• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ministar Jin Kai Ta Raba Wa Mata 3,500 Tallafin Kudi A Gombe

by Najib Sani a Gombe
3 years ago
in Kananan Labarai
0
Ministar Jin Kai Ta Raba Wa Mata 3,500 Tallafin Kudi A Gombe
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministar jin kai da walwalar al’umma, Sadiya Farouk, a ranar Talata ta kaddamar da rabon tallafin kudi ga mata sama da 3,500 a jihar Gombe.

Ministar ta bada tallafin ne karkashin shirin taimakon mutane da suke fama da matsanancin talauci da ake wa lakabi ‘Conditional Cash Transfer’ (CCT) a turance.

  • NBC Ta Ci Tarar Trust TV Tarar Miliyan 5 Kan Yada Ayyukan ‘Yan Bindiga 
  • An Harbe Dogarin Mataimakin Sufeton ‘Yansanda Yayin Wani Harin ‘Yan Bindiga A Kaduna

Da take jawabi a yayin kaddamar da rabon kudin tallafin a babban zauren taro na gidan gwamnatin Gombe, ministar ta bayyana cewa wadanda aka zaba don cin gajiyar tallafin za su karbi Naira 20,000 kowannensu.

A cewarta, shirin tallafin na CCT na daya daga cikin abubuwan da shugaban kasa Muhammadu Buhari ya kirkiro karkashin tsarin rage talauci da inganta walwalar al’ummar kasa, wanda yake mika taimako ga mutanen da suka fi fama da talauci musamman a yankunan karkara.

Ta yi ikirarin cewa gwamnatin Buhari ta gaji talauci wajen kaso saba’in daga gwamnatocin baya, shi yasa ta mayar da hankali wajen samar da hanyoyin rage wahalhalun jama’a.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnati Ta Ware Wata 14 Don Kammala Aikin Hanyar Abuja Zuwa Zariya

Ƙarin Harajin Amurka Zai Illata Tattalin Arziƙin Duniya

“Wannan shirin yana daga wadanda suka fi ko wanne tasiri a nahiyar Afrika wajen rage fatara a tsakanin al’umma da kuma janyo hadaka daga kasashen duniya don inganta rayuwar al’umma”. Inji ministar.

Sadiya ta kara da cewa ita da kanta ta ga mutanen da a baya suke cikin mawuyacin hali amma yanzu sun canza sakamakon wannan tallafin da aka basu a sassa daban-daban na kasar nan.

Shi ma da yake jawabi, gwamnan jihar Gombe, Inuwa Yahaya wanda mataimakin gwamnan, Manasseh Jatau, ya wakilce shi ya yaba wa gwamnatin tarayya bisa tallafin yana mai cewa tallafin zai kara wa wadanda suka ci gajiyarsa hanyoyin samun kudin shiga.

Ya kuma shawarci wadanda suka karbi tallafin da su yi amfani da kudin a kasuwanci da sana’oi da za su janyo musu riba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: FataraGombeGwamnatin TarayyaMataMinistar AgajiRage TalauciSadiya Umar FaroulTallafi
ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makarantar Tarayya, Sun Kashe Mahaifin Wakilin NAN A Kaduna 

Next Post

Ana Zaton Wuta A Makera…

Related

Gwamnati Ta Ware Wata 14 Don Kammala Aikin Hanyar Abuja Zuwa Zariya
Kananan Labarai

Gwamnati Ta Ware Wata 14 Don Kammala Aikin Hanyar Abuja Zuwa Zariya

4 weeks ago
Ƙarin Harajin Amurka Zai Illata Tattalin Arziƙin Duniya
Kananan Labarai

Ƙarin Harajin Amurka Zai Illata Tattalin Arziƙin Duniya

1 month ago
Gwamnati Ta Amince Da Bai Wa Jami’o’i 11 Masu Zaman Kansu Lasisi
Kananan Labarai

Gwamnati Ta Amince Da Bai Wa Jami’o’i 11 Masu Zaman Kansu Lasisi

2 months ago
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Kananan Labarai

Nijeriya Za Ta Ci Gajiyar Dala Tiriliyan 7 A Tsarin Kasuwancin Musulunci Na Duniya

8 months ago
Gwamna Dauda Ya Ƙaddamar Da Aikin Sake Gina Asibitin Talata Mafara
Labarai

Gwamna Dauda Ya Ƙaddamar Da Aikin Sake Gina Asibitin Talata Mafara

8 months ago
Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Tallafawa Majinyata 1000 Da Abinci Da KuÉ—i
Kananan Labarai

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Tallafawa Majinyata 1000 Da Abinci Da KuÉ—i

8 months ago
Next Post
Ana Zaton Wuta A Makera…

Ana Zaton Wuta A Makera...

LABARAI MASU NASABA

Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

May 15, 2025
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don YaÆ™ar ‘Yan Ta’adda

May 15, 2025
ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

May 15, 2025
‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

May 15, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

May 15, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

May 15, 2025
UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.