ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijar: Sojoji Sun Kame Manyan ‘Yan Siyasa Da Ministocin Bazoum 

by Sadiq
3 years ago
Nijar

Rahotannin da ke fitowa daga Jamhuriyar Nijar na nuni da cewa gwamnatin mulkin soja a kasar ta fara kame jami’an gwamnati da suka hada da ministan ma’adinai na jam’iyya mai mulki, da kuma ministan mai Mahamane Mahamadou, wanda kuma dan tsohon shugaban kasar, Issoufou Mahamadou ne.

Ministoci akalla hudu ne da suka hada da tsohon minista da kuma shugaban jam’iyyar hambararren shugaban kasar Mohamed Bazoum ne, aka kama a hannun gwamnatin soja da ta kwace mulki a ranar 26 ga watan Yuli, in ji jam’iyyar a ranar Litinin.

  • Ba Abin Da Zai Hana Mu Shiga Zanga-Zanga —NLC
  • A Guji Tarzoma Yayin Zanga-zanga, IGP Ya Gargadi NLC Da TUC

“Bayan an tsare shugaban kasar a makon da ya gabata, sojojin sun sake tsare wasu,” in ji jam’iyyar Democratic Democratic Party (PNDS) a cikin wata sanarwa.

ADVERTISEMENT

“A safiyar ranar Litinin, an kama ministan mai, Mahamane Sani Mahamadou, dan tsohon shugaban kasa Mahamadou Issoufou da kuma ministan ma’adinai Ousseini Hadizatou,” in ji sanarwar.

An kuma kama shugaban kwamitin zartarwa na PNDS na kasa, Fourmakoye Gado, in ji shi.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

A baya dai gwamnatin mulkin sojan kasar ta kama ministan harkokin cikin gida Hama Amadou Souley da ministan sufuri Oumarou Malam Alma da kuma Kalla Moutari dan majalisa kuma tsohon ministan tsaro, in ji jam’iyyar.

Jam’iyyar ta yi kira da a sake su cikin gaggawa, tana mai cewa Nijar na cikin tsaka mai wuya.

Wata majiya da ke kusa da fadar shugaban kasar ta ce an kuma kama ministan koyar da sana’o’i, Kassoum Moctar.

Kamen ya zo daidai da wata sanarwa da gwamnatin mulkin sojan kasar ta bayar na bukatar “dukkan tsofaffin ministoci da shugabannin hukumomi da su mika motocin ofishinsu.

A ranar Larabar da ta gabata ne wasu jami’an tsaron fadar shugaban kasar suka hambarar da gwamnatin shugaba Bazoum, wanda shugabansu Abdourahamane Tiani, ya ayyana kansa a matsayin sabon shugaban kasar.

Sai dai ECOWAS da Majalisar Dinkin Duniya sun yi Allah-wadai da juyin mulki da sojojin suka yi.

Inda suka ba su wa’adin mako guda don dawo da mulki ga shugaba Bazoum.

MASU ALAKA

Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Next Post
Barcelona Ta Doke AC Milan A Wasan Sada Zumunta

Barcelona Ta Doke AC Milan A Wasan Sada Zumunta

LABARAI MASU NASABA

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.