ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 18, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijar: Sojoji Sun Kame Manyan ‘Yan Siyasa Da Ministocin Bazoum 

by Sadiq
3 years ago
Nijar

Rahotannin da ke fitowa daga Jamhuriyar Nijar na nuni da cewa gwamnatin mulkin soja a kasar ta fara kame jami’an gwamnati da suka hada da ministan ma’adinai na jam’iyya mai mulki, da kuma ministan mai Mahamane Mahamadou, wanda kuma dan tsohon shugaban kasar, Issoufou Mahamadou ne.

Ministoci akalla hudu ne da suka hada da tsohon minista da kuma shugaban jam’iyyar hambararren shugaban kasar Mohamed Bazoum ne, aka kama a hannun gwamnatin soja da ta kwace mulki a ranar 26 ga watan Yuli, in ji jam’iyyar a ranar Litinin.

  • Ba Abin Da Zai Hana Mu Shiga Zanga-Zanga —NLC
  • A Guji Tarzoma Yayin Zanga-zanga, IGP Ya Gargadi NLC Da TUC

“Bayan an tsare shugaban kasar a makon da ya gabata, sojojin sun sake tsare wasu,” in ji jam’iyyar Democratic Democratic Party (PNDS) a cikin wata sanarwa.

ADVERTISEMENT

“A safiyar ranar Litinin, an kama ministan mai, Mahamane Sani Mahamadou, dan tsohon shugaban kasa Mahamadou Issoufou da kuma ministan ma’adinai Ousseini Hadizatou,” in ji sanarwar.

An kuma kama shugaban kwamitin zartarwa na PNDS na kasa, Fourmakoye Gado, in ji shi.

LABARAI MASU NASABA

Sabon Tsarin Tikitin Abinci Na Nusuk Zai Iya Ƙara Kuɗin Bizar Umrah

Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi

A baya dai gwamnatin mulkin sojan kasar ta kama ministan harkokin cikin gida Hama Amadou Souley da ministan sufuri Oumarou Malam Alma da kuma Kalla Moutari dan majalisa kuma tsohon ministan tsaro, in ji jam’iyyar.

Jam’iyyar ta yi kira da a sake su cikin gaggawa, tana mai cewa Nijar na cikin tsaka mai wuya.

Wata majiya da ke kusa da fadar shugaban kasar ta ce an kuma kama ministan koyar da sana’o’i, Kassoum Moctar.

Kamen ya zo daidai da wata sanarwa da gwamnatin mulkin sojan kasar ta bayar na bukatar “dukkan tsofaffin ministoci da shugabannin hukumomi da su mika motocin ofishinsu.

A ranar Larabar da ta gabata ne wasu jami’an tsaron fadar shugaban kasar suka hambarar da gwamnatin shugaba Bazoum, wanda shugabansu Abdourahamane Tiani, ya ayyana kansa a matsayin sabon shugaban kasar.

Sai dai ECOWAS da Majalisar Dinkin Duniya sun yi Allah-wadai da juyin mulki da sojojin suka yi.

Inda suka ba su wa’adin mako guda don dawo da mulki ga shugaba Bazoum.

MASU ALAKA

Sabon Tsarin Tikitin Abinci Na Nusuk Zai Iya Ƙara Kuɗin Bizar Umrah
Manyan Labarai

Sabon Tsarin Tikitin Abinci Na Nusuk Zai Iya Ƙara Kuɗin Bizar Umrah

July 18, 2026
Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi
Manyan Labarai

Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi

July 17, 2026
Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe
Manyan Labarai

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

July 17, 2026
Next Post
Barcelona Ta Doke AC Milan A Wasan Sada Zumunta

Barcelona Ta Doke AC Milan A Wasan Sada Zumunta

LABARAI MASU NASABA

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota

July 18, 2026
An Kama Matashi A Kano Kan Zargin Kashe Abokinsa

‘Yansanda Sun Kama Mutum Biyu Kan Zargin Damfarar Wayar Salula A Jihar Adamawa

July 18, 2026
Sabon Tsarin Tikitin Abinci Na Nusuk Zai Iya Ƙara Kuɗin Bizar Umrah

Sabon Tsarin Tikitin Abinci Na Nusuk Zai Iya Ƙara Kuɗin Bizar Umrah

July 18, 2026
Tasirin Da VAR Ta Yi A Gasar Kofin Duniya

Tasirin Da VAR Ta Yi A Gasar Kofin Duniya

July 18, 2026
Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

July 18, 2026
Sin Za Ta Inganta Kaddamar Da Aikin Kungiyar Hadin Gwiwar AI Ta Duniya Da Wuri

Sin Za Ta Inganta Kaddamar Da Aikin Kungiyar Hadin Gwiwar AI Ta Duniya Da Wuri

July 17, 2026
Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya

Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya

July 17, 2026
Sin Ta Yaba Da Matakin Amurka Na Kin Tsawaita Dokar Ta-Baci Dangane Da HK

Sin Ta Yaba Da Matakin Amurka Na Kin Tsawaita Dokar Ta-Baci Dangane Da HK

July 17, 2026
Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura

Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura

July 17, 2026
Xi Ya Gana Da Babban Sakataren MDD Da Firaministocin Thailand Da CambodiaA

Xi Ya Gana Da Babban Sakataren MDD Da Firaministocin Thailand Da CambodiaA

July 17, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.