Raba Wa Mata 3,500 Tallafin Kudi A Gombe

by Najib Sani a Gombe
3 years ago
Tallafi

Ministar jin kai da walwalar al’umma, Sadiya Farouk, a ranar Talata ta kaddamar da rabon tallafin kudi ga mata sama da 3,500 a jihar Gombe.

Ministar ta bada tallafin ne karkashin shirin taimakon mutane da suke fama da matsanancin talauci da ake wa lakabi ‘Conditional Cash Transfer’ (CCT) a turance.

  • NBC Ta Ci Tarar Trust TV Tarar Miliyan 5 Kan Yada Ayyukan ‘Yan Bindiga 
  • An Harbe Dogarin Mataimakin Sufeton ‘Yansanda Yayin Wani Harin ‘Yan Bindiga A Kaduna

Da take jawabi a yayin kaddamar da rabon kudin tallafin a babban zauren taro na gidan gwamnatin Gombe, ministar ta bayyana cewa wadanda aka zaba don cin gajiyar tallafin za su karbi Naira 20,000 kowannensu.

ADVERTISEMENT

A cewarta, shirin tallafin na CCT na daya daga cikin abubuwan da shugaban kasa Muhammadu Buhari ya kirkiro karkashin tsarin rage talauci da inganta walwalar al’ummar kasa, wanda yake mika taimako ga mutanen da suka fi fama da talauci musamman a yankunan karkara.

Ta yi ikirarin cewa gwamnatin Buhari ta gaji talauci wajen kaso saba’in daga gwamnatocin baya, shi yasa ta mayar da hankali wajen samar da hanyoyin rage wahalhalun jama’a.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Aka Gudanar Da Taron Tuna Shekara 20 Da Rasuwar Dr Bala Usman

Gamayyar kungiyoyin Seyi Tinubu (STSG) Na Shirin Gangamin Taronta Na Kasa

“Wannan shirin yana daga wadanda suka fi ko wanne tasiri a nahiyar Afrika wajen rage fatara a tsakanin al’umma da kuma janyo hadaka daga kasashen duniya don inganta rayuwar al’umma”. Inji ministar.

Sadiya ta kara da cewa ita da kanta ta ga mutanen da a baya suke cikin mawuyacin hali amma yanzu sun canza sakamakon wannan tallafin da aka basu a sassa daban-daban na kasar nan.

Shi ma da yake jawabi, gwamnan jihar Gombe, Inuwa Yahaya wanda mataimakin gwamnan, Manasseh Jatau, ya wakilce shi ya yaba wa gwamnatin tarayya bisa tallafin yana mai cewa tallafin zai kara wa wadanda suka ci gajiyarsa hanyoyin samun kudin shiga.

Ya kuma shawarci wadanda suka karbi tallafin da su yi amfani da kudin a kasuwanci da sana’oi da za su janyo musu riba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Yadda Aka Gudanar Da Taron Tuna Shekara 20 Da Rasuwar Dr Bala Usman
Kananan Labarai

Yadda Aka Gudanar Da Taron Tuna Shekara 20 Da Rasuwar Dr Bala Usman

September 26, 2025
Gamayyar kungiyoyin Seyi Tinubu (STSG) Na Shirin Gangamin Taronta Na Kasa
Kananan Labarai

Gamayyar kungiyoyin Seyi Tinubu (STSG) Na Shirin Gangamin Taronta Na Kasa

May 23, 2025
Gwamnati Ta Ware Wata 14 Don Kammala Aikin Hanyar Abuja Zuwa Zariya
Kananan Labarai

Gwamnati Ta Ware Wata 14 Don Kammala Aikin Hanyar Abuja Zuwa Zariya

April 18, 2025
Next Post
Ana Zaton Wuta A Makera…

Ana Zaton Wuta A Makera...

LABARAI MASU NASABA

Bangaren Sauka Na Kumbon Shenzhou-21 Ya Iso Doron Duniya

Bangaren Sauka Na Kumbon Shenzhou-21 Ya Iso Doron Duniya

November 14, 2025
NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026

NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026

November 14, 2025
NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano

NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano

November 14, 2025
Gwamnan Gombe Ya Gabatar Da Naira Biliyan 535.69 A Matsayin Kasafin 2026

Gwamnan Gombe Ya Gabatar Da Naira Biliyan 535.69 A Matsayin Kasafin 2026

November 14, 2025
Sin Za Ta Mayar Da Martani Idan Har Japan Ta Aiwatar Da Matakin Da Bai Dace Ba

Sin Za Ta Mayar Da Martani Idan Har Japan Ta Aiwatar Da Matakin Da Bai Dace Ba

November 14, 2025
Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani

Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani

November 14, 2025
Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Saman Yaki Na Sichuan Ya Fara Gwajin Sufuri A Karon Farko

Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Saman Yaki Na Sichuan Ya Fara Gwajin Sufuri A Karon Farko

November 14, 2025
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima

Dalilin Asusun NADF Na Yin Hadaka Da Gwamnatin Jihar Jigawa

November 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Sarkin Thailand

Xi Jinping Ya Gana Da Sarkin Thailand

November 14, 2025
BUK Za Ta Kafa Cibiyar Horas da Aikin Jarida da Sabbin Kafofin Sadarwa Na Zamani

BUK Za Ta Kafa Cibiyar Horas da Aikin Jarida da Sabbin Kafofin Sadarwa Na Zamani

November 14, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.