ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Muddin Sojojin ECOWAS Suka Sa Mana Karfi, Za Mu Hallaka Bazoum – Jagororin Juyin Mulki

by Khalid Idris Doya
2 years ago
ECOWAS

Jagororin da suka jagoranci kifar da gwamnatin demukuradiyya a Jamhuriyyar Nijar, sun yi barazanar hallaka shugaba Mohammed Bazoum muddin kasashen da ke makwafta da su ko kuma ECOWAS ta afka musu da karfin soja.

LEADERSHIP ta labarto cewa ECOWAS a ranar Alhamis ta umarci dakarunta na ko-ta-kwana da su kimtsa su ja damarar fara yaki domin dawo da mulkin demukuradiyya a jamhuriyyar Nijar.

  • Nijar: Sojoji Sun Kame Manyan ‘Yan Siyasa Da Ministocin Bazoum 
  • ECOWAS Na Duba Yiwuwar Amfani Da Karfin Soja Wajen Mayar Da Bazoum Kujera

Rahoton AP ya labarto cewa wani jami’in sojan kasashen yamma, ya shaida bisa sharadin ba za a bayyana sunansa ba cewa, wakilan dakarun Junta sun tabbatar wa mataimakin sakataren wajen Amurka Victoria Nulanda irin barazanar da shugaba Bayou ke fuskanta a lokacin da ta ziyarci kasar a ciki makon nan.

ADVERTISEMENT

Kazalika, wani jami’in Amurka shi ma ya tabbatar da wannan, yayin da ke magana bisa neman a sakaye sunansa saboda ba shi ne ke da ikon magana da ‘yan jarida ba.

Barazanar daga dukkanin bangarorin ya haifar da zaman dar-dar, sai dai an yi fatan dukkaninsu ba za su kai ga aiwatar da kalaman nasu ba, kamar yadda tsohon jami’in ofishin jakadancin Amurka, Aneliese Bernard ya shaida, wanda shi din masani ne kan harkokin Afrika.

LABARAI MASU NASABA

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

LEADERSHIP ta labarto cewa ECOWAS ta gudanar da wani taro a ranar Alhamis a Abuja dangane da matakinta na gaba da za ta dauka kan halin da ake ciki a Nijar.

Da yake magana bayan kammala ganawar tasu, shugaban hukumar ECOWAS, Omar Alieu Touray, ya ce, sun bi matakan lalama da salama amma hakarsu bata cimma ruwa ba wajen maido da shugaba Bazoum kan mulkinsa, don haka ne suka cimma matsayar umartar sojojinsu na ko-ta-kwana da su shirya damarar yaki.

Ya kuma daura laifin dukkanin wani kunci da takunkumin da aka kakaba wa Nijar ya janyo wa jama’an kasar, ya kuma ce, matsayar da suka cimma zai zama hadin guiwa ne.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani
Manyan Labarai

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi
Manyan Labarai

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

December 20, 2025
HOTUNA: Yadda Tinubu Ya Kai Ziyara Don Ta’aziyyar Sheikh Dahiru Bauchi
Hotuna

HOTUNA: Yadda Tinubu Ya Kai Ziyara Don Ta’aziyyar Sheikh Dahiru Bauchi

December 20, 2025
Next Post
Gudun Ka Da Na Tagayyara Da ‘Ya’yana Ya Sa Na Shiga Kasuwanci –Zainab Adam

Gudun Ka Da Na Tagayyara Da ‘Ya’yana Ya Sa Na Shiga Kasuwanci –Zainab Adam

LABARAI MASU NASABA

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025
Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

December 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

December 21, 2025
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

December 20, 2025
Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

December 20, 2025
Matasa Miliyan 80 Ne Ba Su Da Aikin Yi A Nijeriya

Matasa Miliyan 80 Ne Ba Su Da Aikin Yi A Nijeriya

December 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.