• English
  • Business News
Friday, June 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ministocin Da Ake Hasashen Za Su Tsallake Hisabin Tinubu

by Yusuf Shuaibu and Sulaiman
9 months ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Tinubu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A yayin da ake ci gaba da sauye-sauyen tsare-tsare a Nijeriya, alamu sun nuna cewa nan ba da jimawa ba Shugaba kasa Bola Tinubu zai yi wa majalisar ministocinsa garambawul domin kawar da ministocin da ba su yi aiki ba.

 

Wata majiya mai tushe wacce ta nemi a sakaya sunanta a fadar shugaban kasa ta bayyana hakan a kwanan nan.

  • MOF: Kasar Sin A Shirye Take Ta Zurfafa Hadin Gwiwa Da Dukkan Bangarorin GDI
  • Rodri Ba Zai Sake Buga Kwallo A Wannan Kakar Ba Sakamakon Rauni

A cewar majiyar, shugaban kasar ya damu matuka da yadda akasarin ‘yan ministocinsa ba su tallafa wa gwamnatinsa wajen cike burin ajandarsa ta sabunta fata, sannan akwai matsananciyar matsin lamba na yin garambawul ga majalisar ministocinsa.

Majiyar ta ce za a iya sauke wasu daga cikin ministocin, yayin da wasu kuma za a iya sauya musu wuraren aikinsu na asali, wasu kuma a bar su a inda suke aiki domin samun kyakkyawan shugabanci.

Labarai Masu Nasaba

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya

Majiyar ta bayyana cewa ba yi wa majalisar ministocin garambawul tun da farko ba saboda tunuanin siyasar zaben 2027.

Majiyar ta ci gaba da cewa, “Shugaban kasa ya damu matuka saboda yawancin ‘yan majalisar ministocinsa ba su da wani shiri na tafiyar da ajandarsa ta sabunta fata. An dai sha matsin lamba a kan ya yi wa majalisar ministoci garambawul, amma saboda wasu dalilai na siyasa ya ki yin hakan. Yawancin ministocin manyan masu ruwa da tsaki ne a siyasance wadanda ba a iya yin watsi da tasirinsu ba. Tasirin siyasar ne zai taimaka wa shugaban kasa a 2027 domin ya aiwatar da wa’adinsa na biyu. Don haka, gwargwadon yadda shugaban kasa zai so ya nada masu basira domin tafiyar da manufofinsa wajen cimma burinsa, akwai kuma bukatar yin wasu dubaru na siyasa. Saboda haka, kwazon ministocin ba shi kadai shugaban kasa yake la’akari da shi ba wajen yanke shawara.”

A kan ministocin da ake ganin za a tsige idan shugaban kasa ya yanke shawarar yin garambawul a majalisar ministocinsa, wata majiya ta ce, “Ba zai iya gaya muku adadin wadanda za a cire ba. Amma akwai yuwuwar canza wa wasu wuraren ayyuka.

“Duk da haka, akwai wasu daga cikinsu wadanda lamarin ba zai shafan su ba. Wasu kwazansu ne zai cece su, yayin da wasu kuma za su tsira ne sakamakon tasirinsu a siyasa da dangantakarsu da shugaban kasa.

“Wadanda ake ganin za su sha sun hada da Ministan Babban Birnin Tarayya (FCT), Nyesom Wike; ministan lafiya da walwalar jama’a, Farfesa Ali Pate; ministan sufurin jiragen sama da raya sararin samaniya, Festus Keyamo, ministan harkokin cikin gida, Olubunmi Tunji-Ojo; ministan kudi, Wale Edun; ministan kasafin kudi da tsare-tsaren kasa, Atiku Bagudu da ministan ayyuka, Dabe Umahi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaGwamnatin APCMinistoci
ShareTweetSendShare
Previous Post

MOF: Kasar Sin A Shirye Take Ta Zurfafa Hadin Gwiwa Da Dukkan Bangarorin GDI

Next Post

Yawan Cinikayyar Waje Ta Sin A Fannin Hajoji Da Bayar Da Hidimomi Ya Karu Da Kaso 4% A Agusta

Related

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai
Tambarin Dimokuradiyya

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

2 weeks ago
APC
Tambarin Dimokuradiyya

Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya

2 weeks ago
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

3 weeks ago
‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

4 weeks ago
Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

1 month ago
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Adawa Na Cacakar APC A Yankin Arewa Maso Yamma Bisa Goyon Bayan Tazarcen Tinubu

1 month ago
Next Post
Yawan Cinikayyar Waje Ta Sin A Fannin Hajoji Da Bayar Da Hidimomi Ya Karu Da Kaso 4% A Agusta

Yawan Cinikayyar Waje Ta Sin A Fannin Hajoji Da Bayar Da Hidimomi Ya Karu Da Kaso 4% A Agusta

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Yadda NATO Ta Yi Amfani Da Ita A Matsayin Dalilin Neman Fadada

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Yadda NATO Ta Yi Amfani Da Ita A Matsayin Dalilin Neman Fadada

June 26, 2025
Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi

Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi

June 26, 2025
An Yi Bikin Nune-Nunen Kayan Al’adu Na Murnar Cika Shekaru 55 Da Kulla Huldar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Italiya A Rome

An Yi Bikin Nune-Nunen Kayan Al’adu Na Murnar Cika Shekaru 55 Da Kulla Huldar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Italiya A Rome

June 26, 2025
NNPC Ta Gaza Halartar Zaman Binciken Majalisa Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210

NNPC Ta Gaza Halartar Zaman Binciken Majalisa Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210

June 26, 2025
Tattalin Arzikin Sin Na Ci Gaba Da Ba Da Gudunmuwa Ga Habakar Tattalin Arzikin Duniya

Tattalin Arzikin Sin Na Ci Gaba Da Ba Da Gudunmuwa Ga Habakar Tattalin Arzikin Duniya

June 26, 2025
Kashim Shettima Ya Tafi Habasha Ziyarar Aiki

Kashim Shettima Ya Tafi Habasha Ziyarar Aiki

June 26, 2025
Afirka CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwa Kan Kiwon Lafiya Da Kasar Sin

Afirka CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwa Kan Kiwon Lafiya Da Kasar Sin

June 26, 2025
Sabbin Dokokin Haraji Za Su Fara Aiki A Janairun 2026 — Adedeji

Sabbin Dokokin Haraji Za Su Fara Aiki A Janairun 2026 — Adedeji

June 26, 2025
An Watsa Shirin Talabijin Mai Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” A Italiya

An Watsa Shirin Talabijin Mai Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” A Italiya

June 26, 2025
Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…

Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…

June 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.