• English
  • Business News
Friday, June 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ministocin Da Ake Hasashen Za Su Tsallake Hisabin Tinubu

by Yusuf Shuaibu and Sulaiman
8 months ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Tinubu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A yayin da ake ci gaba da sauye-sauyen tsare-tsare a Nijeriya, alamu sun nuna cewa nan ba da jimawa ba Shugaba kasa Bola Tinubu zai yi wa majalisar ministocinsa garambawul domin kawar da ministocin da ba su yi aiki ba.

 

Wata majiya mai tushe wacce ta nemi a sakaya sunanta a fadar shugaban kasa ta bayyana hakan a kwanan nan.

  • MOF: Kasar Sin A Shirye Take Ta Zurfafa Hadin Gwiwa Da Dukkan Bangarorin GDI
  • Rodri Ba Zai Sake Buga Kwallo A Wannan Kakar Ba Sakamakon Rauni

A cewar majiyar, shugaban kasar ya damu matuka da yadda akasarin ‘yan ministocinsa ba su tallafa wa gwamnatinsa wajen cike burin ajandarsa ta sabunta fata, sannan akwai matsananciyar matsin lamba na yin garambawul ga majalisar ministocinsa.

Majiyar ta ce za a iya sauke wasu daga cikin ministocin, yayin da wasu kuma za a iya sauya musu wuraren aikinsu na asali, wasu kuma a bar su a inda suke aiki domin samun kyakkyawan shugabanci.

Labarai Masu Nasaba

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

Majiyar ta bayyana cewa ba yi wa majalisar ministocin garambawul tun da farko ba saboda tunuanin siyasar zaben 2027.

Majiyar ta ci gaba da cewa, “Shugaban kasa ya damu matuka saboda yawancin ‘yan majalisar ministocinsa ba su da wani shiri na tafiyar da ajandarsa ta sabunta fata. An dai sha matsin lamba a kan ya yi wa majalisar ministoci garambawul, amma saboda wasu dalilai na siyasa ya ki yin hakan. Yawancin ministocin manyan masu ruwa da tsaki ne a siyasance wadanda ba a iya yin watsi da tasirinsu ba. Tasirin siyasar ne zai taimaka wa shugaban kasa a 2027 domin ya aiwatar da wa’adinsa na biyu. Don haka, gwargwadon yadda shugaban kasa zai so ya nada masu basira domin tafiyar da manufofinsa wajen cimma burinsa, akwai kuma bukatar yin wasu dubaru na siyasa. Saboda haka, kwazon ministocin ba shi kadai shugaban kasa yake la’akari da shi ba wajen yanke shawara.”

A kan ministocin da ake ganin za a tsige idan shugaban kasa ya yanke shawarar yin garambawul a majalisar ministocinsa, wata majiya ta ce, “Ba zai iya gaya muku adadin wadanda za a cire ba. Amma akwai yuwuwar canza wa wasu wuraren ayyuka.

“Duk da haka, akwai wasu daga cikinsu wadanda lamarin ba zai shafan su ba. Wasu kwazansu ne zai cece su, yayin da wasu kuma za su tsira ne sakamakon tasirinsu a siyasa da dangantakarsu da shugaban kasa.

“Wadanda ake ganin za su sha sun hada da Ministan Babban Birnin Tarayya (FCT), Nyesom Wike; ministan lafiya da walwalar jama’a, Farfesa Ali Pate; ministan sufurin jiragen sama da raya sararin samaniya, Festus Keyamo, ministan harkokin cikin gida, Olubunmi Tunji-Ojo; ministan kudi, Wale Edun; ministan kasafin kudi da tsare-tsaren kasa, Atiku Bagudu da ministan ayyuka, Dabe Umahi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaGwamnatin APCMinistoci
ShareTweetSendShare
Previous Post

MOF: Kasar Sin A Shirye Take Ta Zurfafa Hadin Gwiwa Da Dukkan Bangarorin GDI

Next Post

Yawan Cinikayyar Waje Ta Sin A Fannin Hajoji Da Bayar Da Hidimomi Ya Karu Da Kaso 4% A Agusta

Related

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

6 days ago
Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

2 weeks ago
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Adawa Na Cacakar APC A Yankin Arewa Maso Yamma Bisa Goyon Bayan Tazarcen Tinubu

2 weeks ago
Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027

1 month ago
Tinubu
Tambarin Dimokuradiyya

Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

1 month ago
‘Yan Siyasa Na Gwagwarmaya Ne Kadai Wajen Neman Mukami Ba Wai Don Talakawa Ba — Bafarawa
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Siyasa Na Gwagwarmaya Ne Kadai Wajen Neman Mukami Ba Wai Don Talakawa Ba — Bafarawa

1 month ago
Next Post
Yawan Cinikayyar Waje Ta Sin A Fannin Hajoji Da Bayar Da Hidimomi Ya Karu Da Kaso 4% A Agusta

Yawan Cinikayyar Waje Ta Sin A Fannin Hajoji Da Bayar Da Hidimomi Ya Karu Da Kaso 4% A Agusta

LABARAI MASU NASABA

Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

June 6, 2025
Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

June 5, 2025
Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai

Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai

June 5, 2025
Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

June 5, 2025
Ma’aikatar Harkokin Waje: Kasar Sin Ta Kasance Gwarzuwa Wajen Samar Da Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba

Ma’aikatar Harkokin Waje: Kasar Sin Ta Kasance Gwarzuwa Wajen Samar Da Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba

June 5, 2025
‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 

‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 

June 5, 2025
Lambar “-1.5” Gargadi Ce Da Al’ummar Duniya Ke Yi Ga Azzaluma 

Lambar “-1.5” Gargadi Ce Da Al’ummar Duniya Ke Yi Ga Azzaluma 

June 5, 2025
Sabbin Matakan Amurka Game Da Masu Shiga Kasar Sun Ci Karo Da Ikirarinta Na Mutunta Hakkokin Bil Adama

Sabbin Matakan Amurka Game Da Masu Shiga Kasar Sun Ci Karo Da Ikirarinta Na Mutunta Hakkokin Bil Adama

June 5, 2025
Bukola Saraki Ya Tallafawa Al’ummar Mokwa Da Gudunmawar Kuɗi

Bukola Saraki Ya Tallafawa Al’ummar Mokwa Da Gudunmawar Kuɗi

June 5, 2025
Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona

Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona

June 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.