• English
  • Business News
Saturday, August 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mu Tuna Da Jinin Da Aka Zubar Don Kiyaye Hasken Da Muke Da Shi Yanzu

by CGTN Hausa and Sulaiman
11 hours ago
in Ra'ayi Riga
0
Mu Tuna Da Jinin Da Aka Zubar Don Kiyaye Hasken Da Muke Da Shi Yanzu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wannan hoto ne mai taken “Yaron Kasar Sin”. A ranar 28 ga watan Agustan shekarar 1937, sojojin kasar Japan suka kai harin bom wata tashar jiragen kasa da ke birnin Shanghai, wanda ya halaka fararen hula na kasar Sin da dama. An dai dauki hoton ne bayan harin, inda wani yaron da bai kai shekara daya da haihuwa ba yake kuka a burbushin gini. 

A kwanakin baya, na kalli wani fim mai taken “Dead to Rights”, wanda yanzu haka ke samun matukar farin jini a gidajen sinima na kasar Sin. Fim din ya bayyana duhun da al’ummar Sinawa suka shiga sakamakon wannan yakin da maharan Japan suka tayar, da ma yadda suka tashi tsaye don yakar maharan. A watan Disamban shekarar 1937, sojojin Japan suka mamaye birnin Nanjing na kasar Sin, inda suka shafe tsawon makwanni shida suna yi wa fararen hula sama da dubu 300 na birnin kisan kiyashi. Fim din wanda aka yi amfani da ingantattun shaidun hotuna na ta’asar yakin da Japanawa suka aikata a lokacin kisan kiyashin Nanjing, ya ba da labarin wani rukunin fararen hula na kasar Sin da suka nemi mafaka a wani dakin daukar hoto a birnin Nanjing, a wani yunkuri na neman tsira da rayukansu hajaran-majaran. Sai dai sojojin Japan sun tilasta musu taimaka wa wani mai daukar hoto na sojan Japan wanke hotuna, amma kwatsam suka gano yadda hotunan ke dauke da shaidun munanan ta’asar da sojojin Japan suka tafka a sassan birnin. Bisa kudirinsu na tona asirin abin da ya faru, sai suka boye hotunan tare da jefa rayuwarsu cikin hadari wajen bayyana su ga duniya.

  • Ba Gaskiya Ba Ne Rahoton Da Ke Cewa An Yi Sulhu Da Bello Turji – Guyawa Isa
  • Tsoffin Kansilolin APC Sun Yi Zanga-zangar Nesanta Kansu Da Maganganun Abdullahi Abbas 

A yayin da muke kallon fim din a gidan sinima, masu kallo da yawa sun yi kuka, labarin da fim ya nuna yana da matukar ban tausayi da bata rai, sai dai aihinin abin da ya faru a tarihi har ya fi shi muni.

Fim din ya bakanta ran ‘yan siyasa da masu ziyartar shafukan yanar gizo da dama na kasar Japan, har ma sun musanta tarihinsu na kisan kiyashin, suna zargin cewa, wai “kasar Sin na amfani da fim don yayata ra’ayoyin kin jinin kasar Japan.” Lallai akwai tarin shaidu game da miyagun laifukan da sojojin kasar Japan suka aikata a yakin da suka tayar a kan kasar Sin, amma duk da haka, gwamnatin kasar Japan ba ta taba yarda da laifuffukan da ta aikata ba, kuma masu tsattsauran ra’ayi na kasar sun yi iyakar kokarinsu wajen jirkitawa da boye tarihin kutsen da suka yi wa Sin, don neman gurgunta fahimtar kasashen duniya game da tarihin.

Akwai dimbin fina-finai masu alaka da yakin duniya na biyu, to, amma me ya sa Jamusawa ba su damu da fina-finai irinsu Schindler’s List ba? Sa’an nan me ya sa masu kallon fina-finan ba su ji haushin kasar Jamus ba? Amsa ita ce sabo da gwamnatin kasar Jamus da al’ummar kasar sun yi matukar tuba game da laifukan da kasar ta aikata a lokacin yakin duniya na biyu, tare da neman gafara wurin wadanda suka yi musu laifukan, don haka ma kasa da kasa suka yi musu afuwa. Amma yadda Japan ke kin yarda da laifukanta tare da neman gurbata gaskiyar abubuwan da suka faru, ya kara wa al’ummar kasashen da ta aikata wa laifukan radadin abun da ya faru, kuma hakan ya kasance gargadi ga kasa da kasa.

Labarai Masu Nasaba

Ta Yaya Za a Ba Matasa Damar Raya Kansu?

Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe

A cikin fim din “Dead to Rights”, an ce, “Mu tuna da jinin da aka zubar a yakin, don mu kiyaye hasken da muke da shi yanzu.” Abin haka yake, yau mun waiwayi abubuwan da suka faru a tarihi, ba don neman ci gaba da kiyaya da juna ba, a maimakon hakan, muna son kira ga al’ummomin duniya da su tsaya tsayin daka a kan kiyaye zaman lafiya da magance yaki a tsakaninsu.

