ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Muddin Sojojin ECOWAS Suka Sa Mana Karfi, Za Mu Hallaka Bazoum – Jagororin Juyin Mulki

by Khalid Idris Doya
3 years ago
ECOWAS

Jagororin da suka jagoranci kifar da gwamnatin demukuradiyya a Jamhuriyyar Nijar, sun yi barazanar hallaka shugaba Mohammed Bazoum muddin kasashen da ke makwafta da su ko kuma ECOWAS ta afka musu da karfin soja.

LEADERSHIP ta labarto cewa ECOWAS a ranar Alhamis ta umarci dakarunta na ko-ta-kwana da su kimtsa su ja damarar fara yaki domin dawo da mulkin demukuradiyya a jamhuriyyar Nijar.

  • Nijar: Sojoji Sun Kame Manyan ‘Yan Siyasa Da Ministocin Bazoum 
  • ECOWAS Na Duba Yiwuwar Amfani Da Karfin Soja Wajen Mayar Da Bazoum Kujera

Rahoton AP ya labarto cewa wani jami’in sojan kasashen yamma, ya shaida bisa sharadin ba za a bayyana sunansa ba cewa, wakilan dakarun Junta sun tabbatar wa mataimakin sakataren wajen Amurka Victoria Nulanda irin barazanar da shugaba Bayou ke fuskanta a lokacin da ta ziyarci kasar a ciki makon nan.

ADVERTISEMENT

Kazalika, wani jami’in Amurka shi ma ya tabbatar da wannan, yayin da ke magana bisa neman a sakaye sunansa saboda ba shi ne ke da ikon magana da ‘yan jarida ba.

Barazanar daga dukkanin bangarorin ya haifar da zaman dar-dar, sai dai an yi fatan dukkaninsu ba za su kai ga aiwatar da kalaman nasu ba, kamar yadda tsohon jami’in ofishin jakadancin Amurka, Aneliese Bernard ya shaida, wanda shi din masani ne kan harkokin Afrika.

LABARAI MASU NASABA

Obasanjo Da Atiku Sun Sake Musayar Zafafan Kalaman Zargin Juna

Sana’ar Kilishi:Yadda Ta Bunkasa Daga Jihar Katsina Zuwa Wasu Sassan Nijeriya

LEADERSHIP ta labarto cewa ECOWAS ta gudanar da wani taro a ranar Alhamis a Abuja dangane da matakinta na gaba da za ta dauka kan halin da ake ciki a Nijar.

Da yake magana bayan kammala ganawar tasu, shugaban hukumar ECOWAS, Omar Alieu Touray, ya ce, sun bi matakan lalama da salama amma hakarsu bata cimma ruwa ba wajen maido da shugaba Bazoum kan mulkinsa, don haka ne suka cimma matsayar umartar sojojinsu na ko-ta-kwana da su shirya damarar yaki.

Ya kuma daura laifin dukkanin wani kunci da takunkumin da aka kakaba wa Nijar ya janyo wa jama’an kasar, ya kuma ce, matsayar da suka cimma zai zama hadin guiwa ne.

ECOWAS
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ‘Yansanda Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Harbe Mai Unguwa Har Lahira A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ba Mu Sayar Wa Dangote Da Reshen Jami’ar SAZU Na Yuli Ba-Gwamnatin Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

MASU ALAKA

ECOWAS
Manyan Labarai

Obasanjo Da Atiku Sun Sake Musayar Zafafan Kalaman Zargin Juna

July 25, 2026
Sana’ar Kilishi:Yadda Ta Bunkasa Daga Jihar Katsina Zuwa Wasu Sassan Nijeriya
Manyan Labarai

Sana’ar Kilishi:Yadda Ta Bunkasa Daga Jihar Katsina Zuwa Wasu Sassan Nijeriya

July 24, 2026
Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare
Manyan Labarai

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

July 24, 2026
Next Post
Gudun Ka Da Na Tagayyara Da ‘Ya’yana Ya Sa Na Shiga Kasuwanci –Zainab Adam

Gudun Ka Da Na Tagayyara Da ‘Ya’yana Ya Sa Na Shiga Kasuwanci –Zainab Adam

LABARAI MASU NASABA

ECOWAS

Obasanjo Da Atiku Sun Sake Musayar Zafafan Kalaman Zargin Juna

July 25, 2026
Manufofin Tattalin Arzikin Gwamnatin Tinubu Sun Lalata Rayukan Al’ummar Nijeriya —ADC

Manufofin Tattalin Arzikin Gwamnatin Tinubu Sun Lalata Rayukan Al’ummar Nijeriya —ADC

July 25, 2026
An Karrama Masana Ilimin Lissafi Na Kasar Sin Da Lambobin Yabo Na Fields Medal

An Karrama Masana Ilimin Lissafi Na Kasar Sin Da Lambobin Yabo Na Fields Medal

July 24, 2026
Ta Da Zaune Tsaye Da Philippines Ta Yi A Teku Ba Zai Lalata Dangantakar Hadin Gwiwar Sin Da ASEAN Ba

Ta Da Zaune Tsaye Da Philippines Ta Yi A Teku Ba Zai Lalata Dangantakar Hadin Gwiwar Sin Da ASEAN Ba

July 24, 2026
Jadawalin INEC:Kotun Daukaka Kara Ta Kassara Fatan Jam’iyyu Da ‘Yan Siyasa

Jadawalin INEC:Kotun Daukaka Kara Ta Kassara Fatan Jam’iyyu Da ‘Yan Siyasa

July 24, 2026
An Zartas Da Sanarwar Chengdu A Taron Ministocin Kungiyar APEC Kan Harkar Raya Fasahohin Dijital Da AI

An Zartas Da Sanarwar Chengdu A Taron Ministocin Kungiyar APEC Kan Harkar Raya Fasahohin Dijital Da AI

July 24, 2026
NNPP Za Ta Kwace Mulki A Jihar Imo – Kwankwaso

Jam’iyyar NDC Ta Shirya Tsaf Domin Kafa Gwamnati A 2027 —Kwankwaso

July 24, 2026
Sin Ta Kara Kamfanoni 14 Na Tarayyar Turai Cikin Jerin Wadanda Aka Hana Fitar Masu Da Kaya

Sin Ta Kara Kamfanoni 14 Na Tarayyar Turai Cikin Jerin Wadanda Aka Hana Fitar Masu Da Kaya

July 24, 2026
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa

Kyamar Baki: Shettima Ya Ja Kunnen Gwamnatin Afirka Ta Kudu

July 24, 2026
Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya

Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya

July 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.