Yakin duniya na biyu babbar masifa ce ga dan Adam, kuma irin ra’ayi da ake rike da shi game da tarihin yakin, ya zama wata jarrabawa ga dan Adam. A bana ake cika shekaru 80 da al’ummar Sinawa suka samu nasarar yaki da mahara Japanawa, da ma kasashen duniya suka samu nasarar yaki da ‘yan Fascist, kuma rike ra’ayi madaidaici game da tarihin yakin duniya na biyu a daidai wannan lokaci, yana da ma’ana ta musamman ga kasashen duniya, musamman a yayin da ake fuskantar rikice-rikice da zaman dar dar a duniya.

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ba Gaskiya Ba Ne Rahoton Da Ke Cewa An Yi Sulhu Da Bello Turji – Guyawa Isa

Next Post

UEFA Ta Ci Tarar Lamine Yamal Da Lewandowski Kan Karya Dokar Shan Ƙwayar Ƙara Kuzari

Related

Ta Yaya Za a Ba Matasa Damar Raya Kansu?
Ra'ayi Riga

Ta Yaya Za a Ba Matasa Damar Raya Kansu?

1 day ago
Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe
Ra'ayi Riga

Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe

4 days ago
Amurka: “Afirka Ba Ta Cikin Jerin Fannoni Da Muka Ba Da Fifiko A Kai”
Ra'ayi Riga

Amurka: “Afirka Ba Ta Cikin Jerin Fannoni Da Muka Ba Da Fifiko A Kai”

1 week ago
Mai Cin Moriyar Kai Da Mai Cin Moriyar Juna
Ra'ayi Riga

Mai Cin Moriyar Kai Da Mai Cin Moriyar Juna

1 week ago
Bai Kamata a Rika Kai wa Fararen Hula Hari Ba!
Ra'ayi Riga

Bai Kamata a Rika Kai wa Fararen Hula Hari Ba!

2 weeks ago
Tursasawa Kasashen Afirka Karbar Bakin Haure Daga Amerika Kuskure Ne
Ra'ayi Riga

Tursasawa Kasashen Afirka Karbar Bakin Haure Daga Amerika Kuskure Ne

2 weeks ago
Next Post
UEFA Ta Ci Tarar Lamine Yamal Da Lewandowski Kan Karya Dokar Shan Ƙwayar Ƙara Kuzari

UEFA Ta Ci Tarar Lamine Yamal Da Lewandowski Kan Karya Dokar Shan Ƙwayar Ƙara Kuzari

LABARAI MASU NASABA

Xi Jinping Ya Zanta Da Putin Ta Wayar Tarho

Xi Jinping Ya Zanta Da Putin Ta Wayar Tarho

August 8, 2025
Gwamnatin Tarayya da Ofishin Jakadancin Amurka Sun Haɗa Gwiwa Don Wayar Da Kan ‘Yan Nijeriya Kan Sababbin Ƙa’idojin Samun Biza

Gwamnatin Tarayya da Ofishin Jakadancin Amurka Sun Haɗa Gwiwa Don Wayar Da Kan ‘Yan Nijeriya Kan Sababbin Ƙa’idojin Samun Biza

August 8, 2025
Shin Amurka Ta Manta Da Azabar “Babban Koma-Baya” Tare Da Haraji Mafi Yawa a Lokacin Na Tsawon Kusan Karni?

Shin Amurka Ta Manta Da Azabar “Babban Koma-Baya” Tare Da Haraji Mafi Yawa a Lokacin Na Tsawon Kusan Karni?

August 8, 2025
Nijeriya Ta Horar Da Likitoci 360 Don Magance Mutuwar Mata Masu Juna Biyu

Nijeriya Ta Horar Da Likitoci 360 Don Magance Mutuwar Mata Masu Juna Biyu

August 8, 2025
Sin Ta Mika Sabon Kason Tallafin Abinci Ga Zimbabwe

Sin Ta Mika Sabon Kason Tallafin Abinci Ga Zimbabwe

August 8, 2025
Bashir Ojulari: Me Ya Sa Ake Tsoron Gaskiya Ta Yi Aiki A NNPC? 

Bashir Ojulari: Me Ya Sa Ake Tsoron Gaskiya Ta Yi Aiki A NNPC? 

August 8, 2025
Gwamnatin Kaduna Ta Amince Da Hutun Wata 6 Ga Mata Masu Shayarwa

Gwamnatin Kaduna Ta Amince Da Hutun Wata 6 Ga Mata Masu Shayarwa

August 8, 2025
’Yansanda Sun Kama ’Yan Bindiga 17 Tare Da Kashe 3 A Abuja

An Hallaka Manomi, An Kashe Shanu Da Tumakai A Wani Sabon Rikici A Bogoro

August 8, 2025
An Bude Taron Mutum-Mutumin Inji Na Duniya Na 2025 A Yau Juma’a

An Bude Taron Mutum-Mutumin Inji Na Duniya Na 2025 A Yau Juma’a

August 8, 2025
Bango Ya Kashe Mutum 6, Ya Raunata Wasu A Katsina

Bango Ya Kashe Mutum 6, Ya Raunata Wasu A Katsina

August 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